Skip to content

Chapter 62

Chapter 62

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

Ya Musaddiq.. Daddy yana kiranka, Husnah ta fadi tana ajiye wayar da Daddy yayi kiranta, maida kan Nadeeyah kan pillo yayi, ya sauka suka fita a dakin tare da Anty Raly domin kaiwa baki abin ci da sha... "Baki da karfi dama kika fara *Soyayya* dagowa tayi ta kalleshi, tsareta yayi da ido kamar bashi yayi maganar ba, "ni bana soyayya, ta fadi hade da rufe fuskarta da hijab dinta, faduwar gabanta ya karu sosai, nade belt din hannunshi yayi yace "in ma kinada niyyar farawa gara in tuna miki, kije ki koyi fada, dan in baki da karfi zaki cutu a soyayya, ko tsoron maza bakya ji kin wani tsaya gab dashi, to da bamu zo gurin ba me zai faru kenan? Shi--- runtse idonshi yayi maganar ta makale a makoshinshi, a zuciyarshi yana neman tsari da shedan dake kawata mishi abubuwa marasa kyau, canza maganar yayi da cewa "wuyan baya miki zafi, in yana miki zafi kiyi magana a kaiki asibiti, "Murya can kasan makoshi tace "zai daina in shaa Allah, yana yi kadan kadan, Dauko waya yayi a aljihunshi ya danna number Hinad, tayi ringing sau biyu, a na uku ta dauka, "ina Zee,? jin ya ambaci sunan Zainab yasa ta mikewa zaune, "bata nan ya Hilal, sun fita da *Anty Mee*, kashe wayar yayi ya kira Meerah taki dagawa, wayar na katsewa tata ta shigo, video call, tsaki yaja ya dauka, "Hi dear, ta fadi tana daga mishi hannu, "Hello Meerah kina lafiya? Kamar yadda ka gani am very ok, but am missing yha, ta fadi a shagwabe, kauda zancen yayi ta hanyar tambayarta "where is Zee? Juya wayar tayi zuwa gurin Su Adeel cikin muryarta mai dadi tace "say Hi to Ya Hilal, fitowa tayi a cikin motar wasan yara ta bude hannu hade da cewa "oyoyo! Murmushi yayi yace "yawo, kika fita yawo baki fada min ba, nt good baby, karbar wayar tayi ta bata fuska tace "wayau zaka min ko, dan kaga na hakura bana kuka har yanzu, ka gudu ka barni baka kaini gurin Adda na ba, Tun Nadeeyah na rike murnarta najin muryar gudan jininta, har ta kasa tayi saurin zuwa gurinshi zata karbi wayar, hada ido sukayi tayi saurin maida hannunta, dariyar da bata fito fili ba yayi, sannan ya mika mata wayar, da sauri ta karba sukayi ido da ido da abar kaunarta, safa da marwa ta shiga yi suna hira cikin farin ciki harda yar kwallarsu, murnar ganin yadda zainab ta koma ya hanata sukuni ta dinga yi mata tambayoyi, sun fi minti bakwai suna hira sannan tace "ga Anty Mee ku gaisa, tana kula damu sosai ni da Ya Hilal, kallon juna suka yi na seconds kafin Nadeeyah ta saki murmushi tace "ina wuni, amsawa tayi itama tana mata musayar murmushi, yadda take jin sunan Nadeeyah a bakin Hilal ya tabbatar mata da lallai ganin da tayi mata yafi jinta, domin duk kushen mai kushe bai isa ya nemo aibun Nadeeyah ba, kyawunta na musamman ne, gashin da yayi kwance a gefen farar fuskarta su sukara kara kawata kyawunta, gashi in tayi murmushi ko dariya gefen kumatunta daya ke lotsawa can ciki, haka nan Meerah taji wani abu ya darsu a cikin zuciyarta, ita kanta Nadeeyah da bata cika lura da abu ko sanyashi a ranta ba taji wani abu kadan game da Meerah, kallon farko da sukayi wa juna dukkansu suka fahimci jininsu yayi nisa gurin haduwa, shurun da sukayi suna kallon juna ya sanya Zainab karbar wayar suka cigaba da hira, Tunanin inda ta taba ganin Nadeeyah meerah ta shiga yi, dakyar