Chapter 18
Chapter 18
shige bayi, Husnah ta turnube fuska tace "wani Hafeez din, Anty Raudha tace "Hafeez din mama Suwaiba mana, kaff ta kwashe labarin abinda ya faru ta fadawa Husna suka karashe da dariya dukkaninsu, Badariyya tayi tsaki mai karfi tace "da an hadasu din, da zaifi mana alkhairi walhy, domin zuwansu nan din gaskiya akwai matsala, bama mai yiwuwa bane zamansu anan!! ta karasa fadi a gadarance, "Saboda kece mai gidan ko, Raliya da shigowarta kenan ta fadi tana harararta, Raudha tayi tsaki tace "nima zamansu anan din walhy bana sanshi, ni fa Allah ya sani na tsani talaka, ko sunan talauci banasan ji, Radiya daga bayi ta dago murya tace "ai talauci masifa ne, ni na rasa laifin me talaka yayiwa Allah, subhanallahi!!! Raliya tayi saurin cewa, ya salam, ku kuwa kuji tsoron Allah, talaucin nan fa wadanda suke cikinsa basu suka sawa kansu ba, kuma basu isa su cireshi ba sai Allah yaso, haka zalika arzikin da kuke ciki baku kuka bawa kanku ba, babu banbanci tsakaninmu, tunda duk abinda da talaka zaiyi mai kudi ma zaiyi, wadatar zuci tafi komai a rayuwa, suma Allah bai mance dasu ba, kuyi fatan kar Allah ya jarbceku da dandana rayuwar talauc----- "" eeeeeeh eeeh wait hang it, Radiya tayi saurin katseta, " har abada bazamu taba dandanawa ba "idiotic being, saboda muna sharhi kan talauci shine zaki rabashi jikinmu, to we reject it walhy, sakarai kawai,, uhmmm kawai Raliya tace ta fita tana mamakinsu, har ta kure dakin bata daina jiyo muryoyinsu ba.... Har karfe biyar na yamma Nadeeyah na zaune a inda take, da himilin kayansu, anan taci abincin da me aikinsu ta zubo mata, tana kallon dukkan ahalin mummy a cikin parlon ana hira, Anty Reemah ce kawai bata cikinsu, dan ita tun zuwansu suka wuce can gidansu ita dasu Hinad, ba yadda Hinad batayi tazo su tafi ba taki, kwanciyar hankalinta daya zainab ta bisu shiyasa ma zaman bai gundureta ba, gyangyadi ta farayi a zaune ta jiyo muryar Badariyya tana zuba rashin kunya tana fadin "wallahi mummy indai yarinyar can zata zauna a gidan nan ni bazan zauna ba, saidai ku zabi daya, janyota mummy tayi jikinta tace "haba baby, kiyi hakuri mana, dalili ne yasa zata zauna, kiyi hakuri pls na lokaci ne, kuma kinga makaranta zata koma, ba ganinta zaki dinga yi kullum ba, Keyn mota Raliya ta dauka a kan center table, ta dauki danta tace "Mummy sai anjimanku, tayi hanyar waje ba tare da ta jira amsarsu ba, badan a karkashin wani take ba, wallhy babu abinda zai hanata tafiya da Nadeeyah, mutuwa mai tonan asiri, duk talaucinsu basa zuwa gurinsu maula, rikon na Nadeeyah nawa yake? abinci ne fa kadai sai gurin kwanciya, sai dan kyautatawar yau da kullum, share kwallar idonta tayi ta shiga motar tana fadin, "ya Allah ka raya mu cikin ya'yanmu.... Dakyar mummy ta shawo kan Badar ta yarda, da sharadin a dakin mai aikinsu Nadeeyah zata zauna, dan ita sam bazata iya hada daki da Nadeeyah ba, dan a samu kwanciyar hankali mummy ta yarda amma can cikin ranta badan taso ba, Husna ma abin ya mata zafi sosai, Raudha da Radiya kuwa tsaff suka goyi bayan Badar... Dakin mai aikin nasu ma da d'an kyanshi, kayanta kawai ta shigar ciki ta fada bayi, sai da tayi kuka mai isarta sannan tayi wanka ta daura alwala ta fito... A inda ta idar da sallar ishaa bacci yayi gaba da ita, sai ajiyar zuciya take cikin baccinta, mai aikin nasu yar dattijuwa ce, taji tausayinta matuka, ta kuma yi tirr da hali irin nasu mummy, masu yin watsi da