Chapter 21
Chapter 21
suna ta maganganu cikin fushin rashin ganinta, muryar shaho ya jiyo daga can yana fadin "babu abinda zai hanashi kasheta in ya ganta, da yaso ya sameta yayi yadda yake so da ita amma yanzu kasheta zaiyi dan in ya barta zata iya zama barazana ga rayuwarshi, jin haka yasa Baffa cikin tashin hankali yayi saurin komawa cikin gidan, A kofar sakarkari ya samu ma'u zaune tana damun fura da nono, ganin da tayi ya shigo a firgice yasa ta mikewa ta nufo shi, "lafiya?, ta tambaya tana kallon yadda jikinshi yake rawa, daki ya jata yace "ina bakuwar balarabiyar nan, maza fito da ita mu nemi wani gurin mu korata dan walhy rayuwarmu tana cikin hatsari, ya kwashe duk abin da yaji shaho ya fadi ya gaya mata, cikin dakiya irin tata da jarumta tace babu inda zaka kaita in ba iyayenta ne suka zo neman ta ba, ya zama dole a samu me tsawatarwa shaho, abubuwan da yakeyi a cikin garin nan ya isa haka, kallonta yayi galala yace "wa kike ganin zai tsawatar mishi?, ki fada min wake da wannan zarrar? kwaryar damunta ta dauko tace "nidai na fada maka babu inda zata, ta wuce daki tana tsuma tana fadin babu wanda ya isa ya taba makka, "sunan da ta rada mata kenan tun kafin taji sunanta, ita zuciyarta ta tafi can tunanin in iyayenta suka zo to fa zasu musu alherin ganin sun taimaki yarsu, kuma zata kafa tarihin ita ta fara taba jikin balarabiya a duk fadin tsirarun musulman da suka musulunta a kauyen, cire kayan tayi ta dago yayin ta fito da ita tace "sannu hai yar budurwa, fito muje ki sha fura sai kiyi wanka, raba dara daran idanuwanta ta fara yi dan ko kalma daya bata dauka cikin kalaman ma'u ba, hannunta ta riko suka fito waje ta shimfida mata sabuwar tabarma ta nuna mata tace "zauna, bata fahimta ba haka ta kuma kama hannunta ta zaunar da ita, furar ta mika mata ta dauka ta fara sha hawaye na zirarowa daga cikin idanuwanta, tunanin kaninta takeyi dan shekara 6 a duniya wanda ta zamo gata a gareshi gaba da baya, ko a wani hali yake yanzu Allah masani, ludayi uku tayi ta miko ma ma'u.. Amsar kwaryar tayi tana fadin "hai har kin koshi, da kin kara kadan ta fadi tana miko mata, Girgiza kai tayi saboda ta fahimci nufinta tace "Alhamdillah, Jazakumullah khairan" yashe hakori Ma'u tayi tana dariya har can cikinta tana kyakyato shi, dariyar murnan jin yaren larabci, da kuma ganin ita kanta balarabiyar makkan a gidanta takeyi, saida ta gama dariyarta tace "hai Baffan Boddo an je gidan kawu suwidi in fadowa su inna wuro munyi bakuwa mai tsarki yar Makkah, takalmin robarta ta janyo me ruwan bula tasa a kafarta, ta yayo dankwalin saka ta rufe kanta ta fara tafiya, ta kusa taba kofar Baffa yayi saurin tareta yace "A wala hakkilo na" ("baki da hankali ne?) Kinsan irin halin da zaki samu a ciki in kika gayyato mana mutanen gidan Kawu Suwidi?, kince bazata bar gidan nan ba na hakura ta zauna amma ki sani babu me shigo min gida bare ya ganta ya jaza min masifa, tana nan zaune nasan za'a zo cigiyarta a lokacin sai in mikata gurin iyayenta,, kalonshi ma'u tayi fuskar nan cike da gamsuwa tayi kamar ta yarda din da gaske, yaye dankwalin kanta tayi tace "Haka ne, na manta ne ina ta zumudin kai rahoto dan kawai in burge su inna wuro, yanzu bari inje in sata tayi wanka sai ta canza kaya a wanke na jikinta, gyada kai Baffa yayi cikin jin dadi ya koma daki kusa da yaranshi