Skip to content

Chapter 8

Chapter 8

Dan Mace Book One Complete Hausa Novel 1,295 words 0 views Progress saved
Download Book

yi masa izgili ta hanyar tsallake shagunan unguwa zuwa gurinsa,to idan sun zo d'in ma dai mai makon su jira ya basu,su da kansu suke d'auka suna masa wasa da kayan sana'a,idan yayi magana suci gaba da dariya suna tsokanarsa da fad'in maganganu marasa dad'i,abun ya fara damunsa a rai ya fara tunanin daina sana'ar tunda ita take kawo masa wulak'anci,sai kuma yayi tunanin shin idan ya bari d'in gurin waye zai dunga samun kud'in b'atarwa da biyawa kansa k'ananun buk'atu na yau da kullum.?? Wannan tunani yayi masa jagoranci wajen yin watsi da al'amuran mutane yaci gaba da bin shawarar zuciyarsa,and ya d'ora daga inda ya tsaya,,a lokaci guda yana sana'arsa kuma yana ci gaba da karatunsa,kullum cikin ranakun markaranta da safe zaije makaranta,da yamma kuma zai zauna gurin sana'ar sa,duk da tun farkon fara wannan d'abi'a tasa mahaifansa sunyi iya yinsu akan ya bari tunda komai na rayuwa akwai a gida amma sai yace shifa sam su kyale shi yayi,to ganin ba dainawar zai yi ba yasa suma kansu suka hak'ura suka zuba masa idanu tare da binsa da fatan alkhairi,,,bayan wani lokaci da fara sana'ar tasa Allah ya sake bud'a masa,lokacin da Alhaji zakar ya fahimci da gaske yake son yin sana'ar ya bud'e masa shop a nan jikin gidan,raba d'aya nasara ta kwankwaso masa k'ofa daga zube kaya saman tabarma ya koma babban container,yayi farin ciki sosai lokacin da yayi gamo da canjin da ya samu daga ubangiji,,akan haka rayuwarsa ta fara kullum cikin samun bud'i daga ubangiji akan harkar kasuwancin sa." Dan kallon Nuraz Annie tayi da yake ta kallonta tace "wannan duka ina tsakuro maka labarin abunda ya riga ya faru ne a tak'aice,kafin mu gangara kan asalin alak'ar data had'a mahaifanka. " A hankali gyad'a mata kai alamun ya gane,Annie taci gaba "Asalin alak'ar mu da juna,,,mun kasance tsakaninmu da mahaifinka neighbours ne mu kamar yadda na fad'a tun farko,mun taso cikin unguwa d'aya a cikin line guda,gidajen mu basu da wani nisa tsakani,hasalima sun kasance suna kallon juna,but mun samu bambancin tsagi,ina nufin mu muna wannan gefen suma gidan su mahaifinka suna d'ayan hannun,kasancewar mu a haka na tsayin shekaru yasa babu yadda za'ayi ace bamu san juna ba,duk wanda yake cikin line mu ko da jiya ya zo mun san juna mu da shi,mun kasance mu da kowane gida kamar y'an uwan juna. Gidan mu a gaba d'aya line ya kasance shi ne gidana farko da yafi kowanne tara mutane,bisa wannan dalilin yasa a kullum ba'a rabo da yin fad'a da y'an gidanmu,saboda yawanmu da jaye²n fad'a irin namu yasa muka yi fice a unguwar,dalili yawanmu kuwa shi ne babanmu yayi aure²,wannan yasa adadin y'ay'ansa muka kai ashirin maza da mata,to kuma dai da yake ba'a samu macen data zauna ba a cikin matan daya aura sai mahaifiyarmu,wacce ta zauna tare da shi tsayin lokacin har Allah ya karb'i rayuwar ta tana gidan,bayan mutuwarta sai wata bazawara daya sake aura,idan aka cire wad'annan matan biyu a tarihin gidan mu da aure²n babanmu sune kad'ai matan da suka zauna sama da shekara guda,duk wacce ta zo bata wuce haka,,sannan a yadda muke rayuwa gidan mu ya kasance yana da matsaloli,amma abu na farko daya nakasa gidanmu shi ne rashin had'in kai sai rashin wadataccen muhalli,wannan sune suka bawa gidan tallafin da kullum a kowace safiya yake kamar gidan haya,da zaran gari ya waye za'a fara hayaniya da fad'ace-fad'ace wannan ya tsokani wancan,kullum haka ake yini abu guda,idan har kaji baki ya huta tofa sai dai idan dare ne ya zagayo kowa ya kwanta