Chapter 98
Chapter 98
wanda raina ke hannunshi ni Aliya bazan kyaleku ba, sai na sa kun muzanta a idon duniya, yanda kikayi wasa da rayuwar 'yata kema sai nayi da ta naki yayan, mu zuba mu gani, wuce muje Hajja Asiya ta karashe hade da buga kofar dakin tana huci, Kuka sosai Mummy ta fashe dashi hade da ficewa daga dakin itama, a rude Musaddiq ya saki hannun Nadeeyah ya bi bayanta hankali a tashe, itama Nadeeyar mikewa tayi tana share hawayen da ya ziraro mata tana kokarin bin bayan Mummy Anty Raly ta dakatar da ita, zaunar da ita tayi ta rarrasheta da kalamai masu dadi da kwantar da hankali, jakarta ta ajiye kusa da ita tace "ki kular min da jakar nan, yanzu zan dawo... Sau uku wayar dake cikin jakar na ringing Nadeeyah na kin dauka, saboda bata san bude ajiyar da aka bata, a na biyar ne ta bude ta fito da Wayar, *Tahir Legacy* ta gani a rubuce, da sauri ta ajiye wayar saboda wani irin mugun faduwar gaba da taji, "uncle Taheer ta fadi a cikin ranta, gaba daya ta manta dashi a cikin rayuwarta, gashi yanzu zata sake yi mishi mantuwar din din din, bai fasa kira ba har saida ta gaji ta dauki wayar zata kaima Anty Raly sai a sannan taga wani suna daban, *Aunt S 2* a gaggauce ta dauka tace "Assalamu Alaikum bari in kai mata... yadda yayi haddar sanyin muryarta dake yawan yawo cikin kanshi ya tabbatar mishi da itace, "My omri is going lv me, dagaske ne? Chakkk ta tsaya da tafiyar da ta farayi, cire wayar tayi a kunnenta ta sake kallonta dan ta tabbatar da ko dai sunan gizo yayi mata, maida wayar kunnenta tayi zatayi magana yayi saurin cewa "tell me plss, zama ta koma tayi tace "ina wuni, "Nadeeyah plss answr me, "ummm dagaske ne, ta bashi amsa a hankali... ji yayi gaba daya ya kusa zubewa a kasa, dama lokacin da yagani a status din sabrinah saida yayi jinyar magudanar jininshi na dan lokaci, hawayen da ya ziraro mishi ya share, yace "but why Nadeeyah, why?? Cikin rawar Murya tace "Kaddara ta ce haka, kayi min addu'a Allah yasa auren ya zame min alkhairi, kayi hakuri uncle, Allah ya baka wacce ta fini a komai da kake so, bata jira jin amsarshi ba ta kashe wayar ta dunkule kanta guri daya, dama dakin babu kowa dan Husna sun fita da Hafeez da kawayensu..... Kaga abun da ka janyo min ko Musaddiq, kaga irin cin mutuncin da ka janyo min gurin aminai na, yanzu gaba daya kawayena zasuyi Allah wadai dani, saida na fada maka Nadeeyah ba alkhairi bace a gareni ka nace saboda kaga jar fata da kyawun dan maciji wanda zai diga maka dafin sa ya tafi ya barka da ciwo, Wallahi Musaddiq ka cuceni kuma ka cuci kanka.... Anty Reemah ce ta zauna kusa da ita tace haba Mummy, matar mutum fa kabarinsa, kuma babu wanda yasan alkhairin dake tattare da auren Nadeeyah sai ubangijin halittu, yanzu ita wacce kike so din me tafi Nadeeyah dashi, "Gata da hanyoyin alkhairi, Mummy ta bata amsa tana harararta, "Hanyoyin alkhairi ai na ubangiji ne, shi ke budeshi ga wanda yaso, sai kiga auren Nadee--- a harzuke ta katseta da cewa "in kika kara magana zan balain saba miki, mahaukaciyar banza sakaryar hofi, tashi ki fita ki bani guri, shashasha kawai... Rai a bace Anty Reemah ta tashi ta fita daga dakin, Matsowa Musaddiq yayi ya share mata hawaye hade da kwantar mata da hankalin cewa ta kwantar da hankalinta, babu abun da zai faru, domin shi zai gyara komai, Hannunshi Mummy ta kama tace "Little ka taimakeni, bayan