jininsu saboda talauci, tashinta tayi ta maida ita kan gado taja mata abun rufa...... Mrs Tijjani Shattima........! [07/03 6:31 AM] fareedah: ●ZUMUNCINMU A YAU● 1⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tsakurar abincin dake gabanta takeyi tana juya cokalin, ta rasa menene asalin abinda take ji cikin ranta, farin cikin sanin halin da Nadeeyah ke ciki na rashin iyayenta takeyi ko kuwa bakin cikin tarewar da kowa yayi a gidansu Nadeeyan, Mutuwar mamma na iskarta tayi murmushin farin ciki, tasan Nadeeyah na can cikin radadin da ta sanya ta, saidai takaicinta daya musaddiq sam baya yarda su hadu, duk wata kafa da zata sadasu ya tosheta, dan sam baya son jin ko muryarta, wani irin tsanarta yakeji a zuciyarshi na rashin imaninta, babu wanda bai ziyarci gidan mutuwar ba sai ita, kullum tana zaune a gida daga kallo sai cin abinci sai game, babu yadda mummy batayi ba akan tazo gidan mutuwar tun farkon yin ta, amma sam taki zuwa, gashi wata mutuwar ta sake bullo kai... Tura abincin gefe tayi ta mike ta wuce daki dan ta watsa ruwa, ita kadai ta kwana a gidan, sai daddy da taji tashin motarshi da asuba tasan shima a gidan ya kwana, ko gezau bata ji ba a zuciyarta bare ta karaya ta shirya zuwa gidan su Nadeeyan, ita sam bata san zafin mutuwa ba, a ganinta kuncin da Nadeeyah ta sanyata yafi zafi akan radadin mutuwa, tsaki taja hade da wurgi da kayan jikinta ta fada bayi...... *********** Bayan doguwar addu'ar da aka gabatar a kofar gidan malam Adamu na sadakar ukun mamma Suwaiba, sadakar abinci akayi sosai, duk wanda yake gurin saida ya wadatu da abinci saboda yawanshi, cikin kankanin lokaci jama'a suka watse ya rage saura makusanta kawai, Baffa da shock din mutuwar bai sakeshi ba har lokacin ya mike kamar ba laka a jikinshi ya shige cikin gidan, Saida ya zauna yana maida numfashi sannan ya dubi gurin da mummy da Goggo ke magana, fada mummy keyi akan rashin zuwan Badariyya, ita kuwa goggo goyon bayan Badariyya take hade da fadin "kinsan yarinya ce kuma bata san hayaniya, duk mu da muka zauna a gidan har kwana uku bamu wakilceta ba, Baffa dai kallonsu yakeyi zuciyarshi na tafasa amma bakinshi yayi nauyi ya gaza furta koda kalma daya ce, Hinad dake zaune can gefe kusa da Nadeeyah ya yafito da hannu alamar tazo, da sauri ta karaso gabanshi tace gani Baffa, cikin murya mai rauni yace, taje ta kira Hafeezu da Daddy a waje, sai a sannan mummy tasan da shigowarshi, karasowa tayi ta zauna kusa dashi tace "Baffa yaushe ka shigo, murmushin yake yayi yace "yanzun nan, tafi ki kirawo min dukkan ya'yanki akwai maganar da nake so muyi daku, kai ta gyada tace "to Baffa, ta mike ta fita tsakar gidan, Zama Goggo tayi tana matsa mishi hannu hade da cewa duk kwana ukun nan baka da wani kuzari, mutuwar nan fa ba a kanta aka fara yi maka ba, ka rasa uwa, uba, mata, da ya'ya, saidai wannan mutuwar na lura tafi razana ka, wanda ni bansan dalili ba, mutuwa daya ce, in mutum yayi ta baya dawowa, inda ana dawowa sai ince ka cigaba da damuwar, watakil damuwar taka na iya dawo da ita, ya kamata ka sanya wa kanka nutsuwa kayi tawakkali, Hawayen da ya zubo a gefen idonshi ya share zuciyarshi na rawa yace "Asama'u! duk mutuwar da akemin ta Suwaiba tafi tsaya min, kinfi kowa sanin hal---- da sauri ya dauke idonshi cikin nata, ya kauda kanshi ya canza maganar da cewa "ina matukar tausayin halin da yaran nan zasu shiga ne,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156