Skip to content

Chapter 26

Chapter 26

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,197 words 0 views Progress saved
Download Book

wa aka kashe? Ke ko Ma'u baki bani gurin zama, duk irin gajiyar nan da na kwaso ki barni a tsaye, Tsaff ma'u ta gano manufarta, taja hannunta tayi hanyar sakarkari da ita, saboda tsaho irin na ma'u tsaff ta hana haire damar waigowa, Labarin abin da ya faru ta fada mata hade da cewa "yanzu Hardejo yasa a dauke gawar yaron ayi mata sallah, dan ance saurayin musulmi ne, kuma ya wakilta wani yaje can tsaunin ya nemo inda yan uwanshi suke a fada musu, cike da damuwa Haire tace "ni yanzu yar buduwar nake tausayi, dan shaho na can ya tashi hankalin gari, kuma yace duk wanda ya dauketa ya boyeta in dai ya samu labari sai ya hallaka shi, kinsan shaho, a wala hore na,, duk dakiya irin ta ma'u saida cikinta ya dauki kugi saboda yadda take jin labarin shi tun zuwanta garin da aure ya kawota,, magana ta fara yi jiki a sanyaye tace "Haire am kinsan babu abinda zan boye miki, gyada kai Haire tayi tace "nasani ma'u, yauwa tace tana mai gyara tsayuwa, ta kwashe yadda akayi Baffa ya kawo yar makka gidan da kuma amfanin da take ganin yar makkan zata yi mata, ta karashe da fadin duk irin kokarin da zanyi in ga na samu wani abu a gurin iyayenta da ita zanyi, sannan kema bazan barki a baya ba, rabawa zamuyi daidai in kin yarda zaki rufa mana asiri, Ajiye kwarya Haire tayi ta zauna tana washe baki tace "wannan ai karuwar mu ce duka, ke ni har na fara hango ni a kasa mai tsarki, yadda su Hardejo suke fadin kasar ace muma gamu a cikinta, shewa sukayi dukkansu Ma'u tace "ai kaff kauyen nan sai sun dawo yi mana bauta, ke dai ki bani hadin kai mu samu abinda muke so, yanzu bari kiga sarkar da na dauke mata na hadata da tarkacen tawa, "aiko dakko ta mu gani, kin gani, ashe dai dama gaskiyar Hardejo da yace musulunci dadi gareshi, gashi nan cikin kwanaki kadan da karbarshi mun sami damin arziki, dariyar murna ma'u tayi ta wuce daki inda take jiyo kukan boddo, rashin ganin Baffa a dakin baisa ta kawo komai a ranta ba, ta dauki Boddo Halima ta duba gurin da ta ajiye sarkar taga wayam ba komai, dube dube ta farayi a gefen da tayi ajiyar, nan ma bata ga komai ba, a kidime ta fito da sauri tana kiran sunan Baffa, Rashin ganin bakuwar a inda ta barta ne ya kara daga hankalinta matuka, bayin gidan ta duba ko tana ciki, nan ma taga wayam babu kowa, gurin Haire ta koma jiki a sanyaye tace "Baffa ya dauketa a gidannan, dama yace zai koreta na hanashi, shine ya faki idona ya aiwatar, shi tsoro gareshi, daya barni da shaho ni nasan yadda zanyi inyi maganinshi, yanzu gashi ya janyo min asarar sarkar gwal da kyautar da iyayenta zasu mana in sunzo daukarta, Cike da kunan rai Haire da ta gama hango kanta a wata duniyar tace "amma Baffan Bingel bai kyauta mana ba, badan sunan annabin Hardejo gareshi ba da sai inyi kokwanton amsar musuluncin shi, tunda ai addinin Hardejo yace mu sowa dan uwanmu abin da muke sowa kanmu, jugum dai ma'u tayi tana bawa Boddo nono, tunanin ko ina mijinta zai kai yar Makkah ne ya cikata ya hanata magana..... Shi kuwa Baffa jin hirar da sukeyi da Haire ne ya sashi dauko sarkar da rigarta ya rufe mata fuska hade da kamo hanunta suka fita a gidan, Hanyar gidan yayanshi Hardejo yayi, duk wanda ya gansu a hanya sai yayi tunanin Ma'u ce, wasu a ganinsu wani abu ne ya faru