Skip to content

Chapter 143

Chapter 143

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

share hawayenta, wayarshi ya dauka ya kira number mai gadin gidansu ya sashi ya duba ko Raliya na nan.. saida yayi kusan minti goma sannan ya kirashi yace bata nan amma ya samu number da take aiki dashi yanzu, cike da murna ya umurceshi da ya turo mishi, bayan ya turo mishi ya wuce daki dan kiranta, yana kira ta daga kamar dama tana jiran wayar, "Hello salamu alaikum, ameen wa alaiki salam mummyn Fadeel, ya gida? Cikin rashin sanin muryar tace "lafiya kalau ya harkoki, fine alhamdulillah ya faďi yana gyara zama, Taheer ne, in bazaki damu ba dan Allah ina son ganinki, Ayya Taheer ya su Anty saude, shikenan sai kuyi zamanku haka akeyi.. dariya yayi yace "Ba haka bane karatu ne ya rikeni, ina Fadeel? Gashi can yana wasa, yaushe zaka zo? Gobe da safe in shaa Allah, to Allah ya kaimu Taheer, sai kazo..... Washe gari suka hau jirgi zuwa kaduna, saida ya fara sauke su Amal a gida suka ci abinci suka huta sannan suka wuce gidan Anty Raliya... Basu sameta a gida ba saida suka jirata har na tsawon minti goma.. Ayi min afuwa Taheer, na kusa fara exams ne walhy, ban cika samun zam---- muryarta ta kakare saboda yin tozali da Nadeeyah da tayi, Mutsitstsika ido tayi haďe da sakin hannun Fadeel, Na---dee--yahh.... ta faďi cikin rawar murya, rau rau idon Nadeeyah yayi tace "Na'am Anty, kirji Raliya ta rike itama idanuwan nata suka kawo ruwa, "Nadeeyah, dama kina nan a raye? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, ina kika shiga? Kasa bata amsa tayi sai kuka mai karfi da ta fashe mata da shi, zama Anty Raliya tayi ta rungumo Nadeeya tana share hawayen farin cikin, Taheer ina ka nemo mana Nadeeyah, shekara ďaya da watanni kenan muna nemanta, an shiga matsaloli sosai na rashin ta, ashe tana nan da rai.. Alhamdulillah, Allah nagode maka da ka dawo mana da Nadeeyah cikin koshin lafiya, kankame Nadeeyah tayi tana shafa bayanta haďe da kukan farin ciki.... kushun kushun din yaro taji yana shirin fara kuka, hannun Taheer ta kalla taga ya daurashi a kafadarshi yana jijjigashi, kallon mamaki ta bishi dashi tace "Taheer kayi aure ne? Babynka ne? ina Mamanshi? Duk wadannan tambayoyin tayi su ne cike da zullumin kar yace mata Nadeeyah ya aura, tasan in hakan ne tabbas rayuwar kaninta na cikin hatsari.. Jin Babyn tayi a kusa da ita tayi saurin kallon Nadeeyah da ta fara kokarin bashi nono, dago kai tayi da sauri taga Taheer har ya fita daga dakin saboda ya bar Nadeeyah ta shayar da Babynta... Nadeeyah yaushe kukayi aure? Ya salam ta faďi haďe da dafe kai hawaye ya sauko a idonta... Daura mata babyn tayi a hannunta tace "Danki ne, jininki ne Anty, dan yaya Musaddiq---neeee.. ta karashe cikin kukan tunanin Musaddiq yayi mata nisa... Wata irin runguma Raliya tayi ma Junior ta dinga sumbatarshi tana zubar hawayen farin ciki, tabbas wannan jininta ne, komai nashi na mahaifinshi ne, wayyo Allah, wannan ita ake kira *Zazzafar Kaddara*, ina ma Musaddiq zai iya zuwa yanzu yaga gudan jininshi... kuka sosai ta dinga yi tana sambatu a fuskar Junior.... Mrs Tijjani Shattima..... [12/06 7:55 PM] fareedah: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣8⃣ By *Aysha Ya'u kurah* A tare suka waigo dan ganin wanda yayi wa kofar gidan haka kamar dama yanada haushin gidan, horn din da zubair yayi ne ya sanyasu manta batun kofar Hilal yaje ya bude mishi gate din.... Daya bayan daya sheik ya kalli su Papy da su Baffa, ganin har ya gama