Skip to content

Chapter 38

Chapter 38

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

da babu mai zuwa gurin, kuka takeyi sosai hade da karatun qurani, tasan in har ba'a ganta ba to tabbas baza'a daura mata auren ba... Zufa Baffa ke sharewa yana fadin "ina tace miki zata, kukan munafurci Ma'u ta kirkiro tace "bata fada min ba, nidai naji Leemah na cewa Suwaiba tace "in aka mata aure saita kashe kanta, salati Baffa ya saki yana fadin yarinyar nan so takeyi ta kunyata ni, duk irin mutanen da muka tara a kofar gidannan so takeyi lallai sai na kunyata, Matsowa kusa dashi ma'u tayi tace "tunda tace bata sanshi a hakura mana, Wani kallo baffa yayi mata yace "so kikeyi in zama karamin mutum, kinsan adadin manyan masu kudin dake zaune a kofar gidannan suna jiran a daura auren nan, kawai kuma sai inje ince musu amarya ta gudu, Sake matsowa tayi tace "to ya zakayi, saidai ko dan mu fita kunya a hada auren da Zainabu, kaga shikenan asirinka a rufe, ita kuma tunda rayuwar da ta zabarwa kanta kenan shikenan sai taje can tayi, dan taga tana da farin jinin ne, in kayi tafiya itace wannan saurayi itace wancan, cike da bacin rai Baffa ya hau kan zancen Ma'u ya zauna, ya fita yanata sababi cikin zuciyarshi.. bai nemi shawarar mukhtar ba dan baisan samm ya rasa shi a matsayin siriki saboda tarin hidimar da yakeyi mishi, gurin daurin auren yaje ya zauna aka fara gudanar da auren kamar yadda addini ya tanada, saida aka daura aure akayi komai sannan maroki ya fara fadin, "Tuwon girma miyarsa nama, yau naga auren da ban taba ganin irinsa ba, jama'a ku shaida an daura auren *ZAINAB* DA *MUNTARI* akan sadaki naira na gugan naira har naira Dubu Uku.... Ba Mukhtar bane kadai ya girgiza, hatta Mahaifinshi saida ya tafi tunanin Zainab ko Suwaiba...... Mrs Tijjani Shattima..... [07/03 2:02 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣0⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Alhaji ku yafe ni!, na yanke hukunci ba tare da neman yardarku ba, dan Allah ku gafarce ni, nayi hakan ne dan in fitar damu daga kunyar jama'ar da muka gayyata, Baffa ne ke jero musu bayanan ban baki lokacin da suka kebe da Alhaji Garba yayi mishi tambayar dalilin sauya akalar daurin auren, share hawaye yayi ya cigaba da cewa, "yarinyar nan taso ta wulakanta ni, sai Allah yasa ina da 'ya'ya matan da basuyi aure ba, kuma bana son mutum kamili kamar Muntari ya subuce min, da zainab da Suwaiba duk daya ne, uwa daya uba daya suke, dan haka kaga wanda yazo daukar suwaiba kuma ya samu zainab ai duk daya ne tunda tsatso daya suka fito, kasa Magana Mukhtar da zuciyarshi ta kai kololuwa gurin bacin rai yayi, har lokacin baiji ko daya daga kwatan son da yake ma Suwaiba ya fita a ranshi ba, da yaji Babanshi na kokarin amincewa da batun yayi saurin cewa "Abba, dan Allah kuyi hakuri, ni suwaiba kadai nakeso, in aka daura mana aure da ita nasan zata hakura ta zauna dani! "Naso yin hakan,amma abin yaci tura saboda guduwa tayi tabar gidan, Baffa ya karashe cike da damuwa, wani abu Muntarin yaji ya soki kahon zuciyarshi, har kiyayyar ta kai haka, ta ina ya gaza da ya samu macen da ta nuna mishi irin wannan kiyayyar, me ya rasa, babu abinda bai mallaka ba na daga dangin kyau, ilimi, gayu, uwa uba arziki na jama'a da kuma na dukiya, me yasa Suwaiba zata rusa tanadin da yayi wa rayuwarsu, yanzu kenan dukkan mafarkinshi zai zamto cikakken mafarki, kenan babu ko daya a cikin mafarkinshi da zai zamto gaskiya, baisan Hawaye ya fito a cikin idanuwanshi ba saida yaji duminsu a kuncinshi, mikewa yayi ya fita zauren hade da share hawayen fuskarshi, motar da suka zo shi da abokanshi ya shiga hade rufe fuskarsa dan hawayen sunki daina zuba, Allah ya sani ba karamin so yake yi ma Suwaiba ba.... Godiya sosai Baffa yayi wa Baban muntari saboda fahimtarshi da yayi,da Kuma alkawarin da yayi mishi na yarshi bazata wulakanta a cikin zuri'arshi ba, ko yana so ko baya so dole ya karbeta hannu bibbiyu a matsayin matarshi, dan zuri'armu kaff babu me wulakanta mace... Sai dare suwaiba ta dawo gida lokacin Ma'u na buduri da makota ana shirin kai Zainab dakin miji, kallo ne ya dawo kanta, daga mai yi mata habaici, sai mai yi mata kallon marar hankali, dakin Baffa ta shige a darare, zaune ta sameshi yayi tagumi yana tunanin ta inda zai fara neman suwaiba, jin muryarta ne ya sanyashi waigowa da sauri, sanyi yaji a zuciyarshi da ya ganta lafiya kalau, a fili kuwa fada ya rufeta dashi, saida yayi mata cin mutunci sannan a karshe yace "Wallahi, wallahi, kinga rantsuwar nan, bata da kaffara, bazaki kara daga kafarki kije makaranta ba, kina cikin gidannan har sai na samu wanda zan bawa ke sadaka, ke ba takamarki kinada farin jinin samari ba, kin daukesu kamar rigar canji, to ki sani kin jawa kanki a gurina, fita ko nan da kofar gida ne ban yarda kiyi ta ba, sai ki zauna a gidan tunda kin zabi butulcewa Allah da ni'imar da yayi miki, tashi ki fita ki bani guri mutuniyar banza mutuniyar hofi, tashi tayi ta fita da gudu tana rusa kuka, a kofar dakin tayi karo da masu kai Amarya ana wakar "Ayye mama", ta gefensu tabi ta shige dakinsu ta kara bude wani sabon babin kukan.... (oyoyo talauci inji Meela) Rayuwar auren Zainab da Muntari kadaran kadaham, sam baya wulakanta ta saboda ya karanci hakkin mace akan miji, kuma mahaifinshi ya sake tunasar dashi, Da fari ta dan samu matsala da mahaifiyarshi domin sam bata san zainab, gani takeyi an lika mishi ita ne dan a cuceshi, saida "Abba" yayi mata nasihar cewa matar mutum kabarinsa, kuma wata bata auren mijin wata, sannan ne ta dan sakko, amma duk da haka bata cika bata muhimmanci ba, biyayyar da zainab ke mishi ne ya sanya shi sake sakewa da ita, wani lokaci yakan tuna suwaiba wani shashin zuciyarshi yaji yayi mugun tsanarta, wani shashin kuma yaji ta ciki a killece, ya sha in zai ambaci sunan zainab yace suwaiba, in ko yayi tafiya to fa sai ya cirewa suwaiba tsaraba, kome zaiyi da ita yake hadawa yayi, wannan abu shi ya kara dungunzuma zuciyar Zainab taji gaba daya Suwaiba ta fice a ranta, kullum cikin kulli Goggo take dan dai kawai kar auren yarta ya mutu, a irin zaman da sukeyi Zainab ta samu ciki har ta haihu, haihuwarta ita ta kara daraja ta a idon iyayenshi da shi kanshi, sannu sannu ya fara fitar da Suwaiba a cikin ranshi, saboda samun zuri'a da ya farayi. Saida Zainab ta jera mishi 'ya'ya Mata uku a karancin tsakani (gwarne ) cikin shekara hudun aurensu, Reemah ce Babba, sai Radiya Sai Raudha, a lokacin da take da cikin na hudu ne Muntari ya saduda ya mika mata ragamar rayuwarshi, domin yasan yanzu indai za'a kirashi to itace ta biyun da za'a kira a rayuwarshi.... Ita kuwa suwaiba baiwar Allah ta zama baiwa ta gidi, komai na gidan ita takeyi, babu makarantar islamiyya, babu fita cikin gari, iyakarta shagon buzu Adamu mai gadin jikin gidansu, duk irin kyawun da

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156