ta rufe fuskarta take kuka, babu wanda ya ganeta kasancewar ma'u ma fara ce sosai, saidai farin nasu ba iri daya bane.. A kofar gida ya samu Hardejo yana koyar da samari karatun Allo, can ciki ya shige gurin matan shi, aiki ya samesu sunayi dukkan su a tsakar gidan, dakin uwar gidan ya shige kai tsaye tare da ita, ganin su a haka ya sa uwar gidan cire hannu a aikin ta wankesu tabi bayansu dan jin ko lafiya taga Ma'u haka, A tsaye ta sameshi yana safa da marwah a cikin dakin, yana ganinta yace "yauwa me babban suna, dama ke nake jira, taimakona nazo kiyi, zama tayi kusa da budurwar da take tunanin ma'u ce, tace "me ya sameki ma'u? Zama yayi daidai kafarta ya bude fuskar budurwar yace ba ma'u bace, bakuwa ce wacce rayuwarta ke cikin hatsari, labarin abinda ya faru kaff ya kwashe ya fada mata har dalilin da yasa ya kawota gurinsu, ya cigaba da fadin "nasan Shaho bashi da karfin da zaizo gidan nan yace zai dauke ta ko ya mata illah, gata nan zan bar miki ita, domin Allahn Hardejo ki kula da ita har iyayenta suzo daukarta,,, A tsorace Aisha (mai babban suna) ta kalli budurwar tace "a wani gari take? Inafa zan san daga inda take, Baffa ya fadi cike da zullumi, gyara zama tayi tace "to babu matsala, na samu labarin abinda ya faru sama sama dazu, Kuma naji ance malam ya tura aje a dauko gawarshi mutanen shaho sun hana sun zauna jiran dawowar budurwar ko wanda zai dauki gawar, cike da tausayawa ta kalli budurwar tace "ya sunanki, Baffa yayi dariya yace "ai bata jin komai, larabcin kadai na lura take ji, da yake Aisha ta dade cikin musulunci, babanta babban malami ne a jalingo, kuma sanadiyyarsu Hardejo ya musulunta har aka bashi aure, tace "maa ismuki ya ukhtee... cike da jin dadi budurwar tace "ATIKA " *ATIKA SHEIK SAHEEB SAIFUDDEEN* Juya sunan Baffa yayi tayi yace "kai ilimi akwai dadi, yanzu kinga sai musan labarinta ta dalilinki mai babban suna.... Mikewa Aisha tayi tace "bari in kawo mata abinci taci sai tayi sallah, kaga magariba ta kusa.... Bayan sallar isha'i kowa ya nutsu a gida, kuka da karai kainin shanaye kadai ke tashi a cikin gidan, matasa da yaran gidan duk suna zaure suna daukar karatun dare, yayin da wasu daga cikin malaman hardejo suka wanke gawar Habeeb da suka samu daukowa da kyar, hade da suturceta kamar yadda hardejo ya koya musu... Zaune yake cike da damuwa ya zurawa abincin gabanshi ido, "mutanen kauyen nan har yanzu imani bai gama ratsasu ba, duk irin fatawar nan da ake badawa bazai sa su hankalta su saduda ba, Hannu yasa a sama yace " *YA ALLAH DUK WANDA ZUCIYARSHI TAKE A KESASHE BATA DA NIYYAR RUSSUNAWA KUMA BA MAI SHIRYUWA BACE YA ALLAH KAYI MANA MAGANINSU DA GAGGAWA* AMEEN suka amsa dashi dukkansu, Adduoi yayi sosai akan duk abinda zai zamto barazana akan alummar musulmi Allah ya kauda shi.... ****** Cikin Harshen larabci take bawa Aisha da Hardejo labarinta... Sheik Saheeb Saifuddeen shine sunan mahaifina, dan asalin kasar cairo ne, babban malami ne kuma dan kasuwa wanda ake ji dashi a egypt.. Ummuna ta rasu shekara shida da suka wuce gurin haihuwar kanina, ummuna mahaifinta dan cameroon ne, mahaifiyarta ce yar cairo, kasancewata babba gurin mahaifina yasa yake ji dani fiye da kowa,, Tun bayan rasuwar mahaifiyata aka aura mishi kanwarta Ummul khair saboda ta kula da kanina, tun daga lokacin rayuwa ta fara sauya

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156