Chapter 11
Chapter 11
"Toh! Alhaji Allah yasa muji alkhairi" Alhaji zakar ya kalleshi da murmushi shima a fuskar sa yace "In sha Allah ma alkhairi ce." Gyara zama Baba yayi yace "Toh Alhaji ina saurarenka,wace irin magana ce wannan d'in.?" Sai da Alhaji zakar yayi ajiyar zuciya ya san tabbas maganar da zai yiwa Baba,idan har bai masa kyakykyawar fahimta ba zasu iya samun sab'ani,haka kuma idan yayi shiru yaci gaba da zuba ido yasan lallai rayuwar marainiyar zata sake shiga wani halin,to amma da yake yayi nufin aikin alkhairi ne har zuciyarsa shi yasa sai ya daure yace "Dama Malam baba magana ce nazo da ita nake son mu tattauna,Allah yasa zaka fahimce ni,dan ba akan komai nazo muyi magana da kai ba sai akan gidanka." Baba yana kallonsa yace "Akan gida na..?" Alhaji yace "K'warai kuwa,akan gidanka." Baba yana binsa da wani irin kallon mamaki da rashin yarda ya sake daurewa yace "Toh ina jinka.." Alhaji zakar yana kallon Baba ya fara zayyana masa duk abubuwan dake faruwa a gidansa,da mugun mamakin yadda akayi ya sani Baba yake ta kallonsa,har ya gama magana Baba bai ce masa komai ba,Alhaji zakar yayi shiru yana ta kallon baba yaji ko zai yi magana amma yaji shiru,dole tasa shi tambayar baba "Malam Baba baka ce komai ba..?" Baba dai yana kallonsa har lokacin da kyar ya bud'e baki cikin kaushin kalami yace "toh Alhaji me zance.?? Tunda Allah yasa munafukai sun fara sawa gidana ido,har sun fara yawo suna yamad'id'i da ni a gari,da tona asirin gidana.. Zance ya lalace tunda har al'amarin gida na ya shiga gari.." "A'a Malam Baba kada kace haka,wannan magana sam baka fahimci yadda take ba,,ni dai ka sanni kuma kasan ba mai shiga harkokin da ba'a sani bane,amma tunda kaga na tsayar da kai nayi maka magana kasan ba zai wuce na hango maka damuwa bane a cikin gidanka na sanar da kai. Toh amma tunda har Allah yasa magana ta batai maka ba,Allah ya huci zuciyarka kuma ya baka hak'uri idan har na b'ata maka rai.." Ajiyar zuciya Baba yayi yace "ai Alhaji wannan batun tunda kazo da shi na san bazai wuce tsaigumi aka kai maka ba,kuma kaima ga shi ka tabbatar min,amma tunda haka abun yake,kafin a fara zagina akan maganar yarinyar nan,dole ne tunda yake nine mahaifinta na zartar da hukuncina akanta ta yadda babu wanda zai sake zuwa min da magana makamanciyar wannan,,zan aurar da ita kowa sai ya huta,da ta d'auko min maganar da zata fi k'arfi na gara na zartar da hukuncin da zan kashe bakin mutane.." Alhaji yana kallon Baba da mamaki yace "Malam Baba aure kace.?" Baba yace "Haka nace",cikin muryar rarrashi Alhaji zakar yace "kada kayi haka malam Baba,yarinyar nan duka nawa take da zaka ce zaka aurar da ita.? Ko a k'auye yanzun tuni an waye an daina irin wannan auren,bare mu da muke cikin birni,,ya kamata kayi tunani dai kafin ka zartar da hukuncin da zai iya kaika ga yin dana sani a gaba." "Alhaji ina ganin wannan hukuncin shi ne dai²,tunda har Allah yasa ka fad'i sak'on da ya kawo ka,kana iya tafiya na gode.." Alhaji yaci gaba da kallon Baba da mamaki "Amma malam Baba ban tab'a tsammanin haka daga gareka ba,wannan al'amari idan har ka tsaya ka nazarce shi da kyau,na tabbata zaka gane gaskiyar da nake son ka fahimta." "Alhaji maganar fahimta ya k'are,tunda har ka fad'i sak'on daya kawo ka,yanzun naka ido ne,,abunda nake fad'a maka a yanzun shi ne batun auren Hauwa na gama yanke hukunci,in sha Allah cikin satin nan zan d'aura mata aure,da ma hak'k'i na ne na aurar da ita ga