Skip to content

Chapter 91

Chapter 91

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

mutumin dake gabanta yana tambayarta ko tana san danshi, ta ina zata iya butulce mishi, a cikin jerin da ta lissafo babu wanda bai taka rawar gani cikin rayuwarta ba, kuma Daddy ne ya samar dasu, dago kai tayi suka hada ido da Mummy ta harareta hade girgiza mata kai, dauke kanta tayi da sauri ta kalli Daddy dake sake jefo mata tambayar, gyada kanta tayi a hankali alamar eh, wanene shi? Dan Musaddiq yazo min da zancenki, in wani kike so shikenan sai sawun giwa ya taka na rakumi, wani irin girma ya kara a idonta ta kasa bashi amsa, "Ko Musaddiq din kike so? Hannun Husnah ta rike sosai ta kasa dago ido ta kalleshi bare ta bashi amsa, sau uku yana tambayarta tana yin shuru, dariya yayi yace su tashi tafi, Nadeeyah har tana tuntube da kofa tayi saurin fita, Maida kallonshi gurin Musaddiq yayi yace "To Malam ka shirya ma aure? nawa ka tara daga albashinka, nidai kasan ba ruwana nima da kaina na auri matata ya karashe cikin zolayar dukkansu biyun, Ganin ya saki fuska yasa Mummy zama a kasan kafarshi, "Dan Allah Daddy ka rufa min asiri, bai kalleta ba yace "Allah ne mai rufawa Zainabu, me ya faru? Hawayen bakin ciki ta fara yi tace "Yanzu kai farin cikinka ne danka guda daya tiloo ya kare anan, tsakani da Allah duk yadda manyan abokanka ke miko ya'yansu mata gurinka domin shi, sai kuma suga ya kare a gurin yar Mai gadi, yadda ta fadi abun ya soki Daddy Matuka, nan da nan fuskarshi ta sauya yace "akan Nadeeyah zan iya bata miki rai wallahi, idan kika sake kiranta da yar mai gadi a matsayinta na jininki wallahi hukuncin da zan miki ba mai dadi bane, cikin bacin rai ta mike tace "ba jinina bace, uwarta ce kadai jinina, kai kasan asalinsu ne, wa yasani ma ko ubanta barawo ne ya shigo cikinmu aka bashi aure, wallahi bazan yarda in hada jini da marasa asali in samu bara gurbi cikin zuri'ata da zanyi tunkaho da ita ba, "wallahi bazata sabu ba, ai nima ina da hakki akan shi, saboda haka wallahi indai ni na haifeshi bai isa ya auri Nadeeyah ba, Sam Daddy bashi da saurin hannu amma tabbas a lokacin yayi niyyar dauke fuskar Mummy da mari, a hankali yace "ke kika haifeshi, ke kuma nike iko dake, wallahi tallahi in har kikayi abun da auren nan yaki yiwuwa sai kin bar min gidana, kinga sai kowa ya nuna ikonshi, Asali kuma Nadeeyah bata da wanda ya fini, a yanzu na zama asalin Nadeeyah, ni ne ubanta, ni ne danginta da komai nata, sai ki je maiduguri ki binciki Asalin Alh Garba kyari mai fata, kallon Musaddiq yayi yace ka tashi kaje ka fara shiri daga bangarenka, ni a bangarena bani da matsala... jiki a sanyaye Musaddiq ya mike ya fita daga dakin, bai taba tunanin zai samu wannan matsalar ba, gashi kuma har ga Allah yana son Nadeeyah bazai iya rabuwa da ita ba, ga kuma Mummy zata yi mishi karan tsaye cikin rayuwarshi, tunane tunane ya dinga yi ya rasa mafita ya dauki wayarshi dan kiran Hilal, a kashe wayar take dan haka ya kwanta yanata sakar da bata da karshe.... Mummy kuwa tana fita dakinta ta wuce cike da bakin ciki ta daga waya ta kira Radiya da Raudha da ta dawo gida weekend tace su kira Raliya suzo su sameta a gidan Goggo, jin yadda muryarta ke rawa suka san ba lafiya ba, ko wacce hankali tashe ta shirya tafiya gidan Goggo... "Radiya ina zaki da sassafe?, ko