Skip to content

Chapter 141

Chapter 141

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

maka wanka kazo muci duk abinda kake so, "Kallon Anty Saude yayi cikin fuskar mamaki yace "Momma ba kince ni zan dinga yin shower da kaina ba, ni dai ba wanda zai min wanka, "Yess big boy jeka toilet dina kayi wankanka, amma fa kar kayi min barna, kuma ka wanke kanka da kyau kaji? Gyaďa kai yayi ya nufi bayin da gudu bayan ya watsar da dukka kayanshi a parlon..... "Momma... wai meyasa har yan---- look Tee, Dan Allah kar mu fara wannan zancen, go and get urself ready kazo kaci abinci, kayi abinda kake so na kyaleka,, ka barni inyi abinda nakeso... Mun fara magana dakai akan Amal, zan kira Mus'ab anjima in sha---- Bai karasa jin abinda zata ce ba ya mike yayi hanyar dakinshi... Taheer lokaci yayi da bazan zauna in zuba maka ido ba, wallahi tallahi cikin kwanakin nan zakayi aure.... Dariya sosai yayi saboda yadda ta daga murya, bai waigo ya kalleta ba ya shige dakinshi yana cigaba da dariyar da yasan zuwar mishi kawai tayi babu shiri, Gefen katafaran gadonshi ya zauna haďe da dafe kanshi, "Ta ina zai fara sanarwa da Momma abinda ke ranshi, yasani sarai ko za'a haďi sama da kasa bazata yarda ya auri Nadeeyah ba, da yaya ma ta yarda da zamanta a gidan, saida ta gindaya mishi tsauraran sharudda akan Nadeeyah kafin har ta yarda da zamanta, Haihuwar junior da tayi ita ta sake samarwa da mahaifiyarshi kwanciyar hankali domin Allah ya daura mata son yaron... kishingida yayi yana tunano baya lokacin da ya fidda rai da samun muradin ranshi, Sai gashi kaddara ta haďasu a lokacin da bai taba zato ba........ *Tuna baya....* Suna isa asibitin ya fito daga motar dakyar, Mutumin da ya sasu a mota ya taimaka mishi suka shiga da ita saboda yanayinshi na buguwa da kuma jini da daketa zuba a kanshi, da sauri nurses suka iso garesu suka sanyata akan gado, Dishidishi Taheer yake gani saboda karfinshi ya kusa karewa, bayan nurses din yabi har zuwa kofar dakin emergency, suna gab da shiga ganinshi ya sauka a kan Nadeeyah da gefen fuskarta ya baci da jini, a firgice ya karasa kusa da gadon ya fara kiran sunanta yana kuka sosai, Dakyar mutumin da ya rakosu ya rabashi da gadon ya zaunar dashi a kan kujera, karfafa jikinshi yayi ya dauko wayarshi ya shiga neman number Anty Raliya, dakyar ya iya ganin number dan hankalinshi ya fara gushewa, Ya kira wayar yafi sau goma bata daga ba, cikin neman mafita yayi kiran uncle Kamal, ringing biyu tayi ya dauka, Cikin wahalalliyar murya yace mishi yaje gidan Alh Mukhtar kyari ya sanar dashi hatsarin da sukayi, Rashin sa'a akayi Kamal yace mishi yana hanyar dawowa daga Abuja, amma gobe da sassafe zai safe zaije gidan ya sanar musu, sunan asibitin da suke ya faďa mishi sannan ya kashe wayar dan gaba ďaya jijiyoyin kanshi sun daina aiki, Ba karamin tashin hankali kamal ya shiga ba na jin muryar Taheer, yana kashe wayar ya nemi *Comr-David* ya sanar mishi da halin da Taheer yake ciki sannan yasashi zuwa asibitin dan ganin halin da yake ciki... Kafin zuwan David har Taheer ya faďi unconscious, cikin kankanin lokaci shima aka bashi gado... Washe gari Yadda David ya ga jikin na Taheer ya tabbatarwa da Kamal suna cikin mayuwacin hali, ya kamata ya sanarwa Anty Saude saboda gudun bacin rana, Hankali a tashe Kamal ya a jiye wayar ya sake kallon masu gadin kofar gidan da sukayi bake bake suka hanashi shiga, Rokonsu ya shiga yi akan suje su fadama me gidan hatsari