Chapter 61
Chapter 61
yayi rai a bace yace "hey bata bukatar garkuwarka, live ur life nd let her live hers, Hannunta ya kama ya cigaba da cewa "ba sa'arka bace, kamar yadda kace, so ka barta tayi abun da takeso, ka nemi sa'oinka ka zame musu garkuwa, yana kaiwa nan yaja ta zuwa dakinsu, Hilal kamar zai mutu saboda takaicin zuciyarshi da furucinshi, To ya zaiyi, shi kanshi baisan ya fadi wasu abubuwan ba saboda tsananin kishin da ya nemi zautashi, Kalaman Taheer sun matukar hassala shi, ledar da yayi wurgi da ita ya dauka ya mikawa Anty Raly yace "ki mayar mishi da abunshi, babu wanda a gidannan waya ta gagareshi, wallahi in kika ce baza ki mayar ba yanzu zan kira Daddy in fada mishi yadda kike son lalata rayuwar marainyar Allah, Yana kaiwa nan ya fara tafiya zuwa dakin Musaddiq, "In ka fasa Hilal, in ka fasa ka fada ka raina kanka, bazan mayar da wayar ba dan Allah in kana iyawa kazo ka zaneni, mara kunyan banza da wofi, Bayan Hilal Husna tabi tana fadin "sorry my PP, rabu da Anty gobe zan mayar mishi da wayar school, wani irin miyau ya hadiye mai daci a hankali yace " laifi ne dan inason gyara rayuwarta, girgiza kai tayi tace "a'a ya Hilal, in akwai irinka cikin rayuwarmu bazamu taba tagayyara ba, amma pls ka dinga danne zuciyarka, in kayi fushi kai kanka tsoron kanka kakeji, bana son ganin fushin.. gyada mata kai yayi ya murda dakin ya shiga hade cewa ta tafi ta barshi shi kadai.... A can daki kuwa Musaddiq keta rarrashin Nadeeyah wacce keta kuka sosai harda shashsheka tana fadin "walhi ban taba mishi magana ba, kuma ni bance ina sonshi ba, nima buri na inyi karatu mai zurfi, dan Allah Ya Musaddiq ka bashi hakuri, wallahi bazan kara ba.. Zaunar da ita yayi a gefen gadonsu, ya tsuguna a gabanta ya sa hannu yana share mata hawaye yace "karki damu, ranshi ne ya baci, duk tausayinki ne yaja hakan, Yasha fada min in dinga sa ido a kanki saboda maraicinki, Hilal na matukar son kiyi karatun da zai sa ki dogara da kanki, A iya sanina ban taba ganin abun da Hilal ya damu dashi ba bayan iyayenshi, sai ni, sai ke yanzu da kike son kwace min mishi, nidai bazan yarda ba, kawai kinsa ya daina damuwa dani, ko waya mukeyi ya dinga tambayata ke kenan, Dariya tayi sosai, yadda yayi maganar a shagwabe ya sanya ta manta duk wani kuncin da ya tokare zuciyarta, Murmushi yayi shima ya mike yaja kumatunta yace "haka nake so kanwata, karki kara zubda hawaye kinji? kai ta gyada mishi ya kashe mata ido daya ya juya zai fita a dakin, Ganin Badariyya yayi tsaye a bayanshi tana huci, wani irin kallo yayi mata hade da cewa "lafiya? Bata iya bashi amsa ba sai hawaye ya ga suna sauka a idanuwanta, mtswwwww.... dogon tsaki yaja ya bi ta gefenta ya bude kofar dakin ya fita, wani kololon bakin ciki ne ya turnuke Badariyya tayi ma Nadeeyah wani irin kallo hawaye na cigaba da ambaliya a idonta, Mikewa Nadeeyah zata wuce Badar ta janyo ta ta hankada ta baya, "uban me kukeyi a dakin nan ta fadi murya kausashe, Husnah da shigowarta dakin kenan tace "me ko sukeyi, *Soyayya* mana, baki san suna soyayya ba dama? ta fadi hakan ne dan ta tunzura ta, dan ta gane take takenta da dadewa.... aiko ta tunzuru, dan hauka ta fara yi, ta cakumi wuyan Nadeeyah iya karfinta tana fadin "wallahi saina kasheki, shakar da tayi mata ita ta hana ta ihu mai karfi, sai hawayen azaba da take fitarwa, Da Husnah taga ta kasa kwace Nadeeyah a