Skip to content

Chapter 134

Chapter 134

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

da yaron, Cike da azama Musaddiq ya taro yaron da har lokacin bai farka daga baccin da yakeyi ba, rawa jikin saurayin ya fara yi cike da tsoro dan da yaron ya faďi ba karamin buguwa zaiyi ba, waya ma kenan da take bata da karfi ta tarwatse inaga rai, Kallon Musaddiq yayi wanda ya zubawa yaron ido suna kallon juna dan yana zuwa hannun Musaddiq ya buďe idonshi tangaran, dariya jinjirin yayi wa Musaddiq wanda ya sanya duka kumatunshi lotsawa, cike da kasala Musaddiq ya maida mishi dariyar haďe da taba kumatunshi, haka nan yaji son yaron na yawo cikin jininshi, matsowa saurayin yayi yana ma Musaddiq godiya haďe da sa hannu ya karbi jinjirin, kuka sosai jinjirin ya fashe dashi wanda a iya saninsu bai taba yin irinshi ba tun haihuwarshi, a ruďe saurayin ya fara jijjigashi yana hangen wani guri alamar neman mahaifiyar yaron, kuka sosai jinjirin yakeyi har yana shakewa, hawaye shabe shabe a rufaffen idonshi, har cikin rai Musaddiq ke jin kukan jinjirin, ganin yadda saurayin ke jijjigashi cikin rashin iyawa yasashi matsowa kusa ya mika hannu ya karbeshi, sanyashi yayi a kafaďa nan take gurin yayi tsitt sai alamar shakuwa da ajiyar zuciyar jinjirin, cike da mamaki dan saurayin yace "Lallai junior, wato nayi maka yaro da raino ko? Dariya Musaddiq yayi yace "Abun mamaki, ban sanshi ba amma ganin farko ya shiga raina, ya sunanshi? *Mukhtar amma Hi*------- "Amaaan.. da sauri ya katse maganar ya amshi junior yace "Sorry.. uncle dina na kirana, inaga zamu wuce ne, thanks alot, bin bayansu Musaddiq yayi dan keyn motarshi ya makale jikin showel din, tsayawa Aman yayi cike da mamaki yace "Any problem? Nuna mishi keyn yayi lokacin ya cireshi haďe da jan kumatun junior, "Bye Daddy, ka daina rigima kaji ko? yadda ya kaďa mishi keyn yasanya yaron sake yin dariyar da ta tsaya a ran Musaddiq, saida suka kurewa ganinshi sannan ne yayi ajiyar zuciya haďe da kokarin cire tunanin yaron a cikin zuciyarshi... Faďuwar da gabanshi yayi ne ya sanyashi faďin "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun... kamar an sake hura faďuwar gaban domin kuwa da sauri da sauri take harbawa kamar ana lugude, runtse idonshi yayi haďe da dafe kirjinshi, tunanin da yake kwana yi shi ya dawo mishi sabo fil kamar yau aka halitta shi a cikin zuciyarshi, Karar wucewar takalma ta bayanshi ya sanyashi buďe idon a hankali, kafin ya juyar da fuskarshi duk sun bi ta kofar sun shige sai Aman da shima ya bi bayansu, kamshin turarukansu da ya biye gurin shi ya sanya Musaddiq sake jingina da kujerar yana mai tsintar kanshi cikin shaukin da ya daďe bai shiga irinshi ba.... Saida jirgin yakai 45mins sannan ya sauka a wani kebabben guri saboda dama private ne, A gajiye likiss suka sauko kowa yana mika saboda zaman guri daya, Anty Reemah Musaddiq ya fara gani yayi saurin karasawa kusa da ita yana mata sannu da zuwa, Sakkowar Sheik ba karamin gigita Musaddiq tayi ba, bai dawo daga wannan shock din ba ya shiga wacce ta fishi, Maleekah ya hango kanta dauke da hular Hilal wacce ta cire suna gab da fitowa, "Kaga Nadeeyarka ko? Kunci ya kare, Papa ya faďi yana murmushi... Hmmm ya faďi cike da mamaki, "Mai kama da ita dai, Nadeeyah ba haka take ba, amma a ina kuka samo mai kama da ita, in ma kunyi haka ne dan hankalina ya kwanta in sake wani auren to ku sani ni da aure sai dai a lahira, yadda Nadeeyah ta gama aure ta tafi ta barni