Skip to content

Chapter 33

Chapter 33

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

sanďa wani sumameshi ya luma mishi wuk'a a bayanshi saitin da zuciya take, nan take ruwa mai karfi ya kece a cikin kauyen, wani irin ihun murna arnan suka fara yi dan duk sunbi musulman sun musu kisan gilla, harda matansu da ya'yansu, cikin murna suka nufi cikin gidan suka fara kwaso shanaye suna bi takan gawarwakin.... Ma'u kuwa tun tana jiyo ihu har ta daina ji, anan ne jikinta ya bata an gama komai,, cike da murna ta fito gida da niyyar zuwa gidan Haire, a kofar gidan taci karo da Baffa da kaya niki niki a hannu, karbar kayan tayi ta fara murna suka shiga cikin gidan, a tsakar gida ya baje kayan yana bata labarin irin abubuwan alkhairin da ya samo, "Ta ina ka shigo garin nan? Ta jefo mishi tambayar tana kallonshi hade jiran amsa, " Ta bayan gari, saboda bana sann kowa ya rigani fada muku isowa ta, yanzu wanka zanyi in wuce gidan Malam, naga garin ma ba kowa nasan duk suna can maza da mata ana sallar juma'a da wa'azin Hardejo, cike da kissa tace "nima ko sai muje dan bacci ne ya daukeni ban samu zuwa ba, dube dube taga ya fara yi tasan tabbas Atika yake nema, murmushi tayi tace "Amarya tana can gidan Hardejo, ka tafi kabar amarya da nauyinka, nace su Baffa ba'a cika min alkawari ba, cikin rashin fahimta yace "me kike nufi? murmushi tayi a ranta na mugunta ne amma a fili ta nuna na soyayya ne tace "matarka dai ciki gareta, tama kusa haihuwa, a daburce yace "ma'u ban karya miki alk---- katseshi tayi da sauri tace "babu komai ai matarka ce, ni fatana ma mu samu dan namiji tunda naga dukkanku baku da namiji, kaga sai mu samu magaji, murmushin farin ciki Baffa yayi ya mike yace "dauko mayafi mu tafi, zunde tayi mishi ta baya sannan tace " har ka fara zumudi, nima bakaga yadda na kosa ba, komai a gidan nan bana barinta tayi, ganin cikin nema yasa hankalina ya kwanta dan ina tunanin namiji zata haifa mana, rungumeta Baffa yayi cikin farin ciki yace "Ma'u shiyasa nake kara kaunarki, tun farkon haduwar mu kike min halacci har kawo yanzu, nagode nagode, gwalo tayi ma bayanshi tace "Ai mun zama Daya Baffa.... Tun a bakin gidan jauro suke karo da gawa har suka isa kwanar gidan Hardejo, wani irin ihu Baffa ya saka da yaga Hardejo kwance cikin jini ruwan da akayi ya dama gurin, girgizashi ya fara yi ya dinga rusar ihu yana fadin waye ya aikata haka a gareka, waye ni, wayyo ni Allahn Hardejo, Dafa shi wani dattijo yayi a cikin wadanda suka gudu yace "Tashi Muhammadu, yanzu ba lokacin wannan bane muyi gaggawar haka rami a cikin gidan hardejo mu tattarasu duka musasu a ciki domin kuwa yanzu makasan sun tafi hada walimar murna kafin su dawo su mamaye gidajen, kuma kaima muna gamawa ina umartarka da ka gudu da kai da iyalinka, mikewa Baffa yayi a tsorace yana kuka suka shige gidan su biyar da wasu samari, a cikin gidan ma ya daburce ya dinga kuka yana kiraye kirayen suna, ita kuwa Ma'u rashin ganin Atika cikin gawar wakin ne ya fi daga mata hankali, kar dai ta samu ta tsere, dube dube ta fara yi har ta kai ga bayin gefen dakin saudatu, Atika ta gani tana kuka tana nishin nakuda, da sauri ta tufe bayin ta koma gurin su Baffa, duk wanda a cikinsu taga zaiyi gurin sai tayi maza ta hanashi, hak'a rami sukayi mai zurfin gaske da tsaho, suka fara dibo gawarwakin suna turawa a ciki, saida suka gama tsaff ta Hardejo ta zama