Skip to content

Chapter 112

Chapter 112

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

da ka koyamin sonka zaka bullo da cin mutunci a gareni, why Yaya Musaddiq? Hawaye ne ya zubo a idonshi amma zuciyarshi sam bata karaya ba yace "I will free u, kije ki auri wanda kike ganin zai fini baki kwanciyar hankali, Toshe mishi baki tayi da hannunta haďe da shigewa jikinshi tana kuka sosai.. "Dan Allah kayi hakuri, don't separate urself from me, plss.... Su Mummy dake tsaye a bayanta tun jin kararta na farko suka dawo cikin gidan ta fashe da kukan munafurci, Shigowa kitchen tayi ta kashe gas din da ruwan ya kusa kafewa tace "Bana san rabuwarku, bansan me yasa kika tsaneni ba Nadeeyah, har kika kai ga zagi da cin mutuncina, har kina nuna min cewa ke ba son ďana kikeyi ba a idona, wace uwa ce zata juri wannan, waye yake zuga ki? Waye shi inje inji dalili, Dama harzuka Musaddiq din tazo yi aiko ya harzuka, nan ya fara zagin Nadeeyah, zagi na cin mutunci wanda a iya saninshi bai taba yinshi ga wani ba, da taga ya tabo inda bazata iya jurewa ba ta share hawayenta ta fara maida mishi, nan kitchen din ya gauraye da tashin hankali, su Raudha da Radiya suka shigo suka haďu akan Nadeeyah, Ganin har lokacin Musaddiq yaki furta kalmar saki ya sanya Mummy rike hannun Nadeeyah tace "A idona kike cin mutuncina da 'yayana, "a idonki 'yayanki ke cin mutuncin iyayena, kin hana su?, Rashin kunya sosai ta zubawa Mummy wanda dama shiryayye ne sun san dashi, kafin ta rufe baki Musaddiq ya daka mata tsawa haďe da furta kalmar saki cikin rashin sani da tsananin bacin rai, Yana furtawa Anty Raudah ta jashi waje dan ma kar kukanta ya karya mishi zuciya, cikin mota ta tura shi tace ma Faida taja shi su tafi...... Tafawa sukayi haďe da sakin tsalle, "zo "zo "zo Badariyya, akwai sauran rina a kaba, kalli ki gani... Hoton Faida ta nuno mata suna zaune cikin mota tana rarrashinshi cikin kwarkwasa, Kallon marakisiyya tayi cikin tashin hankali tace "Ya zamuyi da wannan?, "Ina zuwa Marakisiyya ta faďi haďe da mikewa, da dan gudu tayi dakinta ta dauko wata allura da naďin laya, duk abun nan da sukeyi a idon Yareemah Suhail, jiransu yakeyi su gama ya tarwatsa aikin sannan ya kwace duk wani sihiri da Marakisiyya ta mallaka, Shiryayyen shiri sukayi ma Faida wanda zaisa gaba ďaya taji Musaddiq ya fita a ranta kuma ta faďa mishi duk irin shirin da sukayi dan rabashi da Nadeeyah, ma'anar hakan shine Badariyyah naso in ta koma ya zamana ita kaďai ce wacce zata dinga kula da shi, dan tasan zai tsani Mummy da tayi mata zagon kasa da sauran yan uwanshi, sun fi awa hudu suna aikin kafin su iya samun nasarar aikawa gurin Faida da har lokacin suke tare da Musaddiq, Wani abu ne taji ya soketa wanda ya sanyata dauke hannunta daga kan kafaďunshi, a lokacin shi kuma wasu zafafan hawaye suka shiga fitowa da cikin idonshi, tausayinshi ne ya ratsata taji bata kyauta ba da ta raba shi da matarshi sabon aure, tasan yadda yakeji saboda tana ganin yadda masoya sukeyi a film, sannan ta tuna da rabuwarta da masoyinta Zubair wanda iyayenta suka hanata aurenshi saboda bashi da kudi, "Kayi hakuri Musaddiq, kwantar da kanshi yayi kan sit ya fara kuka mai sauti, "kamar wacce aka tsikara ta fara faďa mishi abubuwan da suka shirya tun kafin aurenshi da Nadeeyah, har zuwa na yau bata rage mishi komai ba, har marin da Nadeeyar tayi mata sannan ta karashe da cewa is not