Chapter 29
Chapter 29
gwammace zuwan da ace ciwo ya yi ajalinta ita kad'ai a gurin da babu wani cikin ahalinta,cikin y'an watannin ta yi wani irin ramewa ta yi duhu kamar ba ita ba,duk wanda ya santa idan ya ganta a wannan tak'aitaccen lokacin na tabbata zai yi wahala lokaci d'aya yayi saurin ganeta,ta kamo hanyar K'ofar Na'isa a karo na biyu cike da fargaba,but data tashi zuwa wannan lokacin sai bata yi k'ok'arin shiga gida ba ko nema na,ta sake aiko min wasik'a,ina zaune cikin d'aki jigum sak'on ta ya riske ni,na karanta naga fiye da rabin maganarta akan na nema mata yafiya ne a gurin Baba,sai sauran mutanen da nasan wani mu'amala ya tab'a had'a su,ina kuka ina karamtawa har na zo inda take barmin wasiyya tana sanar min ta jima ba ta da lafiya na taimaketa na nema mata alfarma gurin Baba na zo na ganta ko da sau d'aya ne kafin ta Allah ta kasance mata,a wannan wasik'ar nayi gamo da tsananin tashin hankalin da ya wuce tunani na _"Kiyi hak'uri y'ar uwata.! Babu yadda zanyi,ya zame min wajibi na sanar miki,duk da na san kema ba laifinki bane da kika kasa zuwa inda muke,,a halin da nake ciki,bayan dawiwa ta ciwo ya ci k'arfina,ina jin kamar ba zan rayu ba,idan haka ya kasance ina rok'on za ki nema min alfarma a gurin Baba,idan ya barki ko da a shek'ara sau d'aya ne zan yi alfahari da hakan,kema ina fatan za ki je ki duba min yarona,ban san yadda rayuwa ta zata kasance ba,shi yasa na yanke shawaran sanar da ke tun yanzun,zan kai Nuraz orphanage,idan kin samu dama dan Allah Yaya ina rok'on ki kije ki ganshi,na san Yarona ba zai yi maraici ba idan kina raye,na san yana da wata mahaifiyar kamar ki kuma za ki kula da shi fiye da yadda zanyi masa,ni dai tawa ta zo k'arshe sai dai ina yi mana fatan mu kasance tare har a aljannah,idan na yi miki wani laifi ina neman afuwar tun daga yarinta har zuwa girma na,ki yafe min y'ar uwata... Allah ya k'addara saduwarmu.. BISSALAAM.!"_ Daga k'anwar ki mai k'aunar k'i har abada *HAUWA BABA MUHAMMAD...* Tsananin firgici da tsoro na shiga lokacin dana gama karanta sak'on ta,ba tare da na jira neman izinin fita a gurin Baba ba na fito daga gida kamar zararriya nabi hanya ko zan ganta,ina tafiya ina tambayar mutanen unguwa ko sun ganta.!? Sai ace min yanzun babu jimawa ta wuce,da sauri nake wucewa na bar wajen na yi gaba,ina tafe ina sake tambaya,amma abun takaici har na fito titi na gama dubawa ko mai kama da ita ban samu ba,na koma gida cikin firgici na tarar Baba ya dawo,ina kuka na sake zuwa gurinsa da wasik'a ko zai tausaya min ya bari naje,still Baba ya sawa idanunsa toka kamar waccan ranar,ya nuna min sam baya ko son yin maganar,dana takura akan ya barni naje yace idan na sake na fita bada izinin sa ba Allah ya isa bai yafe min ba. Tsoro da tashin hankali suka sake shigata,rashin sanin matsayin Allah ya isa da Baba yayi min,da tsoron halin da y'ar uwata take ciki suka sa na kasa ko magana,ina ji ina gani ga address d'in inda take amma zuwa na dubata ya gagare ni,ban san mene ne zai faru ba idan na fita ba da izininsa Bana ba,sannan mene ne makomata idan na sab'awa umarninsa,,sati guda da zuwanta kullum da ciwon kai nake yini saboda damuwa ga yawan mafarkai da nake yi marasa dad'i,zuciyata kullum cikin yi min khud'ubar naje na duba ku take,na daure na ci gaba da zama ina jiran tsammani,,a cikin