Skip to content

Chapter 52

Chapter 52

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

momma kice su tafi zan kawo shi, cike da mamakinshi ta kashe wayar tace "zai miko shi inaga yayi bacci ne, nagode sosai Raliya, a'a haba Anty babu godiya a tsakaninmu anty Raly ta fadi tana murmushi, sallama su Nadeeyah sukayi mata ta amsa cike da fara'a, bayan Nadeeyah tabi da kallo tana Nazarin wasu abubuwa, har saida ta kurewa ganinta sannan tayi ajiyar zuciya ta fara bude kulolin abincin.... Mrs Tijjani Shattima [15/03 12:04 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣7⃣ By *Aysha Ya'u kurah* *JIGON RAYUWA* Kallon Mamaki Anty Saude ta bishi dashi, kayan da ya shiga dasu sanye a jikinshi ba dasu ya fito ba, wannan karan Ash Shadda ce a jikinshi, yayi kyaun da shi kanshi ya yaba, babu ta inda Taheer bai hadu ba, ya hada komai da duk namiji zai yi tunkaho dashi, matsalarshi daya ido, ciwon idon da ya samo asali tun yana yaro gurin wasansu na yara, babu inda ba'a kaishi dan duba idon ba, saidai ya dan samu sauki amma bazai bar ciwon duka ba, a karshe har iyayenshi suka hakura suka dawo asibitocin ido na nigeria, a nan ne suka daurashi kan magunguna har idon yayi kyawu sosai, da taimakon Allah da taimakon glasses dinshi da suka kara fito da ainihin kyawunshi yake ganin abun da ke nesa.. Zaunar da Fadeel yayi akan kujera ya dauki nama daya cikin soyayyun naman da Anty Raly ta kawo, zama yayi kusa da Anty saude ya kai naman bakinshi yace "Momma zan fita, "Ina zuwa kuma? ta tambaya hade da ajiye plate din hannunta, Murmushi yayi mai matukar kyau yace "zan mika Fadeel gida, sannan zan je aiken da zuciyata take ta min kullum, "Hannunshi ta kama da sauri tace "Fara isar min da aiken TEE, fada min sakon in taya zuciyar taka adduar samun karbuwar sakon, nata hannun ya rike shima zuciyarshi na kai kawo, farin ciki ne cike a cikinta na ganin tana gab da samun abin da take so, lumshe idonshi yayi , kana hango yanda gashin idon ya kwanta ta cikin glass yace "i'm in love Momma, wani irin numfashi ta saki wanda zai tabbatarwa da mai kallonta tana cikin matsanancin farin ciki, "wacece Taheer? wacece wannan? ya Allah kayi mata albarka, share hawayen da ya zubo mata tayi, tace "bani labarin ta Tee, "murmushi yayi dan dama yasan yadda zatayi reacting kenan, yace "calm down Momma, with time zaki santa, kuma nasan zaki sota, ni dai addua'arki nake bukata, ina son ki dage da addu'ar samun nasara, inason zuciyata ta kasance da ita a duk bugun numfashina, tun ranar da fara ganinta har zuwa yau kaunarta ce ke kara tasiri a cikin ruhina, "rungumeshi tayi sosai tana fadin Alhamdulillah a jere har sau uku, jin kukan da takeyi yana neman yayi yawa ya sashi saurin raba jikinshi da nata, hannu yasa yana share mata hawayen hade da girgiza mata kai, a shagwabe yace "kina so in bata kwalliyata ne, sai ma na fasa in bawa zuciyata hakuri tunda aikenta nasa min ke kuka, dan mari takai ma fuskarshi tana dariya tace "tashi maza ka tafi, Allah ya baka dukkan sa'a my boy, daukar Fadeel yayi yace "Ameen Momma, kallon farin ciki ta bishi dashi hade da mikewa ta isa gaban hoton mahaifinshi, rau rau idonta yayi tayi saurin maida hawayen hade da fadin "tun bayan rasuwarka Taheer dinka bai sake yin farin ciki ba, yau!! a karo na biyu a rayuwarshi na ganshi cikin farin ciki, kasa controlling