Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

yanzu kuma babban tashin hankalinta bai wuce na rashin walwalar da ta gani a gurin yar uwarta mai kaunarta ba, tana wannan tunanin taji Ma'u tazo ta wuce cikin dakin... Yanzu dai kinga halin wacce kika fifita akan yar uwarki, kindai gani da idonki, kuka zainab ta fashe dashi tace "Wallahi Goggo ina mutuwar kaunar muntari, na dauka zan iya hakuri in bar mata shi, amma yanzu da naga aski yazo gaban goshi walhy bazan iya hakura ba, duk abinda da kika ga ya dace kiyi Goggo, nima ko meye zan yi walhy, murmushi Goggo tayi a zuciyarta tace "wuya makarantar kare, waya fada miki borno a gabas take, kwantar mata da hankali tayi tace gobe zatayi komai da tasan zatayi ta rabasu,,, wani sabon kuka ne ya kufcewa Suwaiba da ta gama sauraren kalaman Goggo, mikewa tayi ta je bakin pampo tayi alwala ta dawo dakin, a zaune ta samu Leemah da yaya zainab suna magana kuskus, darduma ta dauka ta fito waje tayi raka'a biyu ta zauna a gurin tana kai kukanta gurin ubangiji.... Baffa na fasa auren muntari! Wata iriyar faduwar gaba Baffa yaji wacce zata iya sanya zuciyar bawa tsayuwa, hade rai yayi kamar bai taba dariya ba yace "wace irin magana ce kin fasa aure?, dama yardar aurenki da rashinshi duk a hannunki suke,? dama ke kike da ikon zabawa kanki miji bani ba, dan Allah ya kawo miki miji shine har kike da bakin butulce mishi, lallai suwaiba ban taba tunanin baki da hankali ba sai yau, idan kika sake furta min wannan kalmar walhi sai na lahira yafi ki jin dadi, tashi ki bani guri sakarya kawai.. tashi tayi ta fita tana kuka a ranta tana fadin nima ba asan raina bane Baffa, ina gudun a sabauta rayuwata da ta muntari ne, ya zanyi in fahimtar dakai akwai matsalar dake shirin bullowa, ya zanyi ka fahimci matarka wacce na dauka uwa marar kaunata Guba ce a cikin rayuwarka, da wadannan tunanin ta isa zauren gidansu ta zauna akan dakali ta cigaba da kuka, saida ta dauki kamar minti talatin a gurin sannan ta tashi ta wuce makaranta... A dimauce ya dago kai ya kalleta sosai yace "maimaita abin da kika fadi, cike da dakiya tace "kayi hakuri dan Allah ka janye batun auren mu da kai, wallahi zuciyata ta kasa aminta da yin rayuwar aure dakai, share zufar da ta keto mishi yayi yace "karyane! Wadannan kalaman ba naki bane, ko kina da ciwon aljanu ne ban sani ba? Hawaye ne ya fara zuba a idonta tace "Gaskiyar magana nake fada maka daga cikin zuciyat---- karya kikeyi! Ya daka mata tsawar da sake sanya ruwan idonta ambaliya, sauke muryarshi yayi yace " baki da lafiya suwaiba, kin gane ko, jeki gida ki kwanta, "lafiyata kalau ta fadi murya na rawa, ka fahimceni, rayuwar aure bazata yiwu da zuciyoyin da basu gama yarda da junansu ba, nayi duk iya kokarin da zanyi in tusa sonka a raina na kasa, kallonta yakeyi da manyan idanuwanshi da suka rine zuwa jajaye, "me yasa kike kuka? Karki damu share hawayenki, share hawaye tayi da sauri, yauwa ya fadi hade da cewa kar in sake ganin kukan nan kinji ko? Gyada mishi kai tayi tace "na daina, "kin min alkawari? Eh "Nayi! Yauwa matar Muntari, kin gane ko, dama ni bana son ki soni, son da nake miki ya isa, ni fa ina sonki ne badan ki soni ba, so karki damu zanyi maneji, ko ba komai in na dawo gidana nasan da abin da nake so zan fara tozali, gyara tsayuwa yayi yace "baki san ke din sarauniyata bace, in kina