Chapter 5
Chapter 5
wannan bakar zuciyar taka, kai a kullum duk inda kaje sai Kasa mutane sun tafi da kai a baki, meye amfanin rashin hakuri, abin da hakuri bai baka ba wallahi rashin shi bazai taba baka ba, duka nawa kake kaima da kake barin zuciya tafi karfinka, wallahi kayi gaggawar sauke bakar zuciyarka har mu bar kasar nan in ba kanaso inyi mummunan saba maka ba, sakarai kawai, "haba anty sorry mana, ba fa wani abu yace min ba, musaddiq ya fadi cikin tausasawa hade da kama hannunta, kallonshi tayi cike da son halinshi tace ko baice maka komai ba meye amfanin abun da yayi a gida, "mum nifa babu abin da nayi, kawai dai gaskiya ce bakwa so, shiyasa Sam bana son shiga gidanku saboda ni ba na gani in kyale kuma in nayi kuce nayi rashin kunya, Allah ma yasan akan gaskiya na-- rufe min baki anty reemah ta fadi hade da bige bakin a hankali, Janta musaddiq yayi suka bar dakin tanata masifar da Sam bata karbeta dan ba sabawa tayi ba, kullum cikin bakin cikin halin danta takeyi wanda Sam bai biyo halinta dana ubanshi ba, da ya tashi sai ya dauko halin mamanta har ya damata ya shanye saidai shi Sam bashi da neman suna kuma komai zaiyi sai yanada hujja... Ruwa musaddiq ya bata tasha yace "kiyi hakuri anty kin so ki bata ranki ne, kinsan halin Hilal, babu mai iya canza shi sai Allah, kuma kin San duk abin da zaiyi akan gaskiya yakeyi he is open, baya barin abu a ranshi, dole ya koyi barin abu a ranshi musaddiq, Reema ta fadi tana mai ajiye kofin da ta sha ruwa,! meye amfanin duk abun da akayi ma mutum yace sai ya rama, wani lokacin ma ba dashi akeyi ba sai ya sako kanshi saboda shi baya gudun bakin duni-- kwanciyar da taji anyi a bayanta ne ya hanata karasawa, kamshin turaren da taji ne ya sanar da ita ko waye, Kara tamke fuskarta tayi hade da Jan tsaki, cikin muryarshi ta yan gayun yaran hutu yace "ki daina gudun bakin duniya Momma na, in dai duniya muke son mu burge to lallai munada aiki babba a gaban mu, "chapter closed", am so sorry for hurting you mum, wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta hade da kara kaunar dan nata, duk iya inda yakai da zuciyarshi ya tsani bacin ranta, baya daukar mintina sai yasan hanyar da yabi ya wanke zuciyarta, dariyar farin ciki musaddiq yayi "yace komai ya wuce ''aunty momma!! , murmushi tayi hade jan kunnuwansu, zama sukayi suka sata a tsakiya suna mata hira kamar babu wani abu na bacin rai daya gifta a tsakanin su,, karar da wayarta tayi ne ya katse musu hirar, zaro ido tayi ta mike tana fadin ya ilahi hade da daukar wayar, sorry Rally shaff na mance da ku, daga dayan bangaren Rally tace ai na Lura da hakan, gashi har mun gama komai, cikin farin ciki Anty reema tace kinyi komai simple dai ko, kinsan komai namu very simple muke yinshi, saima kin gani anty, abin sai ya burge ki ta fadi tana gyara balloons din da sukayi kasa kasa, ok thank u babe, gamu nan Zuwa, juyowa tayi tace kuje ku shirya ku raka ni wani guri, Hilal da ya riga ya harbo su yace ni a shirye nake mum, bata kalleshi ba ta kamo hannun Musaddiq sukayi daki, a cikin sababbin kayan da ta siyo mishi ta zaba mishi tace ya saka ta fita ta bashi guri, saida ya dau minti goma yana shiryawa, jar riga ya saka mai matukar kyau da deep blue wando, ya taje kwantaccen gashin shi, kyawun bakar fatarshi mai sanyi ya kara