ya zauna yana shafa kan karamar dake kokarin tashi.. Murdaddiyar sarkar murjanin gwal din da ta cire kafin ta shiga wanka ma'u tayi ta juyawa a hannunta tana dariyar farin ciki, "Aiya Ya Allahn Hard'ejo, (sunan yayan mijinta kenan malamin da ya fara kawo musu musulunci kauyen), ji wani "kuje ndade' (sarka) kamar ba hannun mutum bane ya kerashi, sashi tayi a wuyanta tace "wannan ko matar Ardo Laminu bata da irinshi, kaii ya zame min dole in je gidan su inna wuro dan bazan bar wannan daddadan labari ya wuce ban basu shi ba, ai ni ko da wannan maka wuyar aka barni na tsira, daki tayi da sauri tana magana kamar zararra, kayanta dake cikin wani akwatin katako ta dauko sababbi na fulani tace " Baffa zan bata wannan kayan nawa tasa saboda a wanke wadancan, gyada mata kai kawai yayi dan mamakinta bai barshi ya bude baki yayi magana ba, ma'u da ko dankwalinta bata iya bawa wani aro shine har ta dauko kayanta da bata taba sasu ba zata bawa wata tasa, lallai yar makkah ta ciri tuta.. Sosai kayan fulanin suka mata kyau a jiki saboda tsabar kyawunta, lallausan gashinta ma'u ta shiga kitsashi da kyar tana yi yana warwarewa, haka dai tayi mata irin nasu na fulani ta dauko mata su sarka da abun hannu duk dan ta mantar da ita sarkar gwal dinta... Mrs Tijjani Shattima... [07/03 6:31 AM] fareedah: •• ZUMUNCINMU A YAU •• 2⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Hanyar sama Badariyya tayi da gudu tana shashshekar kuka kamar ranta zai fita, kofar dakin Daddy ta shiga bugawa kamar zata ballata, da gudu mummy ta fito daga bayi jiki na rawa ta bude kofar, Daddy kuwa zaune yayi yana jiran ganin me mishi irin wannan bugun kofar da safiyyar nan, jikin mummy Badar ta fado ta sake kecewa da wani kukan, waigawa tayi ta kalli Daddy da ya rike kanshi yana tsaki, waje ta jata ta rufo mishi kofar, ta kama hannunta sukayi dakin ta, zaunar da ita tayi a kan gado ta shiga rarrashinta, saida ta tabbatar ta fara samun nutusuwa sannan ta tambayeta abinda ya faru, karya ta shiga rerowa mummy cikin wani sabon kukan, "Ya Hilal ne yayi min dukan tsiya, wai saboda Nadeeyah taje tana wanke wanke kunama ta harbeta, shine yaje ya taso ni ina bacci wai tace mishi ni nasa ta, kuma tace mishi wai na hana a bata abinci jiya har tayi bacci, sannan a gabana Ya Musaddiq ya dauketa ya sata a mota suka kaita asibiti wai kafin su dawo in tabbatar na gama wanke wanken da ya rage------- , Wani irin kunci da tukuki mummy taji a ranta, "Hilal din ne ya dake ki? gyada kai Badar tayi wasu zafafan hawaye na sake bin kuncin ta, 'irin kallon da Musaddiq ke ma Nadeeyah shi ya fi komai taba zuciyarta, kwanciya tayi jikin mummy ta runtse idanuwanta saboda ganin hanun Musaddiq da takeyi cikin na Nadeeyah, "Hello Reemah, daga daya bangaren Anty Reemah ta bude idonta hankali tashe cikin muryar bacci tace "Na'am, ina kwana Mummy, ''lfy kadai mummý tace, ta cigaba, "kizo gida yanzu ina nemanki, bata jira amsarta ba ta kashe wayar.. Mikewa Anty Reemah tayi jiki a sanyaye, tasan akan matsalar Hilal akayi kiranta da safen nan, cikin zafi tace "wai wannan wani irin yaro ne da yakeson kashe ni tun lokaci na baiyi ba, wallhy yau, ko gobe zamu bar kasar nan kar ya jaza min bala'i, ina kokarin gamawa da mahaifiyata lafiya yana neman janyo min tsinuwa, Papa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156