auren da kake so kayi wanda nake so, ka auri Faida, shi kadai ne zai sanya hankalina ya kwanta, in kuma aminta da Nadeeya a matsayin matarka, shuru yayi na dan lokacin zuciyarshi na harbawa da karfi, tunanin mafita ya shiga yi, Dakyar ya sama wa kanshi mafitar amincewa, dan a samu zaman lafiya, amma ko yayi hauka bazai auri Faida ba, daga ya tafi da Nadeeyarsa lagos bazai kara waiwayosu ba sai yayi shekaru, ganin ya amince zai auri Faida yasa Mummy farin ciki sosai har ta kira aminanta ta fada musu..... Sai bayan Magriba akayi kamun amare, "Mami da Anni su suka kama Husna, sai Anty Reemah da sauran yan uwanta sukayi ma Nadeeyah, Mummy ma in ka ganta zaka dauka albishir akayi mata da gidan aljanna saboda murna, Rawa kam kawayen Amare da yan uwa suyi ta sosai har saida suka kure mawakin, sai kusan goma makadin ya tattara kayanshi yayi gaba da tarin alkhairai masu yawa, su kuwa kawayen suka koma dakin kwanansu suka cigaba da hirarsu ta yammata, rabin hirar tasu ma akan Badar ta kare saboda sun so tana nan akayi bikin..... Rana bata karya.... A ran 23 ga watan yuli.. ranar sati da safe dubban jama'a suka shaida daurin auren *Musaddiq Mukhtar Kyari* da *Nadeeyah Adam* da kuma auren *Hafeez Adam* da *Husnah Mukhtar Kyari*... Marokin gurin na gama sanarwa Jamal yayi dariya sosai yace "vice versa, gyara bakin madubi Hilal yayi yace "ai fa, abin ya burgeni, Allah ya basu zaman lafiya.. saura mu, matsowa Jamal yayi yace "ai ni nama gama samu, saidai fatan dacewa, jira kawai nakeyi komai ya lafa in aika sakon zuciyata, bazan tsaya kallon ruwa kwado yayi min kafa ba.... "Kamar yadda Nayi Hilal ya fadi a cikin zuciyarshi.. amma a fili cewa yayi "woww kace anjima akwai gist, "Sosai ma In law... au My son ya karashe yana dukan bakinshi.. Mikewa Hilal yayi yana kyakyata dariya yace "ka tona kanka malam, muje gurin walima kafin mutumin ya fara kumburi..... Wannan kukan da kikeyi bazai taimakeki ba Amarya, dama kinci abinci, da kin samu sauki, "Kinsan adadin matan da suka shigo gidannan ta haka kuwa? to ki sani bake bace ta farko kuma bana tunanin zaki zamo ta karshe, da yawa irin ku son duniyan iyayenku ke ja muku, saboda son abun duniya sai idonsu ya rufe suyi kyautar da zata damesu nan gaba, ta shi kici abincin, kingani harda Farfesun Zomo, ga tuwon lapshi miyar yauki gaskiya ke yar gata ce, dan abin bauta Garzar ki rage min, ta karashe tana turo langar tuwon gabanta, Kafa Badariyya tasa ta ture langar tuwon, nan naman ya zube a kasa, komai ya bayyanar mata, kan zomo ne da kayan cikinshi, sai tsirarrun nama, da sauri kande da ta durkusa tafara kwashe naman tana suďe hannu kamar mayya wacce tayi sabon kamu, Idon da ya soye da bakin ciki Badariyya ta bita dashi tana hawayen zuci, "wannan wace iriyar jarabawa ta fado, kalmar na shiga uku har lokacin bata bar fita daga bakin Badar ba, tana kallo kande ta sude gurin tass kamar an goge sannan ta russuna tace "Ranki ya dade, ko bakya jin yunwa bai kamata ki wulakanta abinci ba, wannan naman yanzu da zan fita dashi tsakar gida sai an kusa kaini kasa saboda wawason shi, ki daure kici ko kadan ne saboda kar yareemah yayi fada, tsakii mai karfi Badariyya taja hade da sake yin tagumi tana tunanin way out.. Shigowar Yareemah ne yasanya kande fita da sauri bayan ta gaisheshi... Zama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156