Chapter 89
Chapter 89
ta share hawayenta ta fara shafa mishi kai, Hinad ce ta shigo dakin ido jajur hannunta da plate din farfesun kifi ta tsuguna a gabanshi tace "yaya ka tashi kaga nayi maka abun da kakeso, "harda zobo mai dadi, Zainab ta fadi itama har lokacin bata bar kukan ba, runtse idonshi yayi hawayen dake kwance ciki suka jika gashin idon, Cikin muryar Kuka Hinad tace "Yaaayaaa plss ka daina kuka dan Allah, ka fada mana abun dake damunka, Muryar Papa sukaji da karfi yana kiran Anty Reemah, amsawa tayi tace tana zuwa, "ki ce mishi ya fito mu tafi Masallaci, tadashi Anty Reemah tayi tace "Tashi kuje kuyi Sallah kaji, in ka dawo sai ka fadamin damuwarka koma meye in shaa Allahu zanyi maka maganinta.... A tare suke jerowa kai kace wa da kani ne, har Hilal ya dan dara Papa tsaho, bai tambayeshi abun dake damunshi ba dan baisan ji saboda kar nashi hankakin ya tashi, nasihohi ya dinga mishi akan yadda rayuwa take "dama dole a duniya mutum bazai samu abinda yake so daidai ba, dole yau zuma gobe madaci, Ganin hawaye a idonka ya fara tabbatar min da yanzu ka fara sanin me duniya take ciki Hilal, wacece ita?? Wani irin kallo yayi ma Papa ya dauke kanshi dan baisan sake zubda wani hawayen, lallai mahaifi daban yake, yasan abun da zai raunata Hilal har haka bai taba wuce soyayya, "Papa mu bar maganar, she is dead, "subhanallah Papa ya fadi cikin tausayawa, hannun Hilal ya rike cike da rarrashi ya shiga bashi hakuri dan tsaff ya yarda ta mutun ne... Dakyar Hilal ya ci wani abu sannan ya tashi ya wuce daki, da ido iyayenshi suka bishi suna tausaya mishi dan sunsan mecece soyayya, basu san tashi har gara ace mutuwar tayi da abun dake shirin rabasu ba, Five missed calls ya samu a wayarshi na Musaddiq, yana kokarin kira Musaddiq din ya sake kiranshi, bai bari yayi magana yace "ka fada mata? Gyaran murya Hilal yayi yace "karka damu, Nadeeyah is all urs in shaa Allah, godiya ya shiga yi mishi wanda ya sanya Hilal ajiye wayar a kan gado, wani irin tagumi ya zuba zuciyarshi na kukan rashin abin da ta dade tana dakon so, yafi awa biyu zaune a haka... Da wuri ta gama komai ta ciro wayarta a charge ta kwanta tana game, bini bini ta duba lokaci, ta kosa taji wani irin sakone wannan da har yake da lokacin badashi, ganin da tayi goma ta gifta harda minti goma yasata fara rubuta mishi sako, kafin tagama taji karar shigowar sako, da sauri ta goge ta bude sakon... *A rayuwa kowa yana tafe da kaddararsa, duk wanda Allah ya rubuta kaddararka ta zama tare dashi ne, to baka da dabara sai ka zauna dashi, naso kiyi zurfin karatu ta yadda zaki kere wasu matan kema a sanyaki cikin jerin masu ilimi sannan kiyi aure... amma hakan bazai yiwu ba saboda kaddararki batazo a haka ba, _I love Nadeeyah_ .... wannan itace kalmar da dan uwana yace in isar miki, Musaddiq na matukar kaunarki Nadeeyah, da fatan zaki amshi soyayyarshi, domin kun dace matuka, kuma nasan bazai barki ki zubda da hawaye ba, Allah ya barku tare kanwata take care.....