Skip to content

Chapter 53

Chapter 53

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

muyi, bata motsa daga inda take ba tana tsaye har seconds sittin, Murmushi yayi ya kara takowa yazo har inda take, kamar me rada yace "matsayinki ya kai in biyoki inda kike, kamar zatayi kuka ta juyo tace "um um dan Allah uncle kayi hakuri, zan dauko dankwali na ne, "Ya riga ya gama fahimtar yanayinta na tsoro yayi murmushi mai kashe zuciya yace "naki wayan, hular kanshi ya cire ya mika mata yace "ki rufe kanki dashi, saurin maida hannunta baya tayi tace "Dan All-- "karki hada ni da Allah, yayi saurin katse ta a kasalance, hannu yasa ya dago habarta ya sanya idanuwanshi cikin nata, kokarin sauke idonta tayi jiki na rawa, yayi girgiza mata kai alamar a'a, karkatar da kanshi gefe yayi, gaba daya soyayyarta tana neman maidashi zautacce, ya mance matsayin malami yake a gareta, suffofinshi na shagwababben Momma suka bayyana, a hankali yace "plssss!!! bata bari yayi magana ba tayi saurin runtse idonta hade girgiza kai, bata taba shiga yanayin da yake kokarin sanya ta a ciki ba, rufe idonshi yayi shima yace "karki hana ni plss, akwai abun da ya ke kokarin karya duk wani lago nawa, *Soyayya* ita gayyaceni zuwa gareki ba tare da shirya ma zuwanta ba, tell me,!! kina son in barta ta sanya ni na rankwafa, bani da wani sauran sukuni tun ranar da na fara ganinki, kiyi min agaji, ki tausaya min, ki tallafe ni, ki amince dani a cikin zuciyarki, sonki ya gama shiga cikin jinin jikina, Shuru ne ya dan ratsa gurin na minti daya, bugun zuciyoyinsu kadai suke jiyowa sai numfashinsu dake gauraya da juna, A hankali ta bude idonta wanda ya zamo kamar hadin baki shima ya bude nashi, da sauri ta dauke kanta hade da rugawa ciki da gudu, saida ta isa daki sannan ta fara maida numfashi.. jin karar ruwa a bayi ne ya bata tabbacin Husnah na ciki tana wanke jikin ta har lokacin, a gefen gado ta zauna ta runtse idonta, ta kasa fassara yanayin da take ciki, wani abu ne yake ta mata yawo a cikin kwanyarta.. karar wayar Husna ta ji tayi saurin mikewa ta dauko ta a gaban madubi, sunan da ta gani ne ya sanyata dauka, tun kafin tayi magana yace "kina lafiya, bata amsa ba tace "ina wuni Ya Hilal ba ita ce, "i knw ya fadi yana dada jinjinawa zuciyarshi da take saurin daukar haske akan kusancinta da Nadeeyah, tana dauka jikinshi ya bashi ita ce, "ya school, hope kina kokari ko,? cikin nutsuwa tace "umm ina yi, lumshe ido yayi ya bude yana kallon kasan office din da yakewa aikin zane yace "Good, babu ruwanki da kowa kamar yadda nake fada miki kullum, karatunki shine gatanki, bana san wani abu ya shiga rayuwarki yanzu, i want u to be successful kin gane ko, gyada kai tayi kamar tana gabanshi tace "in shaa Allah, in yana waya da ita ya kan manta duk wata zuciyarshi da bata san raini, yakan manta ko shi waye duk da har yanzu bai taba nuna mata alamar soyayya ba, so yakeyi ta zama macen da ko ina a duniya za'ayi alfahari da ita, "Zeemarh na gaishe ki, yau dakyar taje makarantar islamiyya wai ni zata bi, murmushi Nadeeyah tayi tace "Allah kuna lalata ta ne, anjima zan kira Anty ince ta dinga zane ta, "u are on ur own ya fadi hade da cewa kema musa a zaneki kuwa, sai ayi 50-50, dariya sosai tayi wacce ta sanya Hilal nishadi, zatayi magana kenan taji Anty Raly na kwala mata kira, sallama tayi mishi ta kashe wayar ta fita da sauri, kallo