Skip to content

Chapter 64

Chapter 64

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,197 words 0 views Progress saved
Download Book

tace "bani hankalinki nan, aure ya haramta tsakaninki da Musaddiq, Dariyar takaici Badar tayi tace "Haramta? Menene ya haramta shi, naga we are cousins saidai in baki son farin ciki na, Buge bakinta Mummy tayi da karfi hade da cewa "bance karki kara min maganar nan ba, Zafin buge bakin da zafin ganin zata rasa masoyinta yasata sakin wani irin Kuka, Inda take Goggo tayo tana tambayar dalilin kukanta, bata amsa ta ba ta cigaba da kukanta, Mummy ce ta tsuguna a gabanta zata fara rarrashi, kafin tayi magana ta katseta... "Cikin kuka mai cin rai tace menene ya haramta aurena da Yaya Musaddiq Mummy, menene shi, a iya sanina bake kika haifeni ba, nasan babu abin da zai haramta aurena dashi saidai in kema so kikeyi ki min gori akan asalina kamar yadda Daddy yayi m---- tassss.. mummy ta dauke ta da mari, itama kukan ne ya subuce mata ta rungumota tace "Allah ne ya haramta shi Badar, Asalinki bazai taba zame min abin gori ba saboda ke din makwafi biyu gareki a gurina, na diya da kuma kanwa, ke kadai ce jinin yar uwata wacce nake gani inji dadi, ban damu da ya kikazo duniya ba nidai nasan ina ganinki a matsayin LEEMAH, Cike da shashsheka Badar tace "to mummy ki yarda ya aureni, walhy in na rasa shi zan iya mutuwa, *Badariyya* *NONO* daya kuka sha da Musaddiq, babu aure a tsakaninku...... Wani irin zaman dirshan Badariyya tayi wanda ya tafi da duk wani ganinta na dan lokaci kadan, " *NONO DAYA KUKA SHA* Kalmar ke ta mata yawo a kwakwalwarta, duk da bata zuwa islamiyya sosai tasan haramcin auren, wasu zafafan Hawaye ne suka dinga ambaliyar fitowa a idonta, "NA MUTU, BANI DA SAURAN AMFANI, kalaman da ta dinga fada kenan kamar zautacciya, rungumeta Goggo tayi tace "bazaki mutu ba indai ina raye, Musaddiq ne ki kwantar da hankalinki zan san yadda zakiyi ki aureshi, anjima zanje gurin liman BADARU ya nemo wani hadisin da ya halasta aurenku, tashi kije maza ki wanke fuskarki, Tashi tayi kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta wuce bayin Goggo, Tashin hankalin da ta tarar a ciki ya sanya ta fitowa da gudu tana haki, "lafiya Suka hada baki suka tambaya, ina fa Lafiya bayi yayi kaca kaca, haba Goggo, dan Allah bakya yin flushing ne? Tabe baki Goggo tayi ta mikawa Zulai mai tayata aikin gida farar shinkafar tuwo dan ta gyara, ta waigo ta kalli Badar tace "tunda kinzo sai ki gyara ai, da tsufa na zanyi ta hakilon wankin bayi, "ay da sai zulai ta wanke ta fadi kamar zatayi kuka, murmushi Goggo tayi tace "kin sani sarai Zulai bata shiga min dakin miji bare bayi, matse fitsarin mararta tayi tace "gaskiya Goggo bazan iya ba, bazan iya zama har wata daya a nan gidan ba, "to ya zakiyi, haka nan zaki hakura, kije can dakin zulai ta tayaki gyarawa dan duk yayi kura, gani tayi kamar laughing stock suka maida ita ta nemi guri ta zauna kamar zatayi kuka tace "Mummy dan Allah ki kaini gidan Aunty Raudha ko Anty Radiya, "Lagos zaki bi Raudha, Radiya kuma kinsan halinta, duk yadda kuke shiri bazata raga miki gurin hidimar gida ba, kiyi zamanki anan na lokaci ne, Mummy ta fadi tana mikewa zata koma gida, Sallama tayi ma Goggo wacce ke amsata da kyar saboda laifukan da tayi mata ciki harda korar Badariyya da mijinta Yayi... Da kyar Goggo ta yarda Zulai ta wanke mata bayi, sai a sannan Badar ta shiga a kyankyame tayi fitsari ta