Skip to content

Chapter 116

Chapter 116

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

abunda zai je ya tarar.... A airport din su Daddy suka jira zuwan su Papy dan su karasa tare, Yanayin da Papy yaga Daddy ya ďaga mishi hankali matuka, kusa dashi ya matso yace "Kayi hakuri Alh Mukhtar, cuta ba mutuwa bace, in shaa Allah zai tashi, kukan da Daddy baiyi ba jiya shi ya saki mai karfi haďe da rungume Papy, share hawaye Anni tayi tace "Mu karasa can asibitin dan Allah, ba sai mun tsaya munyi magana anan ba... jiki a sanyaye Papy ya kama hannun Daddy yana bashi hakuri har suka isa gurin motocin da abokin Daddy ya turo musu... A kofar dakin da aka sa Musaddiq sukaga Hilal rungume da Hijab har lokacin idonshi na fitar da ruwa, daga shi har Zubair babu wanda ya runtsa, yana ganinsu ya mike da sauri ya rungume Daddy yace "Wallahi Daddy sun kasheta, Nadeeyah ta mutu, muje kaji daga bakin doctor... A ruďe Mami tace "Wace Nadeeyar, sai a lokacin Hilal ya lura dasu, nan wani sabon kukan ya kwace mishi ya shiga basu labarin abun da yaji da kunnenshi, Abbati da ya kira Daddy yace su haďu a asibiti shima ya daura daga inda ya sani, nan fa guri ya kaure da kuka, sun ma manta a asibiti suke, Jan Daddy gefe Abbati yayi yace "Ni yau zan koma india, yara kuma sun wuce katsina, na faďa ma Raudha in ta samu miji tayi aure, kayi hakuri dan Allah, Allah ya haďa mu da alkhairi, Murmushin yake Daddy yayi yace "Allah ya albarkaci rayuwarka Yusuf, ai kayi kokari, nagode sosai, Duk da Papy na cikin tashin hankali hakan bai hanashi mikewa da niyyar yi ma Abbati magana ba, rikeshi Daddy yayo yace "Ya cika dan halak, kowa hakan zaiyi in yaji abin da suka aikata, "Dan Allah ka yafe min proff, da sauri Papy yace "Haba, mu su waye da zamu tsallake hukuncin ubangiji, itama lokacin da ta dauko kenan, rayuwarsu ta jin daďi na gidan lahira in shaa Allah, yadda ya karashe maganar cikin rauni ya sanya su sake wani sabon kukan, Duk papy yadda yakai ga matsewa ya kasa saboda shima a karye yake, nan ya zauna ya rufe fuskarshi yana kuka sosai, a duk faďin gurin nan babu wanda yakeda karfin bawa wani hakuri..... Reemah... ki kira danki kice mishi ya dawo min da ďana, tun daren jiya da ya daukeshi ya fita dashi har yanzu basu dawo ba, ki kirashi ya dawo min dashi, tunda shima yana san Nadeeyar in ta gama idda sai ya aureta kuje can ku karata, tunda ke baki san ciwon kanki ba, ki haifi ďa ya dinga juyaki... Mummy na kaiwa aya Anty Reemah tace "Ina airport, danki yana asibiti, ďana bai kai ga yi mishi illa ba, ita kuma wacce kika tsana din da zata dawo gidan duniya da babu abinda zai hana ban aura mata Hilal ba, ai da nasan yasota tun farko da saidai Musaddiq ya hakura tunda shi matsayin uba yake a gurinshi, saidai kashh... yayi nauyin bakin da ya jefa rayuwar Nadeeyah cikin garari, yanzu tunda kunyi sanadiyyar da ta zama gawa, sai ku fara murna ku nema ma Musaddiq hurril aini, tana kaiwa ta katse wayar cike da ďacin rai, bata taba yi ma mahaifiyarta musu ba, amma a yau ta kai bango sosai wanda har ya sata fadin maganganu cikin ficewar hayyaci.... A gigice Mummy ta nemi guri ta zauna tace "Nadeeyah ta rasu, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Raudha dake kiran wayar Abbati tana kuka tace "Whatt... ta rasu? "Wallahi ta rasu, yanzu Reemah ke faďa min, itama tana hanyar zuwa.. Daukar trolley Radiya tayi da sauri tace "Nidai ba ruwana, yanzu nan zan tafi gida gurin 'yayana, Allah ya taimakeni Shamsu bai san labarin nan ba, kallon Raudha tayi tace "Allah ya daidaita ku, Mummy, na tafi kaduna sai kun karaso, tana kaiwa nan ta ruga da gudu da jakarta tana mai dana sanin biye ma zuciya.... A tsure Mummy ta mike ta kira wayar Mahmoud tace ya tambayar mata Zubair wani asibiti suke, Mahmoud ya rude sosai ya kira Zubair dan jin abinda ya faru, sunan asibitin kadai ya iya faďa mishi ya kashe wayar saboda tashin hankalin da suke ciki na cewa Musaddiq ya shiga Coma, Kiran Mummy yayi ya faďa mata sunan asibitin, bata jira abinda zaice ba ta mike ta sanya gyalenta suka wuce tare da Raudha, burinta Allah yasa ba'a faďa ma Daddy abinda ke faruwa ba, tasan yadda zata lauya zancen har ya gamsu da ita.. Kuka ta kakalo ta dinga yinshi cikin motar da zata kaisu asibitin... Da Hafeez ta fara karo yana zaune a bakin gate din asibitin yana kuka sosai, Husna dake tsaye a bayanshi ta dafa kafadunshi a tsorace itama kukan takeyi, kukan rashin Nadeeyah da kuma kukan hali irin na Mahaifiyarta, Mummy na ganinsu ta fito daga cikin mota ta nufosu tana kuka, da sauri Husna tace "Dan Allah karki iso nan da dramarki Mummy, kun kasheta, hankalinku ya kwanta, sai kuyi celebrating ai ba kuka ba, Cike da mamaki ta kalli Husna tace "Auta ni kike faďawa haka, har kin yarda zan iya kashe Nadeeyah da nake so kamar raina, "So indeed, yaushe kika fara sonta? So bayan rai ko, wallahi alhakin Nadeeyah bazai barku sukuni ba, i ha---- toshe mata baki Hafeez yayi yace "Don't say anymore, uwa uwa ce, rungumeshi tayi tana kuka sosai haďe da bashi hakuri.. bayanta ya shiga shafawa yana kwantar mata hankali, yasan irin kaunar dake tsakaninsu, abin da mahaifiyarta tayi bazai taba shafar zamansu ba saboda Zuciyar Husna kamar gold take saboda kyalli.... Bayan sun tsagaita kukan Doctor ya basu shawarar da su bi manyan asibitoci su duba gawarta a samu a sallaceta cikin gaggawa, Suna cikin yanke shawarar yadda zasuyi Mummy ta faďo gurin da suke tana ihu mai haďe da kuka, babu wanda a cikinsu ya kalleta bare har yasan abun da takeyi, Ganin tana neman cika ma yan asibitin kunne yasa wasu Nurses cewa tayi hakuri ta fita daga waje, tana damun patients dinsu, "Sirikata ta mutu sannan ďana na kwance rai a hannun Allah zaku ce inyi shuru, bazanyi shurun ba, ya Allah ka sassauta min, wayyo Allah na shiga uku, Gadan gadan Daddy ya nufota dan ta kure duk wata dauriya tashi, tana ganinshi gab da ita tayi saurin mikewa tana share hawayenta, cike da kissa ta faďo jikinshi tace "Ance Nadeeyah ta mutu, daga sokoto na biyo jirgi na iso nan direct, me ya samu Nadeeyah, me ya sameta?... ta karashe tana kuka sosai, Ran Hilal ya baci matuka na rainin wayon da tazo dashi yayi saurin mikewa zaiyi magana Jamal ya rikeshi, danne hannunshi yayi yace "Karkayi magana, duk lalacewa ita ta haifi mahaifiyarka, dafe kai Hilal yayi yace "shine abun da nake jin haushi matuka, ina ma ace bare ce, wallahi hukuncin da zan mata ba mai sauki bane.. Raba jikinshi yayi da ita haďe da kama hannunta ya fara janta har suka fita waje, bayansu Papy yabi yana cewa "Kayi hakuri Alh Mukhtar, ka kyaleta sai mun koma gida, yanzu fatan mu Allah ya bawa Musaddiq lafiya, kuma Allah ya bayyana mana gawar Nadeeyah cikin gaggawa, Bai saurare shi ba ya hankaďata

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156