yarshi tayi, cikin halin ko in kula suka daka mishi tsawa suka tabbatar mishi babu kowa a cikin gidan... Rasa abin yi yayi gashi Taheer bai san inda yake ba, motarshi ya shiga ya koma gida ya soma shirin tafiya Lagos...... Yana isa bai bata lokaci ba ya kira Anty Saude ya sanar da ita, rikitashi tayi da kukanta tace maza ya shirya su taho nan zaifi samun kula, bai mata musu ba ya koma dakin da Taheer yake... Doctorn da take kula dasu doctor Marliyya batayi jayayya da Kamal ba tayi yan rubuce rubucenta ta bashi sannan ta shawarceshi da ya bari su farfado saboda komai ya tafi mishi cikin sauki, ta dade tana faďa mishi irin Halin da Nadeeyah take ciki, sannan ta faďa mishi tana dauke da karamin ciki, barinta ta farfaďo yana da matukar muhimmaci, Na'am yayi da zancenta ya gaza furta mata ba tare da Nadeeyah zasu tafi ba saboda kar taga rashin hankali da kyautawarsu..... Nadeeyah... Nadeeyah... Na-dee-yaaàaa.... ya furta da ďan karfi, da hanzari Kamal da David suka shigo dakin, Kwanta Uncle T, baka da karfi a jikinka, Alhamdulillah tunda ka farfaďo, dama na riga na yanki ticket 8pm jirgin mu zai tashi, "Where is Nadeeyah Kamal? Ya tambaya dakyar yana dafe kanshi.. She will be alright Tee, lafiyarka itace abin bukatarmu, i went to der house ance babu kowa, in na kaika gurin Anty safely zan dawo in sake komawa gurin yan uwanta, i promise u i will neva lv her alone Taheer, trust mee, Runtse ido Taheer yayi hawayen dake boye a idonshi ya sauka a kumatunshi.. "Ba babanmu daya ba, iyayenta sun rasu shine Daddynmu ya daukota ya dawo da ita gidanmu... "Gara kai Uncle, kana ganin Mahaifiyarka, ni fa bani da dukka, maraici ya kangeni gaba da baya, bamu da kowaaaaa.... Mikewa yayi dakyar bayan ya gama tunano kadan da ya sani daga labarin Nadeeyah... Cannular dake hannunshi ya cire ya fara tafiya dakyar zuwa Dakin da Nadeeyah take Kamal da David na binshi a baya... Ganinta da oxygen ya sanyashi zaman dirshan a gaban gadonta, kuka ya shiga rerowa mai sosa zuciya wanda komin rashin imaninka sai ka tausaya mishi, Dan Allah karki mutu Nadeeyah, Karki mutu ki barni da guilt din kashe abinda zuciyata tafi kauna, Dan Allah ki tashi... "Zata tashi ranka ya daďe, wata nurse ta faďa mishi cike da tausayawa, "Yaushe? Yaushe zata tashi?, Dan Allah ku tasheta---- "Calm down Taheer, tunda suka ce zata tashi she will be fine, ka tashi mu tafi, cikin raďa Kamal ke maganar, Wata gigitacciyar tsawa Taheer ya dakawa Kamal wacce ta sanya kanshi juyawa ya tafi tagaga, Tsugunawa Kamal yayi ya rukoshi yace "Meyasa kakeson wasa da rayuwarka, why Tee? Plss Kamal kasan yadda zakayi mu tafi tare da Nadeeyah, i will call her Aunt, in taji sauki zan dawo da ita, nasan ba karamin abu bane ya fito da ita da daddare da akwatinta, plsss Kamal, Yadda yayi maganar yana ambaliyar hawaye ya karya zuciyar Kamal, "Karka damu in shaa Allah zamuje da David muyi mata duk abin da ya dace... Nurse din dake tsaye a kansu tace "ku samu Dr Marli, she will help alot da report dinta, ba shine mijinta ba? N--- Yess nine yayi saurin katse Kamal, fine biyoni muje, in shaa Allahu ko gobe zaku gama mata komai, Taimaka ma Taheer sukayi ya koma daki tayi mishi allurai sannan suka wuce office din Doctor....... A daren da zasu tafi a daren Nadeeyah ta farfado, ba karamin farin ciki Kamal yayi ba dan yanzu kam zasu san inda wani nata yake dan wayar Taheer tun daren ranar

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156