nima hakan zan je in sameta yadda ta barni.. Hannun Papa Anty Reemah ta kama haďe da girgiza mishi kai suka tsaya a gefe, cike da murna Hilal ya sauko ya rungume Musaddiq haďe da tambayarshi bayan rabuwa, Murmushin da dole uwar naki ta koya mishi shi ya sakar mishi haďe da tambayarshi su waye wadannan masu kama da su Mamma? "Hello broo, Ayyam Atika Ateek, a.k.a Maleekah, tsaki Hilal yayi haďe da cire hular kanta yayi gaba, "Salamu alaikum, nyc meeting u Atika, i am Musaddiq Kyari, Maida hannunta baya tayi dan yadda ya amsa mata sallamar ya burgeta, har kasa ya tsuguna ya gaida su Sheik, dagoshi Sheik yayi ya rungumeshi haďe da amsa gaisuwar, saida suka gaisa sosai sannan suka fita suka isa motar Musaddiq da wata da aka basu a airport din dan zurga zurga, har suka isa gida Musaddiq bai bar tambayarsu daga ina suka nemo dangin Mama suwaiba ba.... Cike da al'ajabi Daddy ya ke duban Sheik, "Ikon Allah kenan, to meyasa babu wanda ya nemeta? Murmushi sheik yayi yace "Kaddarar Zuri'a, a lokacin da labarin yazo mana ina da shekara shida a duniya, amma nakan tuna wasu abubuwan, Lokacin da labarin mutuwarta ya riski ummul bata tsaya tayi binciken komai ba, kamar jira takeyi ta tattara 'yayanta suka fita daga gidan da niyyar in ta koma tace harda ni aka kashe, wani yaron da muke wasa dashi *Husaimin* shi ya shigo ya tasheni yace "inyi sauri gashi can za'a gudu a barni, a lokacin ne yake faďa min cewa an kashe Habeebullah da yayata, da gudu nabi bayansu lokacin har sun hau amalanke sun fara tafiya, takalmina da ya cire na waiga zan dauko Husaimin yajani da tayar hannunshi mukayi gudu muka kamo su, dakyar na iya hawa saboda tsayin abun, ina hawa ummul ta fara yi min masifar borin kunya tana tambayata inda naje, ban bata amsa ba na tsugunar da kaina inata kukan rashin gatan da zan tarar, har muka isa inda zamu tsallaka ruwa ban daina kuka ba, muna zuwa muka samu wadanda zasu tsallaka zuwa Egypt, nan aka loda mu ciki muka fara tafiyar da ta kaimu washe gari cikin ruwa... Karya da gaskiya Ummul ta fadawa mahaifina har ta ce mishi an sallaceta a gabanta domin tasan bazai yarda da ita ba sai yasa an je an dubo ta, saboda tsabar bakin cikin rashin Atika mahaifina ya kamu da mummunan ciwon stroke wanda ya daukeshi shekara biyu yana yi kafin Allah ya dauki ranshi, gaba daya dukiyarshi ummul ta tattareta ita da yayanta ta maidani dan aikinsu, son zuciya yasa ta manta matsayina a gurinta, ta mance cewa inda mahaifiyarmu ta tafi itama zata je komi daren dadewa, gidan Sheik Al' Mannar abokin babana nan nake zuwa daukar karatu, ganin hazakata yasashi ya sanya ni a makarantar boko, daga can sai in wuce gurin da suke aikin gini in dinga koya ina samun na abinci, gaba daya kwanan gidanmu ya gagareni domin kwana nakeyi aiki bani da wani hutu, abinci ma ummul sai taga dama take bani a cewarta itama ba kudi gareta ba, duk wasu kadarori na mahaifinmu ta haďe ta siyar sun cinye kudin da 'yayanta... Muna da shekara sha takwass 'yaranta biyu sukayi wa wata yarinya fyaďe wanda hakan yayi sanadiyyar yi musu hukuncin da yayi ajalinsu, a lokacin ummul hauka ne kawai batayi ba domin saida tayi wata biyu a asibiti, ni nayi jinyarta saboda dayan yaronta an nemeshi an rasa ya gudu da ragowar kudin da ta ajiye, ashe shima smuggling din kwaya yakeyi, ranar da dubunshi ta cika aka kamashi ita ma a ranar rayuwarta tazo karshe saboda shock din fille mishi

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156