abun karyawa bakiyi ma su Umma ba kuma kinsan ba ita kadai bace, shekeke ta kalleshi tace "ni ma uwata ke nema na, ko bani da ikon amsa kiran, su tashi su daura da kansu tunda dai suna da hannu, shikenan ni bani da sukuni saboda umma tazo, a'a wallahi bazai yiwu ba, Raees babban danta ne ya shigo yace "Mama wai inji Umma tace ki kawo mata ruwan zafi zata sha magani, wani dogon tsaki taja tace "maza jeka gurin Gyatum kace ta kai mata, hijab ta dauko tasa tana kunkunin da tun zuwansu gidan takeyinshi, Mikewa mijinta yayi ya kira kanwarshi Haleesah yace "tazo tayi ma Su umma abinci, sam baya jin dadin abin da Radiya kema yan uwanshi dashi kanshi, hakuri kawai yakeyi saboda darajar mahaifinta, yana shiga kitchen ya tarar da wata yar budurwa wacce shekarunta bai wuce sha tara ba. tana tsaye tana taya gyatum aiki, Da sauri gyatum ta gaisheshi ya amsa yana kallon yarinyar, itama tsugunawa tayi har kasa ta gaisheshi, kamanninta da gyatum shi ya tabbatar mishi yarta ce, saidai wannan din bak'inta mai kyau ne, da dara daran ido farare tass ga kyawun diri, har zai fita yace "Gyatum wannan yarki ce? Murmushi tayi tace "eh Alhj, auta ta ce, a gurin kanwata take a jos, a can take karatu, yanzu ma tazo hutu ne tazo tayani aiki, gyada kanshi yayi yace "Dan Allah ku taimakeni ku hada ma su Umma abun karyawa, in san samu ne ma su samu tuwon laushi, da sauri gyatum ta mike tace "har sai ka roka, Bar wanke wanken nan Fatima ki fara hada kayan karyawa, Cike da jin dadi ya fita dan ko abincin baiyi dadi ba yasan zai fita kunyar mahaifiyarshi da kannenta... Cikin kwarewa Fatima tayi miyar kukar da taji daddawa da dagargajajjen naman kaza, sannan ta tafasa kifi kadan ta sa citta da karumfani da tafarnuwa ta dakesu tsaf ta juye a cikin miyar, nan gida ya kaure da kamshi, tana gamawa suka shirya komai cikin cooler gyatum ta dama musu kunun gyada ta fito da garin kosai ta kwaba tasa kwai da albasa ta soyashi gunin dadi, manyan Coolers gyatum ta zuba abincin aka kai musu sannan ta zuba a kananan coolers ta ajiye wa mai gidan a dining, saboda farin cikin ganin tuwon malmala biyu Umma ta cinye, cike da jin dadi Haleesa ta kalleta tace "yau Umma taci abinda take so, san samu kullum da safe da dare a dunga miki tuwo, to hakan bazai yiwu ba, hidimar Maman Raees tafi karfinta, harara Indo kanwar Umma ta jefawa Haleesa tace "yau da tayi kasheta aikin yayi, Dariya Haleesa tayi tace "waya fada miki ita tayi, ita bata gidan ma, mai aikin gidan ce tayi, a daidai lokacin fatima ta shigo kwashe kayan abincin, albarka suka shiga sa mata har ta gama ta fita, umma dai da ido ta bita, a kullum tana ma danta adduar samun mace ta gari ba mai kyale kyale irin Radiya ba, yanzu din ma bazata fasa ba, ganin da tayi wa Fatima na farko taji ta shiga ranta, saidai bazata tilasta shi ya nemeta ba, za dai ta cigaba da addua, dan tabbas danta bashi da mace a gidanshi...... *Wai ina Hajiya Goggo Ma'u ne* Bangaren Goggo kuwa tunda Anni ta tare kullum cikin kunan zuci take, tayi asirin, tayi tsafin duk a banza saboda yin auren Baffa ma kadai karyewar alkadari ne, ga yawan abinci sadaka da Anni keyi kusan kullum domin nema musu tsira ranar Gobe kiyama, Tunda Goggo taga asirin nata yaki aiki saidai suyi ta cin kudinta sai ta hakura

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156