wanda yayi min,yadda nayi niyya haka zanyi aure babu fashi.." Cikin takaici Alhaji zakar yaci gaba da kallon Baba but bai sake ce masa komai ba ya mik'e da niyyar barin gurin tunda al'amarin yafi k'arfinsa,ya yiwa Baba sallama yana niyyar shiga gida,Baba dake zaune har lokacin yana kallonsa cikin d'aga murya kamar wanda aka bawa umarnin yin magana yace "Yawwa Alhaji ina da wata y'ar maganar nima." Waiwayowa Alhaji zakar yayi yana kallon Baba duk da yaji haushinsa amma haka nan daga inda yake tsaye yace "fad'i maganarka ina sauraronka." Shima Baba daga nan inda yake yace "Yawwa! Dama ina so ne na baka cigiya tunda har Allah yasa nace zan aurar da ita,ba tare da samun tsayyaye ba shi ne nake son shaida maka,ko da Allah zai sa ka samu wani mai rangwamen gata kamar ta da yake buk'atar auren,dan Allah ina rok'on alfarma ka sanar masa yazo gida na ina da matar da zan bashi sadaka.." Cike da takaici Alhaji zakar ya bi Baba da kallon sakarci ba tare da ya ce komai ba ya juya zai shiga gida,baba yaga yayi masa magana bai tanka ba hakan tasa shi sake cewa "Yawwa Alhaji,,nace tunda yake Allah yasa har kana ganin tayi k'arama da aure yanzun,kuma kai d'in kana da ma'aikata a gidanka,shin mai zai hana ko su ne ka nemawa d'aya daga cikinsu aurenta tunda kana tausayinta tayi k'arama da aure.. Ka ga dama jihadi kake son yi.. Shi ne sai naga zaifi kyau na sanar da kai,sadaki ma kad'ai idan ka biya ya wadatar a d'aura musu aure,daga nan sai ka ajiyeta a gidanka,kaci gaba da kulawa da ita ko itama ka bata aiki a gidan naka,tunda yake ni mahaifinta na yi ba dai² ba.." Maganar ta yiwa Alhaji zakar zafi,still bai tanka ba ya wuce gida ransa a b'ace har yaji nadamar samun Baba da maganar,shigarsa gida a cikin wannan yanayin suka yi maganar da Hajiya,yadda suka yi duka da baba ya sanar da ita tunda ita ta sashi shiga maganar tun farko,,Hajiya ta lallab'a ta kwantar masa hankali,followed by maganar ta akan me zai hana tunda har Allah yasa al'amarin ya zo da haka kuma Baba da kansa ya bashi damar neman auren yarinyar ga hadiman gidansa,su nunawa masa cewa maganar da yayi cikin izgili a shirye suke su tabbatar da cikarta..??,Alhaji ya zuba mata ido yana kallo cikin rashin fahimta but yayi k'ok'arin yin magana "Hajiya me kike son cewa..?" Tace "so nake ka amince da batun neman auren yarinyar." Yace "Hajiya wane irin batu kike yi haka.? Ni zan nemi auren k'aramar yarinya kamar wannan,sa'ar y'ata fa.?? Ita kike cewa na nemi aurenta..?? Yarinya y'ar shekara sha hud'u.? " Tace "Alhaji nifa ba kai nake nufi ba." Yace "to waye zan nemawa aurenta.? Kin san dai bani da ikon zartar da ko wane irin hukunci akan ma'aikatan gidan nan cos bani ke da su ba,mu kuma ba wani babban d'a namiji gare mu ba bayan Rafeek,idan munce shi,duka shekarunsa nawa suke.? Besides yanzun yake shekara ta biyu a jami'a." Hajiya tace "ni dai alhaji kawai kayi hak'uri da batun shekarunsa,wannan al'amari ne da ya kamata ace munyi iya kar k'ok'arin mu wajen ganin mun taimakawa marainiyar nan,ina tausayin rayuwar yarinyar nan har zuciya ta,kallonta nake kamar Maimunatu na,idan a yanzun da muke da dama bamu taimaka mata ba,mu yaya zamu yi a gaba..?? Kada fa ka manta taimakon maraya abune mai kyau,kamar yadda annabi (S.A.W) yace a hadisi:"Ni da mai taimakon maraya,zamu kasance kamar haka ✌🏻a gidan aljannah,sai ya raba tsakaninsu da wani abu,maleek (R.A) yayi nuni da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180