Skip to content

Chapter 12

Chapter 12

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

faru, tsayar da wutar yayi chak a Kan fuskarta da ta kumbura ta jike sharkaf da hawaye, girman da ta kara bazai sa ya manta fuskarta ba domin ita din jininshi ce, wacce tausayinsu ke karya dukkan sassa na jijiyoyin jikinshi, Cike da tashin hankali ya furta sunan NADEEYAH!!! ,, Tunda ya kara wayar a kunnenshi bai ce uffan ba, tana nan makale a kunnen yanajin duk abin da sukeyi bai tanka ba, bai kuma damu da sanin abinda ke faruwa ba, sunan da musaddiq ya fadi ne ya sanyashi kallon takardun dake gabanshi ya maimaita sunan Nadeeyah? "Me ya Samu Nadiya ya fadi da karfi kamar zai tsaga wayar..... Mrs Tijjani Shattima.... [04/12 09:48] Meela Adeel: ZUMUNCINMU A YAU By Aysha Ya'u Kurah 1⃣3⃣ WOHN IS 3 TODAY ALHAMDULILLAH WOHN FAMILY I LOVE YOU FISABILILLAH... A firgice Hinad ta saki kofin da ta Kai ruwa bakinta ta nufi gurinshi, ihunshi ba ita kadai Ya firgita ba har papa da fitsari ya farkar dashi, palon ya nufa da sauri. tsaye Ya samesu Hinad tana rike dashi tana tambayarshi, wayar dake kunnenshi papa ya amsa Ya Kara a kunne, Shuru yaji Ya cireta ya duba, kallon Hilal yayi yace "lafiya dai?, Kai da wa cikin daren nan,? Kai komai naka baka yinshi cikin hankali, dafa papa hinad tayi tace "shi da uncle ne papa ba fada bane, Wani abu ke faruwa a can gida naji Ya kira Sunan NADIYA, ajiye wayar yayi kan stool Ya Kalli hilal da idanuwanshi da farar fuskarshi sukayi jawur Saboda bacin ran rashin amsashin da musaddiq yayi, burinshi a wannan lokacin ya ganshi a Nigeria, cikin taushi papa yace "wacece nadiya? Inajin Nadiyar mamma suwaiba, Hinad ta bashi amsa,, dafashi papa yayi yace "me Ya sameta? Kamar jira yake "yace Nima bansani ba papa, Musaddiq Yaki fadamin, kamar accident ne! subhanallahi papa ya fadi Yana mai daukar wayar da niyyar sake kiran musaddiq, Ya kira Yafi sau shurin masaki babu amsa, A bangaren musaddiq kuwa tunda Ya saki wayar a kasa Ko takalmin da Ya cire bai sa ba ya fita Ya nufi inda suke, masifa Mahmoud ke mata kamar zai duketa, kuka sosai takeyi tana bashi hakuri, Nadiya!!! Ya kira sunanta a can karkashin makoshi, dago kanta tayi ta kalleshi, bata gane muryarshi ba Kuma bata ganinshi Saboda duhun dake gurin! a kufule Mahmoud yace ka Santa ne? Hannunta Ya kamo ya fara tafiya ba tare da Ya ba Mahmoud amsa ba, kuka mai karfi Nadiya ta saki tana fadin Dan Allah kuyi hakuri wallahi ban san--- shhhh Musaddiq ya katseta hade da daura lallausan hannunshi kan labbanta, hasken motar da ta gifta Su ne Ya bayyana mata fuskarshi, langwabar da kanta tayi hade da sakin doguwar ajiyar zuciya mai hade da shashsheka, hawayen dake fitowa a idanunta Ya shiga share mata da yatsun hannunshi, daga ina kike?? Ya tambayeta Yana mai bude bayan motar, cikin kuka tace "Baba, Baba--bashi da lafiya dan Allah yaya Musaddiq ka taimakemu kar Ya mutu, ba musaddiq ba har Mahmoud dake kufule sai da Ya tausaya mata, shiga ciki muje da sauri Musaddiq ya fadi yana gyara hannun kofar, a gaggauce ta shiga, Gudu Mahmoud keyi kamar zai tashi sama, a dai dai kofar gidan yayi parking, A tare suka shiga gidan da sauri, dakin da yake suka nufa, inda ta barshi a nan ta sameshi, sai dai wannan karan idanuwanshi a rufe suke kamar me bacci, murmushi tayi tace "Alhamdullilah kun ga ya samu bacci, kusa da mamma ta matsa wacce ke jingine jikin gadon kamar mutum mutumi, "ya samu bacci ko