ta iya tunano sketch din da yayi a school as assignment, duk da wancan da dan yarinta sosai amma ta gane ita ce, lokacin duk wanda ya tambayeshi sai ya amsa cikin shakiyanci yace "My dream girl, a mafarki na na hadu da ita shine kamanninta suka mannu a zuciyata, nan da nan kamannin Meerah suka canza, zufa ta fara karyo mata tace "Zee bani wayar nan, mika mata tayi ta zauna kusa da ita, "Bani Hilal pls, tace ma Nadeeyah fuskar ta babu yabo babu fallasa, sai a lokacin Nadeeyah ta waigo ta kalleshi dan ta manta ma yana dakin, juyar da wayar tayi inda ake iya ganinshi ba tare da ta sani ba ta sunkui da kanta kasa, wani irin kallo Meerah ta hangoshi yana yi ma Nadeeyah wanda bata taba sanin ya iyashi ba, lokacin da ta mika mishi wayar bai kalleta ba ya fara kokarin kasheta, da sauri Meerah tace "Kangiwa kana ji na? "Yes Meerah Turaki ina jinki, yadda ya kirata ya tabbatar mata yana cikin shauki, "ina kabar Musaddiq, ta fada tana jin wani mugun kishi a cikin zuciyarta, sai a lokacin ma ya tuna da Musaddiq yace "auchh yana daki may be, ko Daddy ya aikeshi, bari in dubo shi will call u, ya katse wayar kafin ma ta sake magana, Yana kashe wayar Husnah ta shigo dakin da gudu tana kiran Sunan Nadeeyah, Hijab ta mika mata tace "yi sauri kisa, kallon Hilal tayi tace "my PP, zo muje kaga wani abun al'ajabi, Maida wayarshi cikin aljihu yayi ya bi bayansu dan ganin abun da zata nuna mishi... Ga Nadeeyahn nan.... Daddy ya fadi yana murmushin jin dadi, Allah kadai yasan irin farin cikin da yake ciki, gani yakeyi kamar da ita kanta Suwaibar yake zaune, gefe Nadeeyah ta tsuguna tace "ina wuni, Hannu Papy ya bude mata alamar ta iso gareshi, kalle kalle ta shiga yi suka hada ido da Hafeez ya gyada mata kai yana murmushi, mikewa tayi ta isa gabanshi tana mai mamakin kamannin, tsugunawa tazo yi yayi saurin dagota ya rungumeta, kukan da yake kokarin boyewa yaki boyuwa saida ya zubda su, Damke Hannun Hilal dake yunkurin zuwa gurin Husnah tayi tace "Babanta ne fa, twins din Mama Suwaiba, cikin rashin fahimta yace "what, ba Baffa yace ya mutu ba, Baffa dake zaune ya jiyo Hilal yace "muma duk haka muka dauka Muntari, ashe yana nan da ranshi, kaddarar da ta boye mana shi ita ta sake hadamu dashi, kallon Nadeeyah da ta kasa sakin jiki har lokacin Baffa yayi yace "saki jikinki, wannan uwa yake a gurinki, haka uba, domin tare suka zo duniya da Mahaifiyarki, kallonshi tayi sosai dan ta gasgata maganarshi, tun daga hannayenshi har kafarshi saida ta kare musu kallon, kyawawan yatsun kafarshi da ya zamto irin na Mamma da nata shi ya tabbatar mata da maganar Baffa, wata irin runguma ta sake yi mishi tana kuka sosai a zuciyarta tana jero alhamdulillah, ta kusa minti uku a jikinshi tana tunano rayuwar da sukayi da Mamma, ji takeyi kamar dawo da ita Allah yayi cikin wata suffar, saukowa a jikin Mami Ruwaidah tayi ta kama hijab din Nadeeyah tace "let my Papy be, karki bata mishi kaya da hawayenki, Papy na baya son kuka, dagashi tayi ta fara shafa fuskar Ruwaidah hade da rungumeta, duk rashin son mutanen Ruwaidah ta kasa nuna shi ga Nadeeyah, sai ma ce mata da tayi, "ki daina kuka mana, na fada miki Papy baya son kuka, ko so kikeyi yasa Yaya Jamal ya daura ki a bayan *OBENIZA* Dariya Hafeez da Jamal suka saki dan sunsan ta da mugun tsoron obeniza,

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156