ta bita dashi fuskarta dauke da Murmushi, tace "Nadeeyah daga hannu sama mu godewa Allah, da sauri ta daga dan bata san me zasuyi ma adduar ba, bayan sun gama adduar tace "Allah ya kawo miki taimako, yanzu Taheer ya fita a gidannan, kaii yau saboda farin ciki bansan yadda zanyi ba, kin gama dacewa duniya, lahira kadai zaki nema, Nadeeyarmu ce zata zama matar Taheer surukar Anty Saude, wannan dadin ina zan kaishi yau, rufe fuska Nadeeyah tayi ta kasa gane ainihin yanayin da take ciki, na farin ciki ne ko akasinshi, kalaman Hilal ke mata yawo a zuciyarta, wanda sabonsu ke bata mamaki duk da har yanzu tana shayin shi, ga kuma zazzafar kaunar da ta gani a idon Taheer, rungumota Anty Raly tayi tace "saura 3 to months ki gama school, lokacin ne zamu fasa maganar nan, wallahi dadi yau kamar zai kasheni, daki Nadeeyah ta wuce da sauri tana nazarin abubuwan da suka gifta tsakaninta da Tahir...... ********___******* Turjiya takeyi a kasa tana ihu tana fadin "indai yaya Jamal zaije itama sai taje, dariya Hafeez yayi yace "Haba autar mami, yaya jamal fa ba bin mu zaiyi ba, ni da Papy kawai zamu tafi, kiyi hakuri kinji, fitowa yayi yana gyara button din rigarshi yace "fada mata gaskiya mister, dani za'a, dan Allah kafin mu dawo ki mutu tunda ni sa'anki ne, wani ihun ta saka wanda ya sanya Anni da sauki ya samuwa fitowa tana fadin Jamal zan ci maka mutunci akan yarinyar nan, turo baki yayi yace "haba Anni, kina ganin yarinya ta rainani, da nayi aure da wuri da na dire wacce ta fita ya karashe hade da rankwashinta, jikinshi ta shige tana ihu tana yakushinshi tana fadin "babu inda zakaje walhy, ni sai dai mu tafi tare, tureta yayi yana dariya yace "zan gani yau, ji min rigima fa, fitowar Papy ne ya sanyata zuwa gurinshi tana kuka, daukarta yayi yace "haba mamana, kaduna fa zani ba nan kusa ba, zo kiji a kunne, mika mishi kunnen tayi yayi mata rada, dariya tayi ta kalli Jamal tana mishi gwallo, har suka shiga motar tana tsalle tana ma Jamal gwalo tana cewa "an mishi wayau wooo, dariya sukayi dukkansu a motar, ta window ya leko yayi mata nashi gwalon shima kamar yaro karami, janta Mami tayi suka wuce daki dan kar Jamal ya sake ballo mata august... Karfe Hudu da minti ashirin suka shiga garin Kaduna, tunda suka shigo cikin garin Papy yaji jikinshi ya mutu, shidai yasan meeting yazo yi a Kaduna state university, amma yanzu ji yakeyi kamar wani abu mai muhimmaci akasin haka ne ya shigo dashi, Hotel din da aka kama musu Hafeez ya kaisu sannan ya yi musu sallama ya wuce da niyyar dawowa da safe... Washe gari bayan sun gama komai karfe biyu Hafeez yazo ya daukeshi, suna Hira Hafeez yace "mishi daga gidan kakanshi yake, baiji dadi ba jiya kwana yayi yana gudawa, da gangan ya fadi haka dan hakar shi ta cimma ruwa, in ma suna da dangantaka to suna ganin juna a yau zasu gane su kuma warware mishi komai, gidan Baffa ya wuce direct kamar yadda Papy ya bukaci zuwa gaisheshi,, A daidai kofar gidan yayi parking, cike da girmamawa ya bude mishi kofa yayi mishi iso har cikin gidan, fuskar Ma'u ke fuskantar hanyar shigowa, kamar an manne ganinta a fuskar papy, kallon Baffa tayi ta dago ta kara kallon Papy, Da sallama ya shigo ciki ya karaso ya tsuguna ya gaida Goggo, motsi kawai bakinta keyi amma ta gaza furta ko kalma daya, kamar ance Baffa ya dago nan

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156