Skip to content

Chapter 43

Chapter 43

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

tayi tace "maza matso ki tayata ku jera kayan, ke kuma Badar, bana son tashin hankali, Nadeeyah yar uwarki ce, kaddara ce ta sanya kukayi nesa da juna, yanzu kuma Allah ya hada ku, kuma kinsan baki da yadda zakiyi da hadin Allah... Ajiyar zuciya Hilal yayi a ranshi yace "Allah yasa Mummy ta daure a haka, yanzu ne zai tafi hankalinshi a kwance, yafi son yayi nesa da ita ta samu damar yin karatunta ta zama cikakkiyar mace, yasan in har yana ganinta kullum bazai iya controlling kanshi ba, dole yayi abin da zata gane halin da yake ciki, shi kuma ba yanzu yake son furta mata ba, yana matukar tattalin kalmar har sai ta cimma lokacin ta..... Karfe 5pm suka dawo gida hannunsu rike da ledoji, kalolin jallabiya guda shida Hilal ya siyo ma Nadeeyah, sai flat shoes guda biyu milk nd brown, dayar ledar kuma jallabiya ce guda biyu, kwala kiran Husna yayi, da sauri ta fito daga kitchen tana tsane hannunta tace "ya Hilal gani, "ledar ya mika mata yace "wannan naki ne, kinsan yanzu mun fara dasawa, tsalle tayi tana ihu tace "Thank u *bro Son* , bai damu da sunan da ta kirashi ba yace "wannan ki kaima Nadeeyah, kinga kayanta duk sun kode, zan ma Anty Rally magana sai kuje kasuwa a samo mata yan atamfofi, karbar ledar tayi tace "ummm ya Hilal ashe dai kana da kirki, gaskiya thank u, kamar kasan in tasa kaya abin na dan taba ni, wasu ma sun mata kadan, Murmushi jin dadi yayi yace "yauwa gaskiya i love u, u will be my personal person daga yanzu, dariya tayi tace "godiya nake, gashi gobe zaka tafi, gaskiya zanyi missing dinka, bari naje na kai mata, nasan zata ji dadi.... Bude kayan Husna tayi ta dinga yaba kyawunsu tana gwadawa a jikinta, tana cikin gwada wata ja a cikin na Nadeeyah Badar ta shigo dakin, zama tayi a gefen gado ta dauki daya a ciki tace "waye ya kawo mana jallabiya, shine har kika fara zaba baki jirani ba ko ta fadi a gadarance, kwacewa Husna tayi tace "to Mummy kiyi hakuri, ya Hilal ne siyan ma Nadeeyah, ta dauko nata tace 'kinga nawa nima, wayyo, ai kamar Husna ta watsa mata ruwan zafi haka taji, dama duk yau cikin kunci ta wuni saboda yadda Mummy tayi wata wuzu wuzu akan Nadeeyah, mikewa tayi idonta ya ciko da kwalla zata bar dakin, tausayi taba Husnah tace "sis zo wasa nake miki, guda biyu ya kawo mana ni da ke fa, sauran ne na Nadeeyah saboda bata a kaya, bata saurareta ba ta fita daga dakin dan tasan Hilal bazai taba yi mata kyauta ba, ninke kayan Husna tayi ta maidasu cikin ledar ta wuce kitchen ta kira Nadeeya, A tsorace Nadeeya ke daga kayan tace "duka nawa ne? gyada mata kai Husna tayi tace "u are very lucky, yaya Hilal bai taba kyautar ko da naira dari biyar ba, yaushe ma kaga fuska a gurinshi bare ya baka, sai gashi yau har ni ya hada, dark blue din ta dauko a ciki tace "gwada wannan nasan zata miki kyau, bayi taje ta sa a jikinta, fadin rigar yayi mata cibb saboda tana da dan jiki, sai dai tsawon ya so yayi mata yawa, madubin bayin ta kalla hade da gyara gashin da ya kwanto a goshinta, ita kanta ta yarda a zuciyarta rigar ta mata kyau, dakyar ta iya fitowa daga bayin saboda kunyar Husna, wooooww.. Husnah ta fadi a fili, a cikin ranta kuma tace "see beauty, oh Gosh, Allah baya bawa mai wuka nama, "kinga yadda