hak'ark'arinsa,a nan d'inma gurin kwanciyar bawai ina nufin za'a yi shi lafiya bane,dole sai an yada hali kafin baccin,wani lokaci idan ta d'auro cikin baccin ma sai an daki juna,,rayuwar gidanmu ta kasance rayuwa ce ake yinta kowa yana ganin hanjin kowa,zaman lafiya yayi mana k'aranci,kowa tak'amarsa shi kad'ai Babarsa ta haifa,kasancewar duk matan da suka shigo daga haihuwa d'aya ne zaman yake k'in dad'i wata ma bata haihuwar sai kaga an tafi,tafiyar da babu biko bare kome,,kowa shi kad'ai ne bashi da d'an uwa duka a cikin gidan,idan aka cire mu ni da mahaifiyarka da muka kasance ciki d'aya kuma baba d'aya,komai namu mun kasance tare muke yinsa tun tasowar mu duk da tsakani na da ita akwai nisan shekaru biyar (5),bata tab'a raina ni ba,tana bani girma na a matsayin yayarta,yadda ta d'auke ni take girmama ni a matsayina na y'ar uwarta da muka fito ciki d'aya,yana b'atawa sauran y'an uwanmu rai,a ganinsu ta yaya zamu kasance masu had'in kai al'halin duka gidan kawuna suna a rarrabe.? And duk wanda zai neme mu da fad'a bama kulawa daga ni har Hauwa,wannan hali ne wanda mahaifiyarmu ta d'ora mu akai,duk abunda zasu ce idan zasu kwana suna magana bama tanka musu,,kafin Allah ya yiwa mahaifiyarmu rasuwa tayi iya kokarin da zata iya na ganin ta had'a kawunanmu gaba d'aya,ganin lamarin ya gagareta ta hak'ura ta zubawa sarautar Allah ido,Innar mu mace ce mai hak'uri da kauda kai,ta rasu lokacin Hauwa tana da shekaru uku a duniya,,to da yake a gidanmu bamu samu wadataccen muhalli ba,kasancewar duka d'akuna guda hud'u ne,babanmu d'akinsa daban,matar babanmu ma haka,sai ya zama mu mata gaba d'aya muna d'aki guda,sauran d'akin kuma na y'an uwanmu ne maza,,a duka tashinmu halin babanmu guda biyu yake burgeni kuma nake matuk'ar so,duk da nasan da yawa mutane sukan yi mamaki da wannan halin nasa,amma agare mu ba abun mamaki bane,duk da kasancewar muna da yawa a gidanmu hakan ko kad'an baisa ya gagara ciyar damu ba,a kullum rana yadda ake d'ora tukunya a sauke sau uku a ko wane gida da suke jin suna da rufin asiri,muma haka nan ake yinsa a gidanmu,safe,rana da dare duk lokacin da mutum ya b'ukaci abinci zai same shi,,amma batun girmamawa ga juna ko soyayya irin ta y'an uwantaka wannan ne babu shi,haka ko a b'angaren karatu ma dai² gwargwado baba yana iyakar k'ok'arin sa wajen ganin mun wadata da ilimi,sai dai mu d'in a wannan fannin ba kowa ne hankalinsa ke kan karatun ba,duk wanda aka ce yau mahaifiyarsa bata cikin gidan mahaifinsa dole ne rayuwarsa ta samu nakasa dole ne kuma kaga bambanci da ratuwar wanda yake tare da tasa mahaifiyar,mahaifiya ita ce tushen tarbiyya ga ko wane d'a,shin mu da bamu da iyaye wane ne zai ce muyi ko mu bari.? Duk wacce baba zai auro wani lokaci sharrin yau da gobe ke sawa ya rabu da ita,dan har ga Allah babanmu mutum ne da yake da saurin yarda da magana,sannan duk duniya idan har kana son ganin b'acin ransa ka tab'a masa y'ay'a,a wannan lokacin na tabbatar duk yadda kuke da shi lallai za kuyi hannun riga,,ganin abunda muke so shi muke yi yasa itama matar gidan da aka auro take zaune da mu bata tab'a hana mu,idan ana hayaniya bata tab'a cewa mu bari,hasalima sai dai ta kad'e zaninta tayi wucewarta d'aki ta barmu nan,idan muna iyawa mu kashe juna ko mu hak'ura wannan duka ruwanmu ne,wad'annan dalilan yasa gaba d'aya kowa abunda ransa ya so yake yi,makaranta zuwanta sai wanda yaga dama ko yasa kansa,duk safiya baba zai sa mu shirya mu fita saboda yana ganin hakan shine babban gatan da zai mana a rayuwa,zuwa

Table of Contents

Chapters

180 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180