late Musaddiq, Kaje ka dawo da matarka, dan bazan boye maka ba, zaiyi wuya ka samu mace irinta mai kawaici da hakurin shanye abubuwa... Tunda ta fara magana yake mata wani irin kallo na mamaki, tana kaiwa aya ya dubi agogon hannunshi, biyar saura ya gani, bai tsaya bata lokaci ba saboda bashi da ishashshen lokaci yayi saurin cewa "Muje gida plsss, tada motar da sauri, Revrse tayi ta ja motar da gudu kamar zata tashi sama, burinta ta isa akan lokacin domin shirinsu na su koreta ne sai suce ita ta tafi da kanta bayan ta zazzagesu, wayarshi ya dauka ya dinga kiran Nadeeyah yaji wayar a kashe, dangwarar da wayar yayi haďe da dafe kanshi yana ta hango wautarshi, magiyar da ta dinga mishi ya ke tunonowa., runtse idonshi yayi sosai hawaye na artabu a cikin kwayar idonshi, "Me ya sameni,? ya furta a hankali kamar me koyon magana, Faidah da itama ta rasa abinda yake mata dadi cikin ranta tace "Babu, influence din mu, plss forgive me, am going outta ur life yau dinnan.... Suna isa kofar gidan ya buďe kofar tun kafin ta tsayar da motar, wani irin turi yayi ma gate din ya bude dukkanshi, gudu gudu yayi ya shiga ciki, Tun a harabar gidan yake jiyo shewar su Anty Raudha, bai bi takai ba dan shi burinshi daga ya shiga yayi tozali da Nadeeyah, suna jin an turo kofar sukayi gumm suka koma gurin Mummy suna danna kafaďunta suna bata hakuri, Taku uku yayi ya hau sama ya murďa kofar ďakin da karfi, jin karan ruwa a bayi yasa shi sakin ajiyar zuciya haďe da maida numfashi, matakin da ya shirya dauka akan yan uwanshi da mahaifiyarshi mai karfi ne, dan kiriss ya rage su rabashi da abunda yake jin so a yanzu fiye da komai a rayuwarshi, bayin ya nufa da sauri ya murďa haďe da sakin fuskarshi, ganin bata cikin bayin yasashi fara dube dube yana kiran sunanta, kayanta dake cikin dakin ya duba yaga wayam ba komai sai kamshinta dake manne a gurin, da sauri ya koma daya dakin dan duba ko tana can tana kwashe sauran kayanta, nan ma babu ita sai tsirarrun kayanta, faďin irin tashin hankalin da Musaddiq ya shiga a wannan lokacin bata baki ne dan kuwa babu inda a jikinshi baya rawa yana dube duben inda zai ganta, Kasa ya sauko da sauri yana kwala kiran sunanta, matsowa kusa dashi Anty Radiya tayi tace "Ka bar neman wacce ta mari mahai----- Don't u dare... ya faďi da karfi wanda ya tsorata dukkaninsu, wani irin yanayi suka gani akan fuskarshi wanda basu taba sanin akwaishi tattare da kaninsu ba, bai dauke idonshi a kanta ba yace "Ina Nadeeyah? ja da baya Radiya tayi dan ga dukkan alamu Musaddiq na iya dukanta domin yadda idanuwanshi suka canza launi jijiyoyi suka mimmike akanshi, "Ta tafi Musaddiq, nasan batayi nisa da gida ba, zo muje mu nemota kafin lokaci ya kure... kallon mamaki su Radiya suka bi Faida dashi, basu iya furta komai ba har suka bar parlon.. Duk inda ya kamata su duba sun duba basu ga Nadeeyah, gaba ďaya hawaye ma Musaddiq nemanshi yayi ya rasa saboda tashin hankali, gidan Hajiya Zubaida nan suka je a karshe bata can, duk tashoshin kusa saida suka duba basu ganta ba, ko wayarshi dake ta ringing bai duba ba bare yasan wanda ke kiranshi... Sake kiranshi Hilal yayi a karo na goma sha hudu har lokacin Musaddiq bai dauka ba, Zubair ya kira a waya yace "yazo ya daukeshi a airport bazai gane gidan ba, ya kuma rokeshi da yayi sauri dan tun jiya hankalinshi yaki kwanciya, Minti

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156