Chapter 55
Chapter 55
da yayi wasu yan mintuna sannan ya tashi hade da gamsar da zuciyarshi koma meye in Anni tazo zata warware mishi komai.... Ita kuwa Goggo safa da Marwah ta dinga yi a daki tana tunanin ta inda wannan mutumin ya fito, tasan a hannunta saifu ya cika, kuma a gabanta aka binne shi, anya ba aure Baffa yayi ba lokacin da yake tafiye tafiyenshi, katse mata tunani yayi yace "Ma'u wannan yaron ko dai dan Hardejo ne, kodai..... saurin katse shi tayi murya a kausashe tace "ko kuma naka ba, ni zaka ciwa Amana Muhammadu,? ashe dama kayi aure a boye ban sani ba, "Nan jikin Baffa ya fara rawa yace "wallahi banda Atika ban taba auren wata mace ba, daga ke sai ita, kwafa Goggo tayi cike da masifa tace "gaskiya zatayi halinta ai gobe, da bana son yaron nan ya dawo gidannan amma gobe da kaina zansa Hafeez ya kawo shi dan a warware min wannan kullin, ina ganin watan jin kunyarka ne ya tsaya, saboda sanin yana da gaskiya shiyasa yace "Allah ya kaimu, komawa yayi ya zaune a zuciyarshi yace "shi yaushe ma ya kalli wata mace a matsayin mace har ya aureta, har yanzu gani yakeyi duk duniya babu macen da ta kamo kafar ma'u a komai, sauran mata duk kallonsu yakeyi kamar gumaka, tsaki yayi yace "Ma'u batayi mishi adalci ba, tasan bazai taba cin amanarta ba, amma babu komai gobe gaskiya zatayi halinta... Haka suka kwana dukkansu zuciyoyinsu ba dadi, kowa da abun da yake sakawa a ranshi, har gari ya waye Baffa bai bar hango fuskar Abdallah ba..... **********●●●******* Karfe biyu da rabi suka iso kaduna, Hotel din da su Papy suka sauka can Badamasi ya wuce dasu, bayan sun huta a masauki suka ci abinci sannan ne Mami ta tambayi Papy dalilin zuwan nasu, bai amsa ta ba saboda yaga Anni ta dan kashingide tana son tayi bacci, Ruwaidah ya daura akan cinyarshi yace "me Mamana tayi miki jiya kika duketa, irin kukan nan da tayi nasan ba karamin duka kikayi mata ba, Harararta Mami tayi tace "ai badan Anni ba walhi da sai na balla hannunta sai ayi dauri, kaga daga nan ma huta da barna, turo baki Ruwaidah tayi hade da tura kanta cikin kirjin Papy, "ni kike turowa baki,? mami ta tambaya tana nuna kirjinta da yatsa, a ina ta turo miki baki, ki kyalemin uwata ta huta, shikenan dan bana nan bazatayi abin da takeso ba, Mikewa Mami tayi tace "ko kai da kana nan sai ka tayani, man gyada na zaune cikin jarkarshi ta dauko tukunyarta ta wasan yara wai zata soya dankali, tasan jarkar tafi karfinta haka tasa karfi ta yar da ita kasa, gaba daya kitchen da store babu inda bai samu albarkar mai ba, "tabbb... ai Mami kin ma mata da sauki, da kin cire hannun ne sai a sa mata na roba.. harara Papy ya jefa gefen da Jamal ke zaune yana latsa waya kamar bashi yayi maganan ba, "shikenan dan ta zubar da mai sai a duke ta, ba koyon girki takeyi ba, in bata koya ba waye zai dinga tayaki aiki, "Na yafe Mami tayi saurin fadi tayi hanyar bayi tace "ka cigaba da shagwaba yarinyar nan, ta riga ta maida mu kamar kakanninta, bayan Ruwaidah Papy ya shafa yace "rabu da Mami kinji, zan siyo miki kayan abincinki ki koya da kanki ki dinga dafa min inci kinji ko? Gyada kai tayi tace "kuma bazamu samma Yaya Jamal ba, dariya papy yayi yace "eh mana wama zai bashi, yaje can yaci jagwalgwalon Mamin shi, dariya sosai Jamal yayi yace "opposite, Kuma in na kara ganin kin taba ma Mami ko da gishiri ne sai na yanka hannun