Chapter 58
Chapter 58
suka faru kamar yadda kika ji na fadesu, yanzu kin yarda da maganata na cewa ban taba magana da mijinki ba, na yafe miki zargin da kikayi min, domin a yau bana fatan abun da zai bata min rai, a cikin farin ciki nake matuka na ganin Abdallah na ya samu abinda yayi shekara da shekaru yana kawaicin tambayarsa duk da nasan babu ranar da zata fito ta fadi ba tare da yayi tunanin rashin mahaifi ba, kullum in na kalli murmushinsa nakan hango damuwa a bayan murmushin, wannan suna da ake kiranshi dashi na *ABDALLAH HANNE*, yana matukar yi min ciwo, ansha zuwa gabanshi a kirashi da dan mace, duk damuwar da Abdallah zaiyi bai taba yarda yayi ta a gabana ba, sakin Goggo tayi hade daga hannun sama tace "Alhamdulillah, Allah zan cika maka alkawarin da na dauka na yin azumi duk ranar da ka cika min buri na... Murmushin farin ciki Baffa yayi yace "Alhamdulillah, Allah mun gode maka da ka dawo mana da saifullahi, ina ma Allah zai dawo da Suwaiba ta dawo taga dan biyun ta, sai dai kashh Allah baya barin wani dan wani yaji dadi, kallon Mamaki Anni tayi ma Baffa tace "kana nufin Abdallah yan biyu ne? Kwarai kuwa Baffa ya fadi yana gyara zama, Gaba daya ya manta da Ma'u da bai samun katabus in tana guri, ya cigaba da cewa "su biyu mahaifiyarsu ta haifa, kamar yadda kika sani shi mun dauka ya mutu, to ashe shi din ne rayayye ita kuwa Suwaiba tabi mahaifiyarsu, watanni kenan da mutuwarta, ta rasu ta bar 'ya'ya uku, HAFEEZ shine babba, sai Nadeeyah da Zainab, "_Hafeez_" Papy ya maimaita wasu hawayen masu zafi suka biyo bayan furucinshi, "Tabbas jini ba karya bane Anni ta fadi tana share nata hawayen, soyayyar da Abdallah ya nunawa Hafeez daga ganin farko ashe ba haka kawai bace, ashe Jini ne yayi aikin shi, dalilin zuwan Hafeez karatu Gombe ba karatun bane, wannan haduwar itace silar zuwanshi, duk inda alkhairi yake baya taba faduwa kasa banza ta karshe tana goge idonta da gefen hijab dinta, waya Papy ya dauko ya danna number Hafeez, "Kana ina ne?, ya tambaya murya a shake, "Muna kofar gida, mu zo ne? Hafeez ya amsa cike da girmamawa, "eh kawai papy yace ya kashe wayar, Hankali a tashe ya shigo gidan saboda yanayin da yaji muryar yasan babu lafiya, kusa dashi yaje ya tsuguna "Gani Papy, Wani irin kallo yayi mishi wanda yake nuna tsantsar soyