Skip to content

Chapter 79

Chapter 79

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

karka kashe ni, bari in kawo maka wani abinci me nauyi, kallon Husnah yayi dake kara jaddaddawa Hafeez suje ta bashi kayan shi ya saka, "in kinje ki bashi riga kadai ta isheshi, kinga sai kuji dadin zagin halitta ta, ya karashe yana kai kofin bakinshi, dariyar ma kin fitowa Husnah tayi suka fita tare da Nadeeyah, Dariya Hafeez yayi yace "manta da ita kaji, gida zan koma in canza kaya, bari in kira Jamal ya kawo min mota, ciro key Musaddiq yayi yace "ga tawa kaje ka dawo kafin a fara walimar, karbar keyn yayi yace "ka dai ajiye min nawa abincin kar ka cinye kai kadai, "Haaahaha... zan daina cin abinci kwata kwata a idon mutane, gara in rage wannan kibar, da zan iya ma harda tsawo zan rage, "dariyar Shirmen Musaddiq Hafeez yayi ya fita yana jin dadin yadda al'amura suke kasancewa kamar yadda Mamma take so, Allah sarki Mamma, ina ma ana mutuwa a dawo kiga yadda wuya take neman rikide mana ta zamto dadi, kiga yadda dan uwan da baki sani ba yake gatata mu kamar shi ya tsuguna ya haifemu, Allah yayi miki Rahama ya fadi ya shiga motar zuciyarshi a dagule saboda tuno iyayenshi da yayi....... Ana idar da sallar isha'i su Nadeeyah suka fara shirin barin gurin su Anni, hankalin Nadeeyah a kwance ta gama shiri dan tasan yanzu su Anty Radiya sun bar gidan, "kallon banza da habaicin talauci hade da rashin asali da suke mata yana sosa ranta matuka, kalmar da Anty Raudah ta fadi na "anyi clean fata ta murje da abinci akan kari sai kace wata yar shugaban kasa, a dai dinga tuno asali dan kar garin iyawa a wuce gona da iri!! Wadannan kalamai sun matukar tsaya mata, dan ma Musaddiq dake bayanta wanda dan shi Anty Raudah tayi mata habaicin yace "Haba Anty, sai kace sa'arki, dani take magana bada ke ba, ku ke jawa kanku raini wallahi, yayi tsaki a hankali hade da cewa Nadeeyah ta kira Husnah su tafi... Hannu ya kyasta mata a kusa da idonta, a firgice ta dawo daga tunanin abubuwan da suka gifta dazu a gidan, rage Murya yayi yace "Tunanin su Anty ko? Abin da ya kamata ki saba dashi ne tunda saidai in basu zo gidan ba, in kika kula mutum a kullum burin shi ya bata miki rai to sai kiyi fatali da duk abin da yace, domin shi kadai zaiyi dakon bacin ransa, "Zuciya is very special my sister, fill it with love, karki bari bacin rai ya samu kofar shiga cikinta, dan bacin rai na destroying duk abin da aka tanadarwa zuciya, dan haka bana san ganin tunani ko bacin rai nan a tare dake, kinji ko? gyada kai tayi hade da murmushinta mai kyau, "Thats my lovely sis, oya kira mana Husnah mu tafi, kafin ta kai ga amsawa suka hango Husnah sun fito tare da Hafeez da Ruwaidah a tsakiya, gefe kuma Jamal ne sanye da kayan bacci shima yana dosar inda suke, "Badai bacci zakayi ba, Musaddiq ya tambayeshi yana mishi kallon mamaki, jingina jikin motar yayi yace "in banyi bacci ba ai sai in kasa moruwa, yau ko tamola bata kaini garuwa ba, wahalar da Baffa ya bani yau ba kadan bace, "duk wani abokinshi da yazo gurin daurin aure wanda baida mota saida na maidashi gida, just imagine kaine, hmmm thank Goodness akwai ruwan zafi, da yau sai na tashi aiki, ya karashe yana danna bayanshi, "Lazy youth!! Ruwaidah ta fadi tana boyewa a bayan Hafeez, dariya ta basu dukkansu Nadeeyah tace "duk kokarin nan da yayi ki kirashi lazy, murya cakwai tace "Allah Adda he is very lazy and he can exaggerate, yanzu haka gida uku yaje, haka Mami ke fama dashi baya san a moreshi, Rai a bace Jamal yayi inda take yana fadin "ni sa'anki, wani irin ihu ta saki hade da rugawa ciki, bayanta yabi da gudu dan yaci alwashin ko a gaban Papy ne sai ya gurji bakinta, Dariya Hafeez yayi yace ku shiga mota ku tafi dare nayi, indai su Jamal ne kullum sai sunyi sau ba adadi, ya kasa gane dadin tsokanarshi takeyi, saboda bata da abokin wasa shiyasa ta maidashi abokin wasanta, shi kuma san girma yasa baya wasa da ita, " haushin hakan yasa ta rainashi sosai, motar suka bude suka shiga suna dariyar Ruwaidah da Jamal, Sallama sukayi ma Hafeez da kunya ta hanashi katabus saboda irin kallon da Husnah take mishi, dalilin da yasa ya sanya Ruwaida a tsakaninsu kenan da ya fito yi musu rakiya, ko a da lokacin da yayi wauta da rudin kudi mata ke kawo kansu, ita kuwa Husnah ganin irin gidan da ta fito ya sanyashi jin kunyarta da taka tsantsan, dan yasan tafi karfinshi, shi da bashi da cikakken asali kamar yadda Goggo ke yawan fada, wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa, gara ya nemi saffa saffa dai dai shi.... Mrs Tijjani Shattimah...... [01/04 3:08 PM] fareedah: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣0⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Kasa tabuka komai Nadeeyah tayi ta dauki wayarta ta latsa number Hilal, sai tayi kamar zata shiga sai tayi saurin kashewà, tun daren jiya take abu daya, tasan yadda ya saba da yi mata text haka nan bazai ki turowa ba sai da dalili, Abin da bata sani ba shine, duk latsin da zatayi ma numbershi tana shiga kadan sai ta katse, da haka ya fahimci ta damu da rashin tura mata sakon wanda yayi shi domin fahimtar wani abu daga gareta, Yana gama shiryawa ya dauki wayar ya latso ta, ajiye kwan da take kadawa tayi da sauri ta dauka ringing na farko, "ajiyar Zuciya yayi a hankali, ita din ma hakan tayi amma nata ya dan fito kadan, shuru ne ya ratsa wayar na yan sakwanni, shi ya fara katse shurun ta hanyar cewa "ina kwana Anty, saura kiris wayar ta fado a hannunta tayi saurin riketa tace "kayi Hakuri, ina kwana, "a'a ai ni ya kamata in fara gaisuwar, kina nan lafiya? bata amsa ba ta sake cewa "ina kwana, yasu Anty? dariya yayi mara sauti yace "kowa lafiya, "harda k--- shuru tayi ta kasa karasawa, "Harda ni Nadeeyah, lafiyata kalau, alhamdulillah ta fadi a zuciyarta, a fili kuma tace "to Masha Allah, gyara tsayuwarshi yayi yace "jiya kuma bakiga sakona ba, ke kuma baki damu ki turo ba, shikenan da mutuwa nayi haka zaki manta dani bare har in sa ran addu'a, cikin rawar Muryar da take nuni da alamun tayi matukar missing sakonnin shi tace "Dan Allah kayi hakuri, na rubuta sai na kasa turowa, "ehen me kika rubuta? fada min da baki, toshe bakin tayi da hannu taki sakinshi dan bata san abun da zata ce mishi ba, tana jiyo Muryar Hinad na cewa "Papa na kiranka, muryarshi taji bayan fitar Hinad yace "ina jiran ganin sakon irin na jiya sakk, zan gane rubutun na jiya da na yau, sai na jiki ya karashe hade da kashe wayar ya sauka kasa gurin Papa.... ******* Karfe goma na dare Mummy ta shigo dakin su Nadeeyah bayan ta gama kashe kayan kallon parlon, kallon Nadeeyah tayi wacce ke zaune da blue riga da wando na bacci, tasan Nadeeyah ce kadai a gidan

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156