Skip to content

Chapter 155

Chapter 155

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

zuciyarta, ko ba komai hankalinta ya kwanta tunda Junior ya saki jiki da mahaifinshi, ko a yanzu tasan Musaddiq zai samu saukin kaso 50 cikin ďari... Cikin sanďa ta isa gurin gadon dan gyarawa Junior hannu dan gab yake da famawa Musaddiq ciwon dake hannunshi wanda hakan zaiyi sanadiyyar katsewar baccin da ta tabbatar yana jin dadinsa, da dabara ta gyara mishi taji ya rikota yana sambatun "Daddy am very angry with u, i will nt talk to u ever again, Dariya tayi haďe da sumbatar kumatunshi ta zame hannunta cikin nashi, bargon dake jikinsu ta gyara musu ta shafa kan Junior ta dago da niyyar yin hanyar waje, kamar gizo haka taga idon Musaddiq a buďe, sake juyowa tayi ta kalleshi tagansu a rufe, ajiyar zuciya tayi ta fara tafiya dan zuwa kofar da zata sadata da waje, "Nadeeyah... Taji ya furta a hankali wanda ya sanya hantar cikinta kadawa, tsayawa tayi cakk a gurin ba tare da ta amsa ko ta waigo ta kalleshi ba.. jin har minti uku baiyi magana ba yasata juyawa dan ganin halin da yake ciki, wannan karan a juye yake idanuwan nan a rufe wani sabon bacci ne ma yayi gaba dashi wanda daga gani kasan yana cikin mayen magani ne, da sauri ta murďa kofar ta fita saboda kwalla da taji ta taru a idonta, wannan wacce iriyar zazzafar jarabawa ce, ya Allah ka kawo mana mafita baki dayanmu dan alfarmar annabi Muhammad s.a.w..... Gidan Alhaji Mukhtar ya zama tamkar gidan zaman makoki, kamar babu wata hidima da za'ayi a cikinsa nan da kwana biyu, Anty Reemah dasu Raudha sune kadai ke hidimarsu bisa ga umurnin Daddy, sai kuma Mummy da a yanzu takan samu shigowa duba jikin Musaddiq, duk da bata samun koda gaisawa da Daddy hakan yayi mata daďi tunda ya yafe mata kuma ya yafewa 'yayanshi yana sakar musu yanzu, a yanzu bata da burin da ya wuce taga rayuwar Musaddiq ta inganta, ta rasa kalmar da zata roki Nadeeyah dashi ta yarda da auren ďanta wanda ta zama sila a rabuwarsu, gashi abun da tayi yayi sanadiyyar sanya shi cikin tsakiyar rayuwa da mutuwa... A yau ma kamar kullum bayan ta gama gyara ďakin Goggo inda take kwana ta shirya tsaff dan tafiya dubo Musaddiq sannan ta zauna ayi kamun Nadeeyah da ita, tana rufe kofa ta jiyo muryar Badariyya wacce a yanzu Yareemah Suhail ke fitowa da ita ya kawo ta har gida tun dawowar Nadeeyah,, kwancen kayan da su Husna suka bata shi ta sanya tayi kyau abunta, sannan su suwidi suma sunyi kyansu dan a yanzu suna samun sake da kuma abinci wanda duk tazo sai yan uwa sun sai mata, "A'a Badariyyah kece a gidan, to juya muje ki duba jikin Musaddiq daga nan ki jira ayi kamun Nadeeyah dake, cike da damuwa ta juya suka fita suna tattauna damuwar da Musaddiq din ke ciki a sanadinsu, Badariyya a cikin ranta ta dau alwashin kebewa da Nadeeyah ta faďa mata abubuwan da tayi wanda ya rabasu, babu mamaki taji tausayinshi in tasan baya cikin hayyacinsa sanda yayi sakin.... Bayan ta gama sauraron kalaman Badariyya wanda takeyinsu cike da nadama tace "Badariyya abun da kukayi bai isa ya raba mu ba, tunda kika ga mun rabu to tabbas Allah ya rubuta rabuwar tamu ne a lokacin, sannan a yanzu in na ki uncle Taheer shi munsan halin da zai shiga, dan Allah ku fahimceni, ni kadai nasan halin da nake ciki, ku tayani addu'a nasan komai zai daidaita da yardar Allah... Share hawaye Badariyya tayi tace "Zamu tayaki, Allah yasa hakan shine mafi