Skip to content

Chapter 32

Chapter 32

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

diyar fari, nan fa suka shiga tsokanarta cike da nishadi kamar ba kishiyoyi ba..... *BAYAN WATA BIYAR* ●●●●●● *Mummunar Kaddara* Har lokacin Baffa bai waiwayi gida ba, yana can yana neman kudi saboda ya tsira mutuncinsa da na iyalinsa, kullum cikin tunaninsu yake, ciki harda Atika da sam bashi da masaniyar tana dauke da cikinshi, cikin kudirar ubangiji neman da yakeyi Allah na sa mishi albarka a cikinsa dan har ya samu ya siya dan gida mai daki uku ginin siminti na jaka biyar da rabi a cikin jalingo, a wannan lokacin ne ya yi niyyar zuwa gida dan ya tattaro iyalinshi ya fara sabon zama dasu mai cike da jin dadi.. A cikin watanin da suka shude aka daura auren Maryam Da Bala Shaho, murna a gurin shaho ba'a cewa komai saboda yadda ya dauki malam da ahalinsa, bauta ce kadai bazai iya masa ba, domin kuwa ya taimaka mishi gurin samun rayuwa mai inganci da tsafta... Atika ma tayi bul bul, cikinta yayi girma sosai har yayi mata nauyi, gaf take da shiga lokacin haihuwarta, kula ta musamman take samu a gurin Hardejo da matanshi, ba irin kayan da basu sak'a ma jaririn ba tun kafin Zuwanshi duniya, a wannan lokacin Atika ta dan fara jin fillanci kadan kadan, dan in aka mata magana zata ji amma mayarwa ke mata wahala.... Ita kuwa Ma'u tun da ta tafi can garinsu ukari bata dawo ba sai dai aiken mugun abu da take ta yo wa Atika da cikin jikinta, haka duk juma'a sai ta bi motar katako taje garin dan taga ko mijinta abin kaunar ta ya dawo sannan ta shiga gurin Haire ta bata sakon magungunan da take kaiwa Atika dan cikin ya zube, bata san Haire watsi takeyi da maganin ba, domin ita mace ce mai tsananin tsoro, tunda ta amshi musulunci ta daina duk wani aikin sabon Allah, dama wani lokaci ma'u ke zugata suyi tare, yanzu ko da ba ta nan, kullum tana gidan Hardejo daukar karatu... Yau ma kamar kowace jumma'a ta gama shirye shiryenta na mugun kullinta, ta dauko su Bingel ta shiryasu dan yau in ta tafi bazata dawo ba, tasan da tana garin babu abin da zai hana ta kashe dan dake cikin Atika, yanzu kuwa ta dauki alwashin kashe har Atikan saboda in ta barta to fa Hardejo sai yasan yadda yayi ya sake sata cikin rayuwarsu, gara kawai ta kashesu gaba daya.. A daidai kwanar da zata sadasu da hanyar kauyen suka hango cincirindon yan ta'adda, babu kaya a jikinsu sai wukake rataye a kafadunsu da kugunsu, tsayar da motar sukayi suna ta wasa wuka a kasa, fitsari Bingel ta saki ta fara ihu tana kuka, sakko dasu mutanen sukayi suna mazurai, cikin wani irin yare suke tambayarsu ko su musulmai ne, drivern da yake yana yawon safara, Kuma yasan musulmai sun fara yawa yace "eh shi musulmi ne, nan take suka farďeshi sukayi wurgi da gawar, Ma'u jiki na rawa tace "Dama kai musulmi ne ka dauko mu? Ta fara tambayar karen motar, girgiza kai karen motar yayi yace ni cikakken mabiyin Addinin sarki *HAWAIZU NA UKARI* ne, Dariyar keta mutanen sukayi suka ce "ina za ku? Ma'u da ta gama samun mafita tace "Gembu, kauyen da Malam Hardejo ya cika shi da musulmai, zamuje ne domin yi musu magana akan abin da sukeyi mara kyau, sun yarda bautar iyaye da kakanni sun dauki wani addini da Hardejo ya kawo, cike da farin cikin samun Nama ogan yace "dama mun dade muna son kai farmaki kauyen, mai girma *SADUN* ya dade yana bamu labari akan malamin da yayi wa