Chapter 36
Chapter 36
gudu ta barsu a waje da Bingel da tayi tsaye tana kallonshi kamar mutum mutumi, Hannu yasa yayi kasss a fuskarta yace "ina wuni yar uwarmu, firgigit tayi tace "ni ya kamata in fara gaisar dakai, murmushi yayi yace "kuma sai kika barta ta gudu baki rike ta ba, dariya tayi tace "kasan yarinya ce, kunya gareta, amma bari in tayata tadin, cikin nutsuwa ta dinga tambayarshi halayarshi da abubuwan daya kamata ta sani, sun dade suna hira yana fada mata yadda yake ji a cikin rashi game da kanwarta, da zai tafi ya bukaci ta kira mishi ita su yi sallama, sallama tayi mishi ta wuce gida ta iske suwaiba a zaure tace "jeki kiyi sallama dashi, ko so kikeyi yayi fushi, dakyar ta fito ta tsaya nesa dashi tace "ina wuni, jingina yayi jikin stalet dinshi yace "bazan amsa ba, ashe ma dai ni dodo ne ban sani ba, rufe fuskarta ta sakeyi tace a'a kayi hakuri, murmushi yayi yace to nayi, ya bude gaban motar ya dauko leda yace "gashi inji mamanki tace wai a kawo wa yarta, dakyar ta karbi ledar ta ruga cikin gida da gudu, murmushin shaukin samun farar mace kamila yayi sannan ya shiga mota ya tada ya wuce.... Bayan zuwan magabatan Mukhtar aka saka ranar aure sati biyu, babu irin hidimar da baya ma Baffa saboda so da kaunar da yake yi ma suwaiba, ita kuwa Bingel ramewa ta soma yi saboda tunanin mukhtar da ta sanya kanta ciki, bangaren Ma'u kuma sai hada tuggunta takeyi wanda zai hana auren, gori kuwa babu wanda bata sha daga makota, da abun ya isheta ta zauna wani dare ta dinga rusar kuka, Halima da itama kishin suwaiba ya dameta ta zauna tana tayata kukan, a haka suwaiba da ta dawo gurin mukhtar ta samesu, kudin da ya bata ta fito dashi ta mikawa Ma'u tace "Goggo gashi yace in kawo miki kudin walima, amsa tayi ta ajiye a gefe, cike da fargaba tace "Goggo me ya sameki, rungumar munafurci Ma'u tayi mata tace "Suwaiba ya zanyi da raina, ya zanyi da gorin mutane, yanzu kina karamar kanwar yayarki ace kinyi aure ita bata yi ba, kinsan dole abun ya dameni, dole ne in shiga cikin kunci da takaici saboda nasan babu wanda zai aureta yanzu, matso da ita ta kuma yi tace "kinsan dai ni na haifeku dukkanku ko? Gyada kai Suwaiba tayi tace "eh, to yar albarka ina umurtarki da ki janye auren nan akanki ki barwa yayarki, nasan Allah zai dubi abin alherin da kikayi ya baki wanda ya fishi, jiki na rawa suwaiba tace "Goggo, dan Allah kiyi hakuri, wallahi ina sonshi, kuma shim--- ya isheni, yanzu duk halaccin da Bingel tayi miki tun kina yarinya har kawo yanzu baki gani ba, duk irin kaunar da ta nuna miki bazaki dubashi ki sadaukar mata da mijin da zaki aura ba, kuka ne ya kufcewa suwaiba tace "hakkinta ne Goggo, Hakkinta ne a matsayinta na yayata ta kula dani kuma ta sadaukar da komai nata a gareni, wallahi da zan iya da na rabu dashi na bar mata shi amma bazan iya---- wani wawan mari Ma'u ta kai mata, tace "lallai rashin kunyarki ta tumbatsa, a gabana kike cewa kina son namiji, lallai ďan da baka haifa ba dole ya nuna shi ba naka bane, dammmmm.... suwaiba taji a kirjinta, kalaman Goggo suka sa zuciyarta ta fara yawo a cikin ma'ajiyinta........ Mrs Tijjani Shattima [05/03 11:10 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* 2⃣9⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* *_Duniya kurkukun mu'imuni, kuma Aljannar kafiri, akwai mutanen da Allah swt yake Halittarsu a cikin duniyar nan ba domin suji dadi ba, sai dai domin rayuwakansu su zamto izina ga wadanda sukazo domin zamanta na din din, mai hankali shi kadai yasan duniya ba gurin jin dadi bane, lahira itace matabbata, sannan akwai tarin tanadi da Allah yayi wa bayinshi masu hakuri, tanadin Allah shine tanadi Allah ya sa mu dace,_* *RABUWA DA MASOYI* Mikewa tayi ta isa gabanta tace "Goggo, dan Allah karki ce bake kika haifeni ba, Kukan Munafurci Ma'u ta saki tace "Suwaiba yau kin sani na fada miki abinda ban taba tunanin fadin shi ba, yau kin kaini makura har na fito miki da *SIRRIN BOYE* kuka ne ya kufce ma Suwaiba tace "wacece mahaifiyata? , a ina take?, nan take shaukin son taga mahaifiyarta yazo cikin zuciyarta, rungemeta Ma'u tayi sosai tace "Tambayar bata da amfani tunda bata raye, ni nan ni na raine ki tun kina jarinta da taimakon yayarki, munsha gwargwarmayar rayuwa gurin baki tarbiyya, musamman yayar taki da kike yunkurin k'in sadaukar mata da soyayyarki, cikin kuka suwaiba tace "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kara kankameta Ma'u tayi tace "duk abin da kika ga na miki a baya bawai dan bana sanki bane, nayi shi ne dan samar miki tarbiyya mai kyau da amfani, kiyi hakuri, kiyi hakuri ki bar mata, "labarin karya ta shirya mata akan mahaifiyarta sannan ta karashe da fadin irin kular da zainab din tayi mata, kukan bai fasa zubowa a idonta ba tace "Allah ya jikan mahaifiyata Goggo, Ameen Ma'u ta fadi sannan tace "nasan zaki bar ma yar uwarki mijin da zaki aura ko? Nasan zuciyar zinari gareki, girgiza kai Suwaiba tayi tace a'a Goggo, yaudara ce wannan, bazan iya hakuri da shi ba, domin kuwa Allah sai ya tambayeni, yasa rai da aurena kuma kawai sai in ce mishi ya auri yayata, hakan bazai yiwu ba, tana karashe fadi hade da tashi ta fita zuciyarta na tariyo mata irin ukubar da tasha a hannun Goggo, ba tun yau take tunanin cewa ba Goggo bace ta haifeta, gashi yau sanadiyyar Mukhtar an warware mata komai, hawayen idonta ta share dan tasan in shaa Allahu ta kusa daina zubda su, tasan Mukhtar zai zame mata komai da ta rasa a rayuwa.. Dakinsu ta shiga jiki a sanyaye, a zaune ta tarar da zainab da ta gama sauraron duk abinda suke cewa, tafarfasa zuciyarta takeyi saboda yadda ta dauka Suwaiba zata iya barin mata komai take bukata a rayuwa, lallai a yanzu ne ta fahimci cewa uwa daya ya wuce wasa, tayi imanin da Leemah ce zata yarda ta barta Mukhtar dan kar ta kunyata, wata irin tsanar Suwaiba ce ta darsu a zuciyar zainab wacce dama ta dade ana mata aikenta, sai yanzu shaidan ya samar mata mazauni a zuciyarta, barka da hutawa yaya, suwaiba ta fadi tana cire hijab dinta, uhmmm!! kawai taji tace sannan ta mike kafarta a kan gado, gabanta ne ya fadi dan bata saba ganin hakan a gurin yar uwarta ba, gefen gadon taje ta tsuguna tace "yaya ko na miki wani abu ne, juya mata baya tayi tace "karki dameni suwaiba, kaina ke ciwo, nan take idonta ya ciko da kwalla ta mike ta fita kofar dakin, kuka sosai ta zauna tana yi, zuciyarta sai kai kawo takeyi akan maganar da Goggo tayi mata, sam bata damu da sanin cewa ba ita ta haifeta ba, dan ta dade da sanin uwar da ta haifeka baza tayi maka irin wannan tsanar ba, abin kawai da ya daga hankalinta shine rashin sanin uwarta da kuma rashin adduar da bata samu daga gareta a matsayin sadaka a kabarinta..
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156