yayi miki kyau kuwa, kunya ce ta ishi Nadeeyah tace " nagode, bari inje in cire, tareta Husna tayi tace "godiya dai zamu je kiyi ma "ya Hilal, daburcewa Nadeeyah tayi tace "a'a dan Allah bari in canza kaya sai muje, dagewa Husna tayi tace lallai sai dai suje a haka, dakyar ta yarda ta yafa gyalen a kanta, murda kofar dakin suka ji anyi, a tare suka waigo, daburcewa Nadeeyah tayi ganin Musaddiq da Hilal tsaye a bakin kofar, karasowa ciki Musaddiq yayi cikin zolaya yace "a'a iyye, kaga kanwata, ashe dai kina da kyau haka, to juyo ki nuna mana kwalliyar mana, janyo hijab tayi ta cukwikwiye kanta tace "ba kwalliya nayi ba, Husna ce tace in gwada ko zai min daidai, dariya yayi yace "kuma ya miki kyau, ashe dai mun iya zabe, to babu ko yar godiya, kara rufe fuskarta tayi tace "yanzu dama zamu je muyi, kuyi hakuri, Nagode Allah ya saka da mafificin alkhairi, Ameen Ameen, muma mun gode da addu'ar da muka roka, gurin Hilal Husna ta matsa tace "ya Hilal kaga yadda kayan suka karbemu, thank u once again, murmushi yayi yace "never mind, kinga mukullin motata cikin kayan nan, zazzage kayan ta koma tayi, babu komai a cikin su, dago kai tayi tace "baya ciki, ko ka barshi a jikin motar? Tunani ya fara yi yace "eh to bari inje in duba, ta gefen ido yake satar kallonta tun shigowarshi dakin, sai da zai fita ne ya kalli yadda ta matse kanta, murmushin shauki yayi ya fita zuciyarshi wasai saboda yadda yaga ta fara samun sakewa a gidan..... Jirgin karfe shida na yamma zasu bi, tun safe Hinad da Zainab suka tafi saloon suka wanke kansu akayi musu kitso, daga can gidan Mummy aka wuce dasu, nan suka yini har bayan la'asar sannan suka soma shirin tafiya, har bakin mota ta rakasu tana dada yi ma zainab nasiha, saida taga sun shiga motar sun zauna ta kalli Zainab da idonta ya ciko da kwalla tace "kuka kuma zakiyi, to bari in tafi in barki tunda kuka zakiyi, hannunta Zainab ta rike tace "Adda zan tafi in barki a gidan mummy su dinga saki kuka, meyasa bazaki zo mu tafi ba, share mata hawaye Nadeeyah tayi cikin dakiya tace "inji wa yace miki zasu sani kuka, bana nuna miki kayana da mummy ta kawo min ba, yau ma tace zata kuma kawo min wani, kar kiyi kuka kinji dukkan mu zamuji dadi, gyada kai Zainab tayi tace "Haka mumyn Hinad tace min, sake matse hannunta tayi tace "banda rashin ji kinji, in kikayi rashin ji zasu fada min, ni kuma sai inyi ta kuka anan, kinaso inyi kuka, girgiza kai tayi da sauri tace "a'a bana so, bazan kuma yi rashin ji ba, kumatunta Nadeeyah taja tace "good girl, hira suka cigaba dayi suna jiran drivern yazo suka hango motar Hafeez ta shigo gidan, da murna Nadeeyah taje gurin shi tana mishi barka da zuwa, rungumeta yayi suka wuce gurin su Zainab, ta window zainab ta fito ta dane wuyanshi tana murna, komawa mota yayi ya dauko katuwar leda yace "wannan sweets dinku ne ke da Hinad, kuma saura inji labarin kin mayar da shi abincinki, kara kankameshi tayi tace mun gode yaya, amma zaka dinga zuwa gurina ko? "Kullum zaki ganni, kedai kiyi karatu, banda rashin ji, banda takurawa mutane akan abin da babu kina ji na ko, gyada kai tayi tace "duk na sani Adda Nadeeya ta fada min, motar ya mayar da ita yace "to Allah ya kiyaye hanya, Hinad ki gaida Anty Reemah kinji, "in shaa Allah

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156