kallonshi bai dire idonshi kan yayarshi ba ya sanya shi tambayar inda take, Baffa da tun shigowarshi gurin ya ke kallon Sheik yana hasashen da ya tabbatar gaskiya ne, Daddy ne yayi karaff ya fara ma sheik nasiha da sigar tunatarwa sannan ya nuna Baffa yace wannan shine mijinta, wannan kuma danta ne, Allah yayi ma twin sis dinshi rasuwa, introducing kowa na gurin Daddy yayi mishi sannan ya karashe da cewa Nadeeyah is no were to be found, bamu samu gawarta ba shiyasa muka yarda da cewa she is alive, Baffa ne ya cigaba da magana bayan Daddy ya dire ya ba sheik labarin yadda rayuwar Atika ta kasance da yadda kullum bata da magana sai tashi, har ranar da zata koma ga mahallincinta saida ta ambaci sunanshi.... Kukan da sheik yakeyi mai sauti shi ya katse Baffa daga bashi labarin Atika, babu wanda ya hanashi zubda hawaye saima wadanda ke tayashi irin su Papy, Baffa da Maleekah, saida sukayi mai isarsu sannan suka fara tsagaitashi saboda nasihar da Daddy ya cigaba dayi, Labarin gararin rayuwar da Papy ya gani suka bashi wanda ya sake jefashi cikin mamaki da tsananin tsoron Allah, sosai Sheik yayi bakin cikin rashin sake ganin yayarshi, amma yayi murna matuka da ganin yadda zuri'ata ta yaďu gwanin ban sha'awa duk da baiga mutum biyu ciki ba, daya bayan daya ya shiga rungumarsu kamar zai maidasu ciki, farin cikin kasantuwa da yan uwa baya misaltuwa, a wannan rana sheik ya kira Hilal da alherin rayuwarshi, dan a sanadiyyarshi ne ya haďu da yan uwanshi na kusa, zuri'ar yar uwarshi da tasoshi matuka...... Masauki na musamman Daddy ya kamama Sheik da iyalanshi, a can ma saida suka raba dare suna hira kamar babu gobe.... Jamal da Ruwaida ne zaune kusa da Maleekah suna faďa mata yadda suka daďe suna kallon films dinta, cike da jindadi tayi musu alkawarin tafiya tare dasu domin kallon sabon film ďinta Saheebul qalbee, sun dade suna hira haďe da daukar hotuna, sai kusan 12 na dare suka fara shirin zuwa masaukinsu suma.. Har waje ta rakasu tana karewa kasar da bata taba zuwa ba kallo, Har motar su Papy ta bacewa ganinta bata koma ciki ba saima waje da ta fito tana zagayawa dan karewa arear kallo sannan ta jira ganin fitowar Hilal da ke can kasa yana ma Abbunta order irin coffeen da yakeso duk dare.... "Omoo see fine girl.. wani dan bayerabe ya faďi bakinshi kunshe da wiwi, dayan da gaba ďaya a buge yake yana kallonta dishi dishi yace "O boy i no see anything, kamo hannunshi yayi suka nufi inda take takunta day day hannunta rungume da kirjinta, rigar dake jikinta girmanta duka bai wuce gwiwa ba, sai dan karamin mayafi da ta ďaura shi akanta, Suna karasowa kusa da ita taji wani mugun warin da bata taba jin irinshi ba duk rayuwarta, da sauri ta matsa baya tana faďin "Ya subhanallah, sake matsota sukayi gadan gadan har suka samu sa'ar cafke hannunta, gaba daya yanayinsu kyama ya bata hakan yasa ta fara masifa cikin harcen larabci tana kokarin kwatar kanta, da taga sunfi karfinta kuma suna janta iya karfinsu ta saki wani ihu tana neman ceto, Shurun unguwar ya sa babu wani mataimaki a gurin sai Allah, kara karfin ihunta tayi lokacin da taga sun nufi wani lungu da ita, "Ya hayyu ya qayyum bi rahmatika astagithu.... hakan ta dinga faďi hawaye na fita sharrr daga cikin idonta... Full light aka saki wacce ta haska gurin da suke, basu saketa ba sai sa hannu da sukayi suna kare fuskarsu suna masifar dalilin haskasu, A haka Hilal ya bar motar ya fito da sauri ya nufi inda suke, ganin

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156