* Tana kaiwa karshe taji wani irin jirin da Allah ya taimaketa a zaune take, dan ta fadi, Ya Musaddiq ke sonta, "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, ya zama dole gobe tayi shirin tafiya Gombe kuma ta zauna a can, ina zata iya da bala'in Badar, su Anty Raudha, uwa uba Mummy da ta dau burin duniya tasa a kan shi, inaaa samm bazama ta taba nuna taga text dinnan ba, da sauri ta kashe wayarta ta dukunkune cikin bargo.... *MAFARKI* _Hannu tasa ta cire akan farar fuskarshi da ta koma jaaa saboda kukan da yaci, "rau rau idonta yayi murya ta fara rawa tace "Yaa Hilal, me ya sameka, wanene? Hannunta kawai ya rike dan kukan yaci karfinshi ya kasa magana, hawayen dake makale cikin idonta ya fara zuba kamar fanfo, a shagwabe tace "Dan Allah ka fada min, menene? Zaiyi magana kenan ya hango wani farin haske dan karami ya doso inda suke, hannun Nadeeyah ya rike yana janta yana fadin ta kyaleshi tazo su tafi, mikewa tayi duk da kankantar haske haka ya rinjayeta ta dinga binshi tana waigen Hilal da ya sunkuyar da kanshi kasa sautin kukanshi ne kadai ke tashi a gurin.... A firgice ta tashi zufaa duk ta jikata, janyo wayarta tayi da sauri ta kunnata, bata bari ta gama settling ba ta latsa number Hilal, lokacin karfe 1 a nigeria, tasan dakyar yanzu in bai yi bacci ba, saida ta kira sau uku bai daga ba, kwanciya tayi taji duk babu dadi dan so takeyi taji ko lafiyarshi kalau, yana idar da Sallah ya bi bayan kiran da tayi mishi, hannu na rawa ta dauka tace "ina wuni? "Kwana dai Nadeeyah ya fadi murya a dashe, "umm haka ne, ba kayi bacci ba? dama bacci ne ya daukeni kuma bani da charge shiyasa na kiraka saboda tunin sakon.. "yasani sarai ta gani, danne zuciyarshi yayi yace "mantawa nayi kanwata kuma surukata, bari in fada miki da baki amaryar Small uncle, yadda ya fadi murya na rawa ya sanyata kashe wayar da sauri, dana sani ta dinga yi dan yanzu ya tabbatar mata a kunnenta, Allah ya sani bata kin Musaddiq amma koda wasa bazata taba iya aurenshi ba, komawa tayi ta kwanta tunane tunane marasa dadi suka dinga zuwan mata har wani baccin ya dauketa.... A parlor ta zauna da asuba tana jiran ganin Daddy ya dawo daga Salla, ga mamakinta tare suka shigo da Musaddiq, dama ita ke tashinshi Sallar asuba to yau taki zuwa, tasan Daddy ne ya tasheshi, Har kasa ta tsuguna ta gaida Daddy, amsawa yayi hade da cewa baki koma bacci ba, "gyada kai tayi tace "eh Daddy dama ina son in tambayeka ne, cikin palon ya shiga ya zauna yace "zo zauna inji, kusa dashi taje ta durkusa tace "Daddy mun gama jarabawa, dan Allah ina son inje Gombe, tare zamu tafi da Husna, fadada Murmushinshi yayi yace "jiya muka gama magana da mamanku, ku shirya jibi Malam Ali zai kaiku, godiya sosai tayi mishi ta mike ta shiga kitchen, shima sama ya wuce dan bacci zai koma saboda lahadi ce babu aiki.. Saida yaji Daddy ya rufe kofar dakinshi sannan yayi saurin zuwa kitchen din, tsaye ya sameta a kofar shiga kitchen din tana jiran su shiga daki itama ta fito ta shige daki, Tana ganinshi tayi saurin juyawa zata koma ciki, shan gabanta yayi da sauri tsayinshi yayi mata rumfa babu abin da take gani a gabanta sai shi, jan hijab dinta tayi ta rufe bakinta tace "zanyi aiki ne, "nima shi zanyi ya fadi yana kwaikwayonta.. Gefenshi tabi zata wuce taga yasa hannu ya tare gurin, marairaicewa tayi tace "dan Allah ka matsa, ko baka san Daddy ya karya da wuri? nade hannuwanshi yayi yana murmushi yace "sai kin yarda muyi tare, gyada mishi kai tayi alamar amincewa, yauwa ya fadi hade da jan hannun jallabiyar shi, dankali ta debo ta dauko abin ferewa guda 2 ta mika mishi daya, karba yayi yana dariya yace "Allah sa dai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156