Mamma? Na tsorata sosai na fita babu Ko takalmi, a hanya na hadu da Su yaya musaddiq, gasu nan ku gaisa sai ki tashi Baba mu kaishi asibiti, "He is no more fa KYARI, Mahmoud yayi mishi rada a kunne.. Rawa jikin musaddiq ya fara yi Yayi saurin matsawa kusa dasu Nadiya, dafa Mamma yayi hannu na rawa Saboda firgici da tausayin rai, suuuu suka ga ta fadi kasa babu alamar numfashi, Innalillahi Wa Inna ilaihir rajiun Mahmoud ke maimatawa Saboda tsananin tashin hankali, Wani irin kuka Nadiya da musaddiq suka saki a tare, jijjigata Nadiya keyi tana kiran sunanta, komawa jikin Babansu tayi tana tashinshi, Baba ka tashi kaga Mamma, me Ya sameta, waje musaddiq ya fita da gudu Yana kuka kamar ba namiji ba, Mahmoud ne yayi karfin halin dagata Yana mata nasiha, fisgewa tayi ta kwanta kan mamma tana ihun kuka mai Sosa zuciya, "nasiha bata da muhalli a wannan lokacin, (Allah da Kuma Wanda abun Ya faru dashi ne kadai suka San irin halin radadin da mutum yake ciki a wannan lokacin).. zubar da ruwan hawayenta keyi a fuskar mamma Ya fara farfado da ita daga doguwar sumar shock din da shiga, motsin da nadiya taji ne Ya sata mikewa da sauri tana kallonta, dagota tayi tana kiran sunanta da karfi tana dariyar farin ciki, tsugunawa Mahmoud yayi ya rike kanta yace "jeki maza ki debo ruwa, a guje ta fita ta nufi ma'ajiyar ruwan Su ta dibo cikin kwanon sha, tare suka dawo da Musaddiq da idanuwanshi sukayi jawur saboda kuka, a hankali Mahmoud Ya debi ruwan a hannunshi ya shafa mata a fuskarta hade da tofa mata adduo'i, ajiyar zuciya ta saki Mai karfi ta fara binsu da idanu, tana sauke idonta kan Nadiya ta fashe da kuka Marar sauti, kukan da idan ka ga mai yinshi sai dukkan gabban jikinka sun saki saboda tsabar tausayi, rungumeta Nadiya tayi suka cigaba da kukan tare, Mahmoud ne kadai yayi karfin halin tashi ya rufe Baba da zani sannan Ya dawo Ya dafa Musaddiq yace "Tashi muje mu sanar da mutane a gaggauta Yi mishi sutura kafin safiya, Mikewa yayi yana share idonshi da bayan hannunshi kamar karamin yaro sukayi waje suna jiyo kukan Nadeeyah kamar ranta zai fita... Nayi tarayya da mutane da dama tun tasowa ta har kawo wannan lokacin, na hadu da mutane masu hali na Kwarai haka na hadu da marasa kirki Kwarai dagaske, a cikin yawon da nayi kasashen duniya da cikin kasarmu ta Nigeria ban taba haduwa da mutum Marar imani da kirki Wanda babu abinda ya sani Sai kansa ba irinki ki! dole ne yau in fitar da abin da yake raina, BAKI DA IMANI Badariyya, ki guji bakin duniya, ke ko babu baki ki guji rayuwar ita kanta, ganinki kikayi a inuwata shiyasa kike yin San ran-------- Tabdijam lahaulu Wa la quwwata, Alhaji!!! Ashe da raina zanji batun gori Ya shiga tsakaninka da jinina, Gori kuma??? Daddy ya furta yana kallon mummy da ta rike hab'a tana mishi kallon raini, kuka Badariyya ta fashe da shi tayi hanyar da mummy ta fito ta rungumeta, shafa bayanta ta shiga Yi tace "Gori mana Alhaji, har nawa Badariyya take da zaka kira ta da Marar imani? Har kana furta tana zaune a karkashin inuwarka, wallhy ko a mafarki ban taba kawo zakayi tunanin goranta ma Badariyya ba, Sai gashi yau a zahiri naga wannan bakar rana, mtswwwwwww... Daddy yaja dogon tsaki yace "Na goranta mata, indai Badariyya bazata canza halinta ba wallahi ba gori ba wata rana Kiri Kiri zan nuna ba n------ katse Maganar yayi dan baiga amfanin furta ta ba, Ya cigaba da fadin

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156