satin wani abu daya faru ya sake sawa jiki na yayi sanyi,ko wane lokaci na kwanta bacci da rana ko dare mafarkin Hauwa nake yi,a ko wane lokaci da zan ganta tana kuka tana sake rok'ona kada na manta da kai na kula mata da kai,,kwana biyu tsakani na sake yin mafarki da Innarmu,tun bayan rasuwarta da nayi ta mafarkai da ita,na jima sosai ban sake ganinta ba,ranar na kwanta bacci kenan tazo min cikin wani irin fuska mai ban tsoro,ina murna na nufi inda take zaune da niyyar na rik'e ta sai na ga ta yi tafiyarta,na dunga binta ina rok'on ta tsaya amma bata sake waiwayowa ba,sai dana gaji na fad'i a k'asa,ina kuka ina kiranta da rok'on ta tsaya,sannan naga ta juyo tana kallona tana kuka,hankali na a tashe nace "Inna mene ne ya saki kuka.??" Bud'ar bakinta tace "Ban san haka za kuyi min ba Maryam.. Ke da mahaifinki kun tozarta ni,kun wulakanta ni.. Laifin me nayi muku haka.!?" Nace "Inna laifin me muka yi miki ne.!? Ban gane abunda kike magana ba.!" Ta share hawaye tace "Saboda kunga bana raye kuka wulakanta min y'ata.! Me yasa sai da kuka bari na tafi sannan za ku wofantar da ita.!?" Ina kuka ina bawa Inna hak'uri,bata saurare ni ba ta juya ta ci gaba da tafiya tana cewa "Idan har baki nemi inda y'ar uwarki take kin zauna tare da ita ba,kada ki sake kira na mahaifiyarki,ni ba mahaifiyarki bace,a kullum ina jin bak'in ciki na haifi y'a irin ki.." Nace "Inna ki yi hak'uri dan Allah,nima fa duka ba laifi na bane,ki yarda dani,babanmu ya hana ni zuwa na dubasu." Ta juyo ta kalle ni tana goge hawaye tace "Shi kenan,tunda kin yarda ya raba muku zumunci ki zauna tare da mahaifinki,in sha Allah ubangijin daya hallice mu ba zai tab'a barin Hauwa'u tayi maraici ba.. Daga yau ba zaki sake gani na ba,ki je ki zauna da mahaifinki.." Tana gama fad'ar haka ta juya da sauri,ina kuka ina kiranta amma bata sake waiwayowa ba,jan jiki naci gaba da yi ina son bin hanyar da ta bi,saboda lokacin dana fad'i na ji ciwo sosai a k'afata,na kasa tashi na bita ina nan kwance ina kuka da kiranta har ta b'acewa ganina,cikin k'araji na kwalla kiran Inna,,a firgice na tashi ina dube²,na bud'e ido naga y'an uwanmu mata zagaye da ni sai kallona suke yi suna jiran su ji abunda ya faru na ke zabgaga ihu a farkon dare,na daure na juya ban yiwa kowa magana ba duk tarin tambayoyin da suke min,da suka ga ba ni da niyyar amsa musu kowacce ta juya ta kwanta,,a wannan daren ni dai ban samu damar komawa bacci ba har gari ya waye. Misalin k'arfe 10am lokacin babanmu ya fita na shirya cikin damuwa,ba tare da sanin kowa ba na d'auki takardata na fita daga gida,na samu mai napep na fad'a masa inda zai kaini,yace na shiga ya san gurin,na shiga muka d'auki hanya,mintuna kusan talatin suka d'auke mu saboda baya wani sauri sosai muka k'araso,ya tsaya a dai² block d'in dana fad'a masa,ina ta tunanin halin da zan tarar da ita yace min "Hajiya mun k'araso." Na kalli gurin da muke nace "Ka tabbata nan ne kuwa.!?" Yace "Hajiya ai number za ki duba,ke kika fad'a min fa,ga gidan nan ki sake dubawa mana" Na kalli house number sosai na duba ta jikin takarda,na ga iri d'aya ce babu bambanci,na sake kallon tsarin gidan na tabbatar nan ne inda ta rubuta,na sauka na biya mai napep kud'insa sannan na juya na kalli gidan,zuciyata har lokacin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180