gurina a killace to bani da wata damuwa, dan haka bana san jin komai je ki gida ni zan tafi, ko kina son wani abu? Wani kukan take kokarin sake yi yace "mutum dai yasan hukuncin mai saba alkawari! Nidai ba ruwana, kamun Allah bana mutum bane, share hawayen tayi da sauri ta ruga gida.. Kwantar da kanshi yayi akan sitiyarin motar zuciyarshi na azalzala da kalamanta, ya zaiyi in da gaske ya rasa Suwaiba, da wace mace zai iya rayuwa in ba ita ba, sake kallon kofar gidan yayi sannan ya tada motarshi ya wuce gida jikinshi duk a sanyaye.... Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba, Suwaiba ta daina fita gurin Mukhtar, ko yazo saidai ya karaci tsayuwarshi saboda rashin baffa a gari, Ana jibi daurin aure ne ta fito ta sameshi, a wannan ranar saida ya nuna mata irin nashi bacin ran kafin ya tafi ranshi a bace, yana mata uzurin yarinta da kuma bata san meye kalmar so ba, gidan su Abbakar ya wuce direct, cikin bacin rai yake magana yana fada mishi yadda al'amura suka sauya cikin kankanin lokacin, "Abbakar kai kadai zaka mata magana, wallhi ina shiga cikin matsanancin hali in naji tace "bazata aureni ba, yarintar ta bata gaya mata gaskiya, in ba haka ba sai ka kalli mutun kace baka kaunarshi, Shiryawa Abbakar yayi suka wuce gidan su suwaiba, dakyar ta sake fitowa, har saida ma'u tace ta fita, ita duk tunaninta asirinta ne ya kama Suwaiba, bata san kauna ce ta sanyata hakura dashi ba, tasani tunda sukayi alwashi zasu iya rabasu kuma ta zauna a gidan su gasa mata aya a hannu, gara ta hakura dashi ya auri yar uwarta ko zasu samu maslaha da ita, dan a yan kwanakin nan ta jigata da rashin kulawar da Zainab take bata.. "Abokina yayi laifi ko? Rufe fuskarta tayi murya na rawa tace "A'a, to meya faru?, fada min a matsayina na uncle dinki, kuka ta fara yi kamar yarinya karama tace "nidai kawai bana sanshi ne, kuma yaki ya taimakeni yace ma Baffa bazai aureni ba, runtse ido Mukhtar yayi kirjinshi kamar zai fado kasa, matsowa kusa da ita yayi kamar zaiyi kuka yace "nasan bakya sona, kiyi hakuri ki bani amanar rayuwarki, nayi alkawarin koya miki sona, wani abu taji tun daga kanta har tafin kafarta, "meyasa Ya Allah, meyasa na samu gatan da zaisa in zama lele kuma yanzu gatan zai subuce min, meyasa, wannan shi ake kira da Dandani haukaci, a fili kuma kukan dai ta cigaba dayi tace "ni bazan iya jure zama dakai bane, uncle Abu dan Allah kace yayi hakuri ya nemi wata, "bazanyi hakurin ba, Abbakar yarinyar nan bata da hankali, rabu da ita kazo mu tafi, in an daura auren ta mutu, kafadunshi Abbakar ya dafa yace "calm down kyari, hannun ya ture kafadun shi yace "dan taga ina lallaba ta ne, wallahi abinda zai hanani aurenki saidai mutuwa, ko kuma dama bani da rabon zama dake har mu samu 'ya'ya, amma in har inada jini a jikinki sai kin aureni (Rabon yayi muku wannan farraqun), yana kaiwa nan ya fita yana huci kamar zaki, Duk irin lallashin da uncle Abu yayi mata ta kafe akan ita bata sanshi, har yaji haushi sukayi sallama, kafin yakai kofar fita yaji ta rushe da kuka mai ratsa zuciya, tsayawa yayi yana kallonta a ranshi yace tabbas akwai matsala, haka nan bazata ce bata son kyari ba, koma menene Allah ya kawo mata mafita.... *RANAR AURE* Tun da suka idar da asuba Suwaiba ta wuce islamiyyarsu ta zauna can wani lungu

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156