Skip to content

Chapter 15

Chapter 15

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

matukar tausaya musu, duk da irin wadatar abincin da suke samu baisa su walwala ba bare har su kai ga cinshi cikin jin dadi, A cikin kwanakin Mummy tayi bajinta matuka, ta manta duk wani girman kai nata, sai ma tsananin tausayin yar uwarta, A wannan lokacin ne Daddy da Musaddiq da duk wasu makusantansu suka san lallai jini daya ya wuce wasa, yaran mummy ma sunyi bajinta matuka daga su har mazajensu, sam mummy bata ba kowa kofar da zaiyi complain ba.. A cikin kwanakin kullum ta koma gida a tsorace take, Jikinta na bata kamar zata iya rasa wani makusancinta lokaci daya, ( Nidai nace Allah yasa wannan canjin ya daure).. Bayan an watse adduar bakwai kowa na shirin tafiya gida, mummy ce ta shigo daki ta zauna gefen gadon da mama suwaiba take, cikin Nasiha tace "suwaiba ki kwantar da Hankalinki, kiyi tawakkali, Allah ya fiki san Adamu, kuma ya karbi abinshi, dan Allah kar kiyi abin da zai sa ya'yanki su cutu, domin yanzu ke kadai kika rage musu, dan Allah suwaiba ki rage tunani, ga kayan abinci nan na hadesu guri daya, na bawa Nadeeyah mukullin, gyada kai mamma tayi idon nan yayi ciki ciki, tace "Mun gode mummy Allah ya bada lada, Allah ya biyaku da gidan aljann----- bata karashe ba kuka mai karfi ya kwace mata, Hakuri su mummy da sauran matan dakin suka shiga bata suna tayata sharar kwalla, nan fa kuka ya rikide ya zama tari mai karfi, tun tana tarin da sauran karfinta har takai ga ta fara tarin jini, a gigice mummy ta fito tana kiran sunan Hafeez.. Hafeez na kofar gida yana sallamar baki shi da musaddiq suka jiyo ihun mummy, suka ruga cikin gidan a guje, a rude mummy tace "maza ka fito da mota Hafeezu mu tafi asibiti Suwaiba Aman jini takeyi, fito da ido waje Hafeez yayi cikin firgici yace "aman jini? eh mummy ta fadi tana turashi cikin dakin, Daukota yayi cakk ya fito da ita waje yana fadin dan Allah mamma kiyi hakuri, karki tafi ki barmu, gurin motarshi ya nufa da ita musaddiq ya bude baya aka shimfideta, gefe Nadeeyah ta shiga idon nan a kafe babu ko digon hawaye, zafin da kirjinta yakeyi ba mai kwatantuwa bane a wannan lokacin, motar Hafeez yaja da karfi suka nufi Asibiti mafi kusa. Da isarsu Hafeez ya sauka ko key bai cire ba ya fara kiran nurses, gadon emergency aka gunguro aka shimfideta a kai, gungurashi ciki suka fara yi da sauri sauri, da kyar kalmar salati ke fita a bakin mamma, babu wani sauran karfi a tattare da ita, komai nata ya riga ya gama sakewa, da karfi ta cakumo hannun Nadeeyah wacce take tayata salati ta hada da na Hafeez, idanuwan nan nata dakyar take iya budesu, "Ka rike min su Amana Hafeez, dan Allah ka rikesu, nasani kai me rauni ne Hafizu, abu kadan ke juya kwakwalwarka, na rokeka kar ka barsu suyi kukan rashin mu, na yafe maka, kuma mahaifinka ma ya yafe maka, ta juyo da kallanta gurin Nadeeyah da idonta ya kada sosai tace "Nasani Zainab nada nagartacciyar uwa, basai nace komai ba! Allah ya albarkaci rayuwarki, kiyi Hakuri da rayuwa Nadeeyah, ina matukar alfahari dake tun daga haihuwarki har kawo yau, Allah ya cigaba da taimakonki a duk halin da kika tsinci kanki, hannu Nadeeya tasa ta rufe mata baki tace "mamma babu abin da zai sameki in shaa Allah.. Dakin emergency aka shiga da ita aka ce su jira a nan likita zai shiga ya duba ta, kuka sosai Hafeez da Musaddiq keyi, Nadeeyah ce kadai