bayyana, hatta madubin da ya kalla yasan babu karya shi din mai kyau ne matuka,, fitowa yayi cikin takunshi na nima na fara girma, kallon kauna anty reema ta bishi dashi tana fadin wowwww kanina, babu kamarka a wannan zamanin, gaskiya kayan nan sun karbe ka, sajenshi ta shafa tace "Allah ya nuna min aurenka dole in zauna da matar saboda kar ta cutar min da kai, Hilal ya ajiye cup din coffee yana dariya yace saboda kinsan uncle din nawa is nt brave ko, zanci ub-- toshe mata baki yayi da sauri hade da rungumeta yana dariya harda kyakyatawa, tureshi tayi tace "wallahi yaron nan ya rainani sosai, zanyi maganin ka, dariya suka saki Hilal ya dauko keyn mota Kan centre table yace oya mu wuce, Anty reema ta kalleshi Sama da kasa tace da wannan wandon zaka fita,,, pls mum karki fara muje kawai ya fadi yana wani narkewa, hmmm kawai tace ta kama hannun musaddiq suka fita Zuwa gurin Mota..... Mrs Tijjani Shattima.....! [04/12 09:44] Meela Adeel: 7⃣ °ZUMUNCINMU A YAU ° By Aysha Ya'u Kurah Mamma duba min kiga kwabin yayi haka, mamma dake kashingide ta dan mike ta kalli kwanon madarar da Nadiya ta kwaba, hannu tasa ta dan taba ta gutsuri kadan tasa a bakinta, "mmmm gaskiya yayi dadi kuma yayi danko ta fadi tana lumshe ido alamar santi duk dan ta kara ma diyarta kwarin gwiwa, murmushin Jindadi Nadiya tayi ta ajiye a kan tabarma ta shiga kitchen ta dauko leda da kwalbar da zata murza madarar, Cikin nutsuwa take murzawa tana yanka su kanana tana sawa cikin wata tsaftatacciyar robar sweet da ta amso a shagon Tasi makocinsu, hira sukeyi cikin jindadi mamma na taya ta kirga wadanda ta yanka, saida suka gama tsaf, Nadiya ta kalli mamma tace "Mamma in rokeki wani abu, mamma ta karashe rufe robar tuwon madara tace fadi kanki tsaye yar albarka, Dan Allah Mamma kiyi hakuri ki daina yin "wankau" ban taba Jin zafin masu yi min gorin kina wankau ba sai yau da Nafi'un Baba Atika yayi min a shagon Tasi, wai masu wanke daudar wasu bazasu taba yin arziki ba, Dan Allah mamma ki daina, in shaa Allahu wannan karamar sana'ar da muka fara zata dinga rufa mana asiri da dan abun da baba da yaya hafiz zasu samo, tunda ta fara maganar idon mamma ya ciko da kwalla, kauda kanta tayi ta dan share da gefen zani tace "Nadiya wanki baya kawo talauci duk canfin hausawa ne, saidai zan daina saboda in karfafa gwiwar ki tunda hakan kika bukata, sannan zamu hada da ruwan kankara saboda yayi karanci a unguwar nan, wani farin ciki ne ya lullube Nadiya tace "alhamdulillah" nagode mamma, bari inje in kaiwa Tasi dan yace ina gamawa in kawo mishi, gyada kai mamma tayi tace "a kai da bismilla Allah yasa mishi albarka, Ameen Nadiya tace tana kiciniyar sa hijab dinta, karo tayi da samari biyu suna kutso kansu gidan hade da sallama, da sauri taja da baya ta kame jikin bango saboda irin kallon da Hilal yake yi mata, tsaki yaja hade da kakkabe kayan jikinshi ya wuce, kanta a kasa ta gaida musaddiq ta raba ta gefenshi ta wuce, binta yayi da kallo zuciyarshi a karye, Allah kadai yasan irin tausaya musun da yakeyi, yarinya karama tasan wahalhalun rayuwa, muryar Anty Reemah ya jiyo tana tambayarta inda zata, sunne kai tayi tace "zanje shago ne in kai tuwon Madara, Hinad ta kalli hannunta tace "wow dan sammin, budewa ta fara kokarin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156