fito da sauri, kan gadon Goggo ta kwanta tana maida numfashi.... "Fito kici Abinci, Goggo ta fadi tana fiffita tuwon a cikin faranti, badan taso ba sai dan tana jin yunwa ta sakko a gado ta fito waje, yadda yaukin miyar ke bin hannun Goggo da zulai yasa komawa daki da sauri, da karfi tace "Tuwo da rana tsaka Goggo, kuma miyar yauki kamar majina ta karashe fadi kar zatayi amai, wannan wace irin jarabawa ce, kudi ta fito dashi a jakarta ta kira Rilwanu ya siyo mata Abinci a restaurant mai kyau.... ko kallonta Goggo batayi ba ta cigaba da kai lomar tuwonta... Tunanin Musaddiq kwanta takeyi, ta ya za'ace babu aure a tsakaninsu, dan kawai sun sa nono daya, Allah yasa Liman ya gano wani hadisin da ya halasta hakan, in ba haka ba walalhi daga ita har shi saidai su mutu ba aure, dan duk wacce yayi yunkurin aura sai ta kasheta..... ******** Danna wayarshi yayi ya kira layin wayar da ya ba Nadeeyah a karo na ba adadi, har lokacin ba'a kunna wayar ba, juyi kawai yakeyi a kan makeken gadonshi, gaba daya ya rasa abinda yake mishi dadi, tun dawowarshi daga gidan su Nadeeyah ya kasa sukuni, ko abinci kwakwkwara bai iya kaiwa bakinshi ba, bacci kuwa sai dai dan barawo ne ya saceshi bayan ya idar da Sallar asuba, Ya gama sawa ranshi sha biyu nayi in yaji ba'a kunna wayar ba zai koma gidan koma me zai faru ya faru, Soyayyar Nadeeyah na neman yi ma zuciyarshi illa, yama za'ayi ya iya rayuwa babu ita, kallon kofar da aka murda yayi yaga Momma ta shigo dauke da kayan break fast, "Gud morning my Tee, Morning Momma, kin tashi lafiya? Lafiya kalau nd u? Nt bad ya fadi hade da mikewa zauna, 'Tee me yake damunka, yau baka fito ba kwata kwata, sannan jiya ina lura dakai dakyar ka tsakuri abinci, yar hirar da muka saba ma baka zauna munyi ba, tell me, meye matsalarka, Bazai iya boye komai na daga dangin farin cikinshi ko akasin haka daga gareta ba, gyara zama yayi ya rike hannuwanta, raunanannun idanuwanshi suka tara ruwa yace "Zan rasa ta Momma, Nadeeyah zatayi ma rayuwata nisa, Zan rasa farin cikin da ya ziyarceni a lokacin da na fidda ran zuwanshi, Fuskarshi ta tallaba da hannayenta biyu cike da tausayin shi tace "bazaka rasa ta ba, baka taba neman abu ka rasa ba Tee baza'a fara akan wannan ba da yardar Allah, ka kwantar da hankalinka kaci abincinka kamar ka sameta ka gama, Anjima da yamma zan kira *Kawu Tidjani* in fada mishi ya taho muje nema maka aure, Murmushin farin ciki yayi yace thank u Momma, Allah yayi miki sakayya da aljanna firdaus, Ameen my Boy, tashi maza kayi wanka ka shirya ka tafi gym wannan tumbin da ka fara ajiyewa ka gyarashi kafin ranar aurenka, shafa tumbin yayi yana dariya yace "ina tumbi anan Momma, sai dai in so kikeyi ya shafe da bayana, dariya tayi hade da mikewa tace "in kayi wanka kazo zan aikeka, gyada kai yayi yace "to Momma bari in fara wankan sai inci abincin.... ******** _Agadaz_.... *DIYA MURADUN AHMEDOO TIDJANI YALLO PALACE* Karar busar algaitar dake fitowa daga katafaren gidan shi ya bawa mutanen gurin damar mimmikewa saboda alamu ne na fitowar sarki, kirari dogarai suka fara yi cikin farasanci ana kodashi kamar yadda akewa sarakuna, Cikin daya daga jerin motocin da aka jera mishi ya shiga, nan ma fadawa suka dinga masa kirari har saida sukaga kurewar motar.. Wani katafaren gida motocin suka shiga, da sauri aka bude mishi kofa ya fito suka taka mishi har kofar parlon, suka murda ya

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156