tayi karfin halin yin addu'a, minti talatin da shigar doctor su mummy suka shigo, kafin su karaso doctor ya fito fuskar nan cike da damuwa, Kallon Hafeez yayi nan take zuciyarshi ta karye yace "am sorry, she is no more!! zuciyarta ta kai awa daya da yin collapse, yanzu ta daina aiki kwata kwata.. wani irin ihu Mummy ta saka wanda ya razanar da daukacin mutanen asibitin... Juyayi kwakwalwar Nadeeya ta shiga yi, a can cikin kanta take jin kalmar "she is no more, baya ta fara ja tana ganin mutane biyu biyu, kukansu sai juya kwakwalwarta yakeyi, batayi aune ba sai jinta tayi jikinta ya saki bata da wani sauran karfin da jikinta zai dauketa, sulalewa tayi saura kadan ta kai kasa, Cikin zafin nama ya karaso gurin ya riketa, babu wanda hankalinshi yake kanta, kowa kuka yakeyi babu kakkautawa, suma shigowarsu gurin kenan don daga airport asibitin suka wuto saboda Raliya ta fada musu halin da ake ciki.. Sunan Doctor HILAL ya fara kira da karfi hade da dagata ya rike a jikinshi, nan take hankalin masu kukan ya dawo kansu, wani daki aka shigar da Nadeeyah aka kwantar da ita a kan gado, hannunta Hilal ya rike yana murzashi da karfi yana kiran sunanta, koda doctor ya shigo Hilal na zaune a gefen gadon yanata bubbuga hannun, magana doctor yayi mishi yace ya tashi ya dubata, mikewa Hilal yayi ya koma kusa da su Papa ya harde hannunshi hade da jingine kanshi a bango, zuciyarshi ta karye matuka, da ya iya yi ma damuwa kuka da irin kukan da zaiyi ba mai misaltuwa bane, sai dai shi sam kuka baya daga cikin jerin abinda ya dauka me yaye damuwa, dan in yaga mutum na kuka har mamaki abun yake bashi. Minti kalilan doctor yayi a kan Nadeeyah ya fita bayan ya sanar musu shock ne yasa ta faduwa, amma in shaa Allah nan da awa daya zuwa biyu zata farka... Dakin gawar suka koma, kuka ya dawo musu sabo, Zuwan Daddy ne ya sanyasu cikin hankalinsu da nasihar da yayi musu, sannan yasa aka dauki gawar a ambulance suka wuce dan yi mata sutura.... ( *ALLAHU AKBAAR* Haka rayuwar ta gada, mutuwa na daya daga cikin abubuwan da muka debo na daga rayuwarmu, akwai masu rasa biyar lokaci daya, kuma badan Allah baya sansu bane, sai dai dan musan mutuwa ta zama dole, dukkanmu zamu dandanata komin daren dadewa, Allah ya kara mana hakurin rashin da mukayi dukkaninmu, kuma yasa mu cika da kyau da imani) Ameen ya Allah Mrs Tijjani shattima... [04/12 09:50] Meela Adeel: ZUMUNCINMU A YAU By Aysha Ya'u Kurah 1⃣7⃣ Ba gidan mutuwar ba, har unguwar su Nadeeyah sai da ta sake hargitsewa da koke koke, duk rashin imanin mutum sai ya zubar da hawaye saboda tausayin rai... ana sauke gawar, kofar gidan ya sake dinkewa da mutane.. A sanyaye Zainab ta shigo gidan, dama dakyar taje islamiyya a ranar, Hafeezu da kanshi ya kaita saboda tirjiyar da tayi, sai da ya sai mata sweets sanan ta yarda suka tafi.. mummy ta tarar a zaune tana kuka kamar ranta zai fita, duk sauran yaran na kanta suma suna sharar kwalla, dakin mamma tazo shiga da sauri, bin bayanta Husna tayi dan ta hana ta shiga, kafin Husna ta karasa zainab ta isa cikin dakin, kwance ta samu Mamma a rufe cikin likkafani, a gigice ta karasa jikinta, girgizata ta shiga yi tana fadin Mamma me ya sameki? meyasa naga suna ta kuka a waje, duk da karancin shekarunta tasan menene mutuwa domin tun rasuwar mahaifinta tasan mecece kalmar, kuma ta fahimci in mutum

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156