Chapter 19
Chapter 19
waye zai rike su? Ina zasu je? Goggo tayi saurin cewa "ai Nadeeya ta mallaki hankalin kanta, sannan ga Hafeezu shi zai fito da mata yayi aure sai ya hada ya rikesu gaba daya, in suka zauna anan shine hankalinsu zaifi kwanciya, d'an abun da baza'a rasa ba ma dinga taimaka musu, ai su yan gata ne, tunda akwai Hafeezu, kuma su uku ne zasu dinga ganin junansu, kama kwantar da hankalinka akan maganarsu babu abinda zai samesu, ake mutuwa abar jariri ma bare su da suka mallaki hankalin kansu, Daddy dake tsaye cike da al'ajabin kalaman Goggo ya kasa motsawa bare yayi magana, jiran ta bakin Baffa kadai yake in hukuncin da zai yanke mai yiwuwa ne, A d'arare Baffa yace "eh kuma haka ne kema kin kawo shawara, rabasu din baida amfani gara Hafeezu yayi aure ya rike kannanshi tunda yanzu da dan jari a hannunshi, yanzu bari Hafizun yazo sai mu ce mishi ya fito da matar da zai aura cikin gaggawa, kuma ya gyara gidannan ya zauna da matarshi ta rike mishi kannenshi... Sallama Daddy yayi ya karaso gurinsu cikin kunan rai, zuciyarshi nata juya kalamansu, lallai ya yarjewa kanshi duk zumuncin da ake samun tsaiko ko rashin jituwa a cikinshi daga tushe abin ke farawa, duniya ina zaki damu, wannan shi ake kira da Zumuncin zamani, tun ranar farko da ya fara ziyartar gidan da niyyar neman aure yasan akwai matsala a cikin zuri'ar, ko gurin bashi auren yasan cewa suwaiba bata da galihu, da tana da galihu da----- bismillah zauna mana Alhaji, "Goggo ta katse mishi zancen zucin da ya tafi na tunanin abubuwan da suka faru shekaru da dama, zama yayi fuskar nan babu yabo ba fallasa, a lokacin duk sauran yan yaran suka karaso, Dakin ya musu kadan, amma haka suka rab'a suka zazzauna, hankalinsu suka mayar gurin Baffa dan jin abin da yasa ya tarasu, Da bismilla ya fara, kowa ya shiga nutsuwarshi dan duk tunaninsu maganar da zai fada ta dattaku ce, sai da ya fara jajantawa su Nadeeyah akan zazzafar rashin da sukayi, sannan ya cigaba da cewa wannan mutuwar duk ta shafemu kuma ta taba mu fiye da tunanin me tunani, Abun da yasa na taraku anan ba komai bane sai dan in fada muku na yanke shawarar yadda zamuyi da Nadeeyah da Zainab, Kallon gefen da Hafeezu yake yayi yace "kai Hafeezu, kana da yarinyar da kake so? Girgiza kai Hafeez yayi cikin rashin fahimta, Baffa ya cigaba da cewa "to na baka nan da wata daya ka nemo yarinyar da zaka aura domin ta zo ta rike maka kannenka, wani irin kallo mummy ta yi ma Baffa, a lokacin in ranta yayi dubu to duk sun baci saboda a tunaninta Baffa ne zai rikesu Nadeeyah saboda sune suka fi cancanta da rikesu din, maganar da Baffa ya cigaba dayi ne ta katse ta, "abinda yasa nace haka, saboda kaga rabaku zai iya zama matsala, duk inda kuka je bazaku ji dadin zama ba saboda kun saba da junanku, ku kadai kun isa ku debewa kanku kewar rashin iyayenku, Goggo ta amshe da cewa kwarai kuwa, kuma kai Hafeezu hankalinka zai fi kwanciya in kasan kannenka na gurin ka, fatanmu dai Allah yasa a samu mace ta gari, Duk cikar gurin babu wanda maganarsu tayi mishi dadi, har shi Baffa din bayan gama maganar saida yayi ajiyar zuciya sannan ya cigaba da zubda hawayen zuciya, Anty Reemah ta bude baki zatayi magana Daddy ya rigata, "kwarai kuwa Goggo shawararki tayi kuma na gamsu da ita dari bisa dari, Musaddiq da Hilal na jin furucin Daddy wanda ya zama shine na karshe da ya rage suji me zaice, zuciyoyinsu suka tsinke a tare, nan take kwalla ta taru a idon musaddiq da ya kalli gefen Nadeeyah da Hafeez yaga dukkaninsu kukan rashin gata sukeyi, kallon bakin Daddy yayi da ya cigaba da cewa "ba sai Hafeezu ya fita neman aure ba, ni nan zan bashi mata wacce nasan bazata cutar da kannenshi ba, Ya kalli Baffa da yayi kasake yana sauraronshi yace "ina son hada auren HAFEEZU da HUSNA..... Kamar saukar aradu haka Goggo taji zancen, zaro ido tayi cike da firgici tace wace Husnan, " *Husnah Mukhtar Kyari*, Daddy ya fadi da gadara saboda yasan shi kadai keda iko da ita,, Nawa Husnan take muntari, Goggo ta fadi tana share gumin daya fara tsatsasafowa a goshinta, Daddy yace "Ita da Nadeeyah shekarunsu daya, in har zamu iya barin Nadeeya ta rike kanta da zainab me zai hana mu hada auren da Husna sai su zauna su rike kansu gaba daya, jinin ai daya ne, babu wani bare ko Baffa, wani irin murmushi Hilal yayi da karfi yace "You are the best grandpa.. Anty Reemah da ta harbo jirgin mahaifinta tayi saurin amsheshi da fadin "hakan shine daidai Daddy, kaga basai ma an shigo da bare ba, kuma Husna ma ai ba yarinya bace, muma muna kamarta aka daura mana aure, Allah ubangiji ya inganta wannan hadin... sai dai ya inganta uwarki Goggo ta fadi ba tare da tasan ta danno ashar ba, Kowa a gurin ya gimtse dariyarshi saboda sunsan yadda Goggo ke son Husna da Badariyya, barin Husna ma son ta na musamman ne a ranta, kullum hango Husna take cikin villar rahamaniya, bazai yiwu ta bari rayuwar Husna ta kare a gurin wadannan masu kashin mindirikin ba, Haukar gangan ta fara yi musu harda kuka wai Daddy yayi mata Gadara da diyarshi, cikin sanyin murya Daddy yace "Goggo ba gadara bane, ai naga duk jikokin ne, tsatso daya suka fito, basu da wani banbanci, cikin ficewar hayyaci tace "Allah ya kyauta wadannan masu kashin tsiyan su fito a tsatson---- da sauri mummy ta mike ta rufe mata baki tayi mata ihun da bata san ta mata shi ba, itama a nata bangaren ko sama da kasa zasu hade bazata bar autarta ta auri Hafeez ba, dan ta kawo karshen rigimar tayi kasa da murya mai alamar kuka tana matso hawaye tace "Rike su Nadeeyah bazai taba zame min matsala ba, basu da kowa sai ni, nice uwa kuma ubansu, dangin mahaifinsu suna nesa damu "Aagadaz" ba nan kusa bane bare muce zamu tura wani nashi yazo, durkusawa tayi gaban Daddy tace "dan Allah in bazaka damu ba zan rike yaran nan a gidanka, ajiyar zuciya Daddy yayi cike da farin ciki yace "Babu wani matsala ai d'a duk na kowa ne, bare kuma yaran nan jininki ne, Baffa farin ciki cike fal a zuciyarshi yace "Nagode nagode Alhaji Allah ya saka da alkhairi, "babu komai Daddy ya fadi yana kallon Goggo dake zabga mishi harara, zuciyarta cike take famm saboda bata san jinin suwaiba ya rabi kowa nata, bata ankara ba taji muryar Anty Reemah na cewa "Mummy dan Allah ku bani daya daga cikinsu in tafi da ita, nima in samu ladan rikon maraya,, Goggo ta kara hassala ta figi hijabinta a kan gado tace "ki je cikin kabari ki fito da Suwaiba da *ATIKA* ki hada duk ki tafi dasu..... Banda Mummy da Baffa da suka san wacece Atika, babu wanda a cikinsu yasan wacece Atika?? Sunan Atika ya shiga yawo a kunnuwan dukkan yaran dake gurin.......WACECE ATIKA???? Shine tambayar da zuciyoyin mazauna
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156