da wuka, murguda mishi baki tayi tace "ni da Papy zai siyomin nawa me zanyi da naku, ko kitchen din mami ma bazan kara shiga ba, "yauwa Good Girl, muna komawa zan yi miki cefanenki, karki kalli kayan Mami sun tsufa, mikewa Jamal yayi yana dariya yace "har abincin Mami ma kar ta kara ci papy, ta dafa nata da kanta, dakuwa Papy yayi mishi ya fita daga dakin yana dariya.... Suna idar da Sallar la'asar Papy yace su shirya zasu je wani guri, manufar shi nakin fadawa Anni shine kar ya fada mata suje bashi bane hankalinta ya kara tashi, gara in suka je yaga bata sanshi ba sai su tafi ba tare da ya daga mata hankali ba, tun yana shekara bakwai ya yankewa kanshi daina matsa mata akan maganar mahaifinshi, domin ya kan ganta cikin tsananin damuwa duk ranar da yayi mata maganar, a irin yadda ya taso yaga ta wahala akanshi shi yasa baya san ganinta cikin damuwa ko kadan... Biyar saura suka isa kofar gidan, motar Mummy Hafeez ya gani a cikin gidan, Addu'a ya fara yi zuciyarshi na Allah yasa kar su hadu su wulakanta bayin Allahn nan, gabanshi bai tsananta faduwa ba saida ya jiyo muryar Radiya, farin sani yayi mata akan rashin mutunci, dake wa yayi ya karasa ciki dasu, Sallama sukayi dukkansu suka shiga cikin gidan, daga cikin daki sukaji an amsa Sallamar, mikewa Goggo tayi ta fito dama zaman jiransu take, tana fitowa idanuwanta suka sauka kan Anni, baya taja kamar zata fadi bakinta na rawa tace, H-an-ne....... Mrs Tijjani Shattima..... [18/03 8:06 AM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣9⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Kallon rashin sani Anni tayi mata dan bata gane fuskarta ba, nan dai ta fadada murmushinta tace "Na'am barkanku da gida, dafatan mun sameku lafiya, Goggo dake tsaye jikinta na rawa kamar mazari tace "lafiya lau, matsawa tayi gefe tace ku shigo ciki, tabarmi Mummy ta fito dasu tace "a'a Goggo bari su zauna a waje yafi iska.. Bayan sun zazzauna an gaggaisa, Goggo ta kalli Hanne kirjinta na duka uku uku tace "baki ganeni ba ko Hanne?, gyada kai Anni tayi tace "ban ganeki ba, gyara zama Ma'u tayi kishi ya motso mata ta fara charge ta kalli Papy tace "wannan ce mahaifiyarka?? Eh!! Papy ya fada yana mai jin dadin an gane mahaifiyarshi a gidan, "TABDIJAM Goggo tace "tana kallon Anni, Wato Hanne ke kika haifeshi,? wannan karan mamaki yasanya Anni cewa kwarai ni na haifeshi, dana ne, lafiya?? Idon Goggo ya rufe ta manta da yara a gurin tace "wato dama cikin shegen da kika dinga yawo dashi a tsakanin jalingo da Gembu dama Mijina ne yayi miki shi, kenan lokacin da nake tausayin ki in su Harira suna tsangwamarki ashe kallon sakarya kike min mijina ne ya kunsa miki, kallon Radiya tayi tace "maza tafi shagon Gidado ki kira min Baffan ku, kafin Radiya ta mike Baffa ya shigo gidan da sallama, yana ganin wucewarsu ya mike a shagon Gidado hade da amso musu lemu, Goggo sam bata basu damar amsa sallamar ba tace "yauwa gara da Allah ya kawo ka, nuna Hanne tayi tace ka gane wannan,? kallonta yayi yaga samm shi bai taba ganinta ba, ita kuwa Anni kallo ta bishi dashi idonta ya ciko da kwalla tana fadin Alhamdulillah, Alhamdulillah, zama Baffa yayi yace "ban santa ba, wacece ita? Tafa hannu Goggo tayi tace "yau ni naga Bariki, Hannen ce baka sani ba? Hannen gidansu Inna wuro kanwar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156