hannunta kuma tana ganin take taken zata iya kashetan da gaske tace "na shiga uku, wallahi karya nakeyi, ki saketa Badar, inaa kesashshiyar zuciyar Badariyya bata ji bata gani wen it comes to Musaddiq, Da sauri Husnah ta fita tana ihu tana fadin "Zata kasheta, wayyo Allah Anty Raly kizo zata kashe ta, Wa za'a kashe? Daddy da ya shigo a lokacin ya tambaya a gigice, Husnah da kuka ya kufce mata ta nuna dakinsu tace Badariyya zata kashe Nadee---- kafin ta karasa fadi Hilal ya murda kofar da karfi har yana cire handle din kofar, lokacin da ya shiga kiriss ya rage Nadeeyah ta suma, dan idonta da ya jike da hawaye ya fara lumshewa, ita kanta Badar din kukan takeyi, amma zuciyarta ta ki bari ta saketa, dama wannan damar take jira, tsanar da tayi ma Nadeeyah mara misaltuwa ce, gara ta kasheta kowa ya huta, tasan hukuncinta kadan ne tunda bata kai 18yrs ba "a karancin iliminta na addini", Iya karfinshi ya sa ya janye Badar, yayi wurgi da ita jikin drawer dakin har saida mudubin drawer ya fashe, da gudu Musaddiq yayi kan Nadeeyah da ta durkushe tana tari dakyar, rungumota yayi jikinshi yana jijjigata, yana kiran sunanta da karfi saboda firgici...... Mrs Tijjani Shattimah...... [24/03 9:36 PM] Ummu Abdul 2: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 4⃣2⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Ganin yadda take lumshe ido ya sa Daddy cewa "kawo ruwa da sauri Husnah, rige rigen dauko ruwa sukayi ita da Anty Raly, A kidime Musaddiq ya bude bakinta yana hura mata iskar bakinshi saboda yadda jikinta ya fara saki, babu wanda a cikinsu ya ji, ko ya saurari irin dukan da Hilal yakewa Badariyya kamar Allah ya aikoshi, Tun tana ihu anaji har muryarta ta dashe, da gudu ta rarrafa ta rike kafar Daddy tace "dan Allah Daddy kace yayi hakuri bazan kara ba wallahi, finciko Hilal yayi yace "kin san Allah dama, belt din hannunshi har ya tattare saboda azabar duka, Badan tausayi ba, sai dan saboda muryarta ta ishi Daddy yasashi cewa "kyaleta Muktar! Badan yaso ba ya kyaleta yana yi mata kallon ban gama dake ba, a guje ta bar dakin tana ihun azabar haurin da yayi mata a baya, a kofar shigowa palon taci karo da Su Mummy, rungumarta tayi a tsorace tace "ke lafiya, meya faru? Kankameta Badar tayi tace "zasu kasheni Mummy, wayyo Allah bayana, kallon su Mami da Anni tayi tace "ku shigo ciki ku zauna, shigowa sukayi suka zauna, Mummy taja hannun Badar suka shiga dakin, Tsaye ta samesu dukkansu akan Nadeeyah da ta bude idonta tana maida numfashi, Belt din hannun Hilal ta kalla rai a bace tace "uban me tayi maka kayi mata dukan ficewar hayyaci, abin da ya kawoka gidan nan kenan, ya ilahi kayi min maganin yaron nan da duk in yazo gidana sai ya tayar min da husuma, wannan wace irin mas---- dakata min!! Daddy ya katseta fuskarshi a murtuke babu alamun wasa, Naji alamar zuwan baki, muje in samesu, da kaina zanyi maganin matsalar gidana, naji duk abin da ke faruwa tun zuwan Nadeeyah gidannan har kawo yau da idona ya gane min, "Nadeeyah, Mummy ta fadi a hankali, ta kalli Nadeeyar dake kwance har lokacin a jikin Musaddiq, Saida Daddy ya bar dakin ta tambayi Husnah abun da ya faru, yadda abin ya faru ta fada mata, ta sakaya mata ainihin abun da ya tunzura Badar, jiki a sanyaye ta fita a daki dan bata da mafita sai jiran hukuncin da Daddy zai yanke....
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156