ta karshen sawa, fuskarnan tashi dauke da murmushi, wani kukan Baffa ya saki yana zuba kasa a kanshi yana rusa kuka, saida suka gama komai sannan hankalinshi ya dawo kan Atika da bai ganta ba, Ma'u in dai ba idona bane yake min gizo banga Atika ba,, kafin Ma'u ta bashi amsa sukaji kukan jariri da karfin gaske, runtse ido Ma'u tayi tace shikenan yazo duniyar, da sauri Baffa yabi ta inda yake jin kukan, kofar bayin ya tura da karfi, a durkushe ya sameta tana dada dafe cikin alamun akwai wani a ciki, daukar jinjirar yayi sannan ya taimaketa ta fito suka wuce dakin Aisha, bin su Ma'u tayi tace bari in taimaka mata, Kamar zautacciya ta dinga maimata yan biyu kyautar Allahn Hardejo, tsaye yayi akansu ya rufe ma jinjirar hannunshi jiki da zanin mai babban suna, saida ta kara awa daya sannan ta haifo Danta kato namiji, cike da yake Ma'u tace "tafi ka nemo abin da zamu yanke cibi, wani abu mai kaifi Atika ta sanya a hannun Ma'u, harararta tayi ta yanke cibiyar, kallon jinjirar hannunshi tayi tace "dame aka daure cibiyar, zanin jikinta ne ta yaga ta daure dashi, kallon ta ma'u tayi a zuciyarta tace duk a ina ta koyo wadannan abubuwan, wani tsumman ta kuma yaga ta katsewa ma'u tunanin da takeyi, amsa tayi ta daureshi sama sama, ta kuma dukunkuneshi ta hana Baffa ya daukeshi, saboda rashin imani Ma'u na ganin jini na ambaliyar fitowa daga jikin yaron tayi banza da alamarin, kuka sosai yaron keyi amma saboda kawaici Baffa yaki yunkurin karbarshi, a ganinshi ma'u ma uwa ce a gareshi, kuka Atika ta fara yi ta yafito Baffa da hannunta, tsugunawa yayi a gefenta shima cikin kuka yace "bana gane abinda kike cewa, cikin yaren fulani wanda ta fara fahimta kadan kadan tace " *SUWAIBA* Shine sunanta,, sunan ummuna,,, shi kuma *SAIFULLAH* in har ya kasance cikin rayayyu, Ka kularmin dasu, Amanarka ne su, Dan Allah ka Nemi *Ateek* da Abbuna dan Allah.. kuka Baffa ya cigaba da yi sosai yana fadin bazaki mutu ba, ki yafemin dan Allah, share mishi hawaye tayi tace "Inda zan tafi ya fiye min nan, son samu ma in tafi da 'yarana, Allah yayi bazan rayu dasu ba, Muryar samarin sukaji a waje suna fadin ku fito mu tafi Muhammadu gasu nan dawowa, da sauri ya mikawa ma'u jaririyar ya dauki Atika a kafadunshi suka bar gidan da sauri... Tun a hanya ma'u ta gane namijin ya cika, nan fa hankalinta ya kwanta sosai, suna shiga gidan yayi saurin shimfidar da Atika ya dauko ruwa yana shafa mata, salati ta farayi idonta ya fara kafewa, ta kara cigaba da kiran sunan Allah, ga jini har lokacin zuba yakeyi kamar famfo, cikin tashin hankali yace ma Ma'u ta taimaka ta kawo maganin da take sha idan ta haihu, kwantar da yaran tayi taje ta dauko MANDA mai tsinka jini ta jikata da yawa ta kawo mata, dago kanta tayi tasa a bakinta ta dure mata shi tasss, wani jinin ne ya kuma tsinkewa shaaaaaa, nan da nan ganin Atika ya dauke, hannuwanta suka saki gaba daya, babu abin da kake iya jiyowa sai sautin kukan jinjirar da maganar Atika, *SUWAIBA* Sunan da take ta maimaitawa kenan hade da kalmar shahada..... Mrs Tijjani Shattima..... [04/03 11:57 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣7⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* *KADDARA* _Ba wanda ke shigowa cikin rayuwarmu ba tare da wani dalili ba, tun daga ranar da aka haifemu har izuwa ranar mutuwar mu, da kowa muka

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156