hawayenta tayi tace "we missed u alot Abba, Allah yayi maka rahama, adduoi ta shiga jerowa mijinta da danta, saida ta gama ta share hawayenta ta kira Abida mai mata hidima dan ta tattara parlon.... Sau biyu ya taba shiga gidan Anty Raly tun zuwanta unguwar, motar da ya dauko daga gida ma ta musamman ce kai kace garin zai bari ba kusa da gida ba, sai da yayi zaman minti uku a ciki sannan ya kashe ya dauki Fadeel, mai gadin na ganinshi ya tsuguna har kasa ya gaisheshi dan babu wanda baisan dan gidan Hajiya Saude ba a unguwar, bude mishi kofa yayi ya shiga, Baya yaja zai tsaya ya hango Husnah ta fito ta nufo gate din, tana ganinshi ta kara sauri tana fadin "uncle da kanka ka kawo shi, mika hannu tayi ta dauki Fadeel hade da ce mishi tana zuwa, mai gadin ta kira tace "ina lawalli, kace yaje ya siyowa Anty Gas, cikin girmamawa ya amsa ya fita da niyyar zuwa kiran lawali driver, Dawowa gurin Taheer tayi ta sake gaisheshi, tambayoyi ta fara jefo mishi, "uncle dama kai dan Anty saude ne? ai na santa, bansan kai danta ba, kasan last year ka fara teaching a school shiyasa bamu san kai danta bane, she is very nice, kasan akwai lo--- katseta yayi yana dariya yace "ashe haka kike da surutu, to tunda bazaki bani gurin zama ba bari in tafi, da sauri tace "laaa sorry uncle muje dan Allah, bai bata lokaci ba ya bita hade da addu'ar Allah ya bashi karfin gwiwar sanar da ita, parlon Baban Fadeel ta bude mishi tayi mishi iso har ciki ya zauna, har zata zauna sai tayi saurin mikewa tace "bari in kawo maka ruwa, murmushi yayi yace "na dauka zama zakiyi da sai ince ashe baki iya tarbar baki ba, dariya tayi ta wuce kitchen, Suna shiga kitchen Fadeel ya saki Kashin da ya fito daga pampers har rigar Husnah, wani irin ihu ta saki wanda ya sanya Nadeeyah da Anty Raly zuwa kitchen din, dariya Raliya tayi na yadda Husnah ta bata baki hade da tale riga da kafarta, da sauri ta dauki Fadeel da ya fara bata mata kitchen da kashi tayi daki dashi, kallon Nadeeyah Husna tayi tace "dan Allah ki kai mishi juice parlor, bata tsaya yi mata bayani ba ta wuce daki tana ware kafa, dariya Nadeeyah tayi ta shirya juice a tray, duk tunaninta Baban Fadeel aka shiryawa abinci a parlon kafin ya dawo, bata damu da yadda gashinta yake a bude ba saboda tasan bai dawo ba, gyara wanda ya dan zubo ta gefen idonta tayi ta wuce parlon, sam bata kula dashi ba saboda kujerar da yake zaune tana baya, duk wanda ya shigo parlon in ba ya lura dakyau ba bai kula da na zaune a kujerar, ganin babu abinci a parlon yasa ta dube dube, sai da ta razana saboda ganin bazata da tayi mishi, da sauri ta ajiye tray din jiki na rawa hade da bugawar kirji tace "ina wuni uncle, bai amsata ba ya tako har inda take tsaye shima kirjin nashi bugawa yake yi sosai, "murya can kasa yace "bakina ya kamata ya fara furta wannan, an yini lafiya *Umm Nadeeyah* Wani abun taji ya tsarga mata tun daga kwanyar kanta har tafin kafarta, yadda yayi kiran sunanta ta ya sake kashe mata jiki dan duk duniya banda Babanta babu mai kiranta da Umm Nadeeyah, bata amsa shi ba ta fara tafiya da niyyar barin parlon, *Nadeeyah* ya sake fadi a hankali yana kallonta, tsayawa tayi kamar zata saki fitsari saboda tsabar tsoron yanayin shi, bai karaso inda take ba yace "dawo ki zauna, akwai maganar da nake so

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156