kauyen kawanya da musulmai, ku shiga mota ku jagorance mu dan mu aikata abin kirkin da za'a dade ana tunamu dashi har duniya ta dade..... A kofar Gidan jauro Ma'u ta sauka da ya'yanta, tayi musu nuni da gidan Hardejo, tace musu zata dubo dayan malamin ko yana nan zata zo ta samesu, wucewa sukayi; ita ma ta kama ya'yanta ta ruga da gudu ta shige gidanta ta turo, babban fatanta shine su fara yin layyarsu da Atika, can kuryar daki ta shige ta kwantar da ya'yanta hade da tsoratar dasu dan kar su tashi suce zasu fita, saida ta tabbatar bacci ya daukesu sannan ta fito ta tsaya a tsakar gida tana kasa kunne, ita dai in bukatarta zata biya Kowa ma ya mutu, yanda taci alwashi a kauyensu na cewar Baffa bai isa ya mata kishiya ba, kuma kawai sai gashi banda kishiyar har 'yan uba gare ya'yanta, inaa sam in ta bari hakan ya faru to bata cika jinin *MANASIR* ba.... Kamar yadda suka saba taruwa a kofar gidan ranar jumma'a maza da mata yau ma hakan ne ta kasance, Kamar daga sama sukaji tsayuwar motar katako a kansu, babu wanda yayi yunkurin katse sallar saboda a iya saninsu kauyen nasu lafiya lau yake domin musulmai sun danyi rinjaye a garin yanzu, tun ba ma komawar shaho cikin musulunci tsundum ba, a sujjadar karshe suke sukaji an fara kai musu farmaki, basu sallame ba har lokacin saida suka gama zaman tahiyar karshe, suna sallemawa kowa ya fara neman hanyar tsira, kewaye su yan ta'addan sukayi suka dinga sarar jikinsu, "Allahu Akbar Malam Hardejo ya fadi nan take gurin ya dauka, a nan fa Shaho da mutanenshi suka tuno da dabanci suka tube kaya suna fadin Allahu Akbaar, suka nufi yan daban, Rashin makamai ne ya cucesu shiyasa duk fadan da sukeyi aka sassari su shaho, cike da karfi Shaho yayi kokarin fusge katuwar wukar jikin ogan, nan fa yasa ihu ya fara sararsu iya karfinshi, a take samarin garin suka shiga gidajen kusa suka dauko makamai, ciki harda Barde mahaifin shaho, shi kuwa Hardejo sallah ya koma ya cigaba dayi yana rokon Allah ya kareshi da dukkan jama'ar musulmi, (idan Ajali yazo) babu makawa sai an tafi, babu addu'ar dake dauke ajali a jikin mutum, kamar hadin baki arnan kauyen suma suka fito da makamansu, "in ka san farkon rigima to fa baka san karshenta ba, Rigimar da Ma'u ta hada saboda san zuciyarta ya haifar mutuwar rayuka da dama, Ma'u bala'i ce a cikin alummar musulmi.... Shaho ya jigata iya jigata, shi kadai ne mai karfin dake yakarsu, sauran arnan garin abin da yasa sukaci galaba akansu saboda daga cikin gidan suka fara gurin matan, saida suka karkashe matansu da ya'yansu sannan suka fito suka hada hannu akan mazan, dama ba karamar tsana sukayi wa Hardejo ba, wani a cikinsu mai siyar da barasa yayi kan Hardejo da gatari saboda shi tuni yake hakonshi dan hani da yayi da shanta ga daukacin musulman kauyen yasa shi ya daina ciniki, Shaho na ganin haka yayi saurin tareshi hade da kai mishi wuka kirjinshi, ta baya wani ya lallabo ya sari gefen kafadun Hardejo, sannan ya sake luma mishi wukar, salatin da ya fara yi ne ya dawo da hankalin shaho kanshi, tuni jikinshi ya mutu ya saki wukar hannunshi ya durkushe a gurin yana rusa kuka, Ya Allah ga hardejonka nan, Ya Allah me yasa baka turo mana da kariya ba a lokacin da muke da bukata, Ni kadai bazan iya ba ya Allah, gawarwakin mutanen ya kalla harda na babanshi ya sake rusa kuka, cikin

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156