alkhairi.... Karfe huďu da yan mintuna Nadeeyah ta shirya cikin wani lace mai kyau da tsada cikin kayan da Taheer ya dinka mata, Anty Raly ke tsaye a kanta tana gyara mata kwalliyarta haďe da yi mata ďauri, wata farar alkyabba mai adon yellow ta dauko ta daura mata a kanta wanda hakan ya sake fitar da kayatuwar da amaryar tayi, jan lallen da akayi mata ya rinu sosai ya koma dark maroon hakan ba karamin sake fitar da suffar yatsunta yayi ba, zaunar da ita Anty Raly tayi tana jiyo sautin maganganu yan biki daga waje,, Cike da masifa take shirya su Nour tana daka musu tsawar su tsaya ko ta zanesu, a hankali Nadeeyah ta janyo hannun Abee tace "Kawo in shiryashi Husna, "Barshi.. kadai ta faďi haďe da janyo hannunshi ta sa mishi irin kayan dake jikin Hafeez, oya a je ayi wasa, banda barna da bata jiki, mikewa tayi da niyyar shiga bayi Nadeeyah ta riko hannunta, "Husnah nasan ni mai laif--- Lokaci na kurewa Nadeeyah, baki da laifin komai kaddararmu ce tazo a haka, na kasa dai jin saukin zuciyata ne shiyasa har yanzun kika ganni haka, with time in shaa Allah komai zai daidaita, Husnah ta katseta fuskar nan murtuke tamkar wacce akayi ma mutuwa.. ganin Nadeeyah na kokarin sake magana yasata zame hannunta daga cikin nata ta faďa bayi, wani irin kuka ne yazo musu a tare mai cin rai, saida sukaci suka koshi sannan Husnah tayi wanka ta fito ta shirya da sauri sauri tayi waje.... Sai biyar da kusan rabi dangin Taheer suka zo sa lallen amarya, sai da suka biya kawayen amarya wacce Amal ce kaďai sai Raliya da ta shiga cikin zancen, turaruka masu kamshin gaske suka karar a jikinta sauran yan uwansu na Agadez wadanda suka ji dadin ganin Nadeeyah da Hafeez suna rangaďa guďa, kwaryar nono wacce suka kawo gidan kanta ta kai hamsin, banda sauran gararrakin arziki da suka kawo, sunci sun sha a gidan sosai dan komai nasu daban aka ware musu, sai bayan Isha'i motocin da suka kawosu suka maida su.... A daddafe Musaddiq ya amsa gaisuwar Taheer wanda ke tsaye rike da danshi cikin tsadajjiyar shadda iri ďaya, lallaba Junior ya shiga yi bayan ya fuskanci irin fushin da yakeyi dashi, sannan kuma dan ya daukewa kanshi damuwar da ke cinshi tun kwana uku baya, wani mugun tari yaji Musaddiq nayi wanda ya sanyashi sakin hannun Junior ya isa gareshi haďe da dauko ruwa yana faďin sannu, ga ruwa kasha, runtse ido Musaddiq yayi haďe da kauda fuskarshi gefe, ya riga ya gama yanke duk wani hukuncin da ya dace, yasani a yanzu ganin gobe a gareshi nada matukar wahala, a yanzu ya sadaukar da komai yasan Nadeeyah da ďanshi bazasu taba yin kunci ba tunda suna tare da nagartaccen mutum irin Taheer wanda a haďuwarka dashi ta farko zata tabbatar da hakan komin kinka dashi, dafe kanshi yayi da hannayenshi biyu saboda hawayen dake zubo mishi babu kakkautawa, Mikewa Taheer yayi dukkan lakar jikinshi a sake ya kama hannun Junior suka sauka kasa, a hanyar da zai sadasu da kofar fita ya haďu da Hilal da ya dawo daga rakiyar abokansu, shima duk ya fukace ya fita hayyacinshi kamar shine mai ciwon, "A'a yallabai har kun fito, ya faďi yana mika mishi hannu, "Eh dare nayi, Allah ya bashi lafiya, "Ameen Hilal ya amsa haďe cewa sai da safe mun gode, "Allah ya tashemu lafiya Taheer yace yana mai saka kafarshi a waje, A gurin motarshi suka tsaya ya kira number Nadeeyah wacce ke kan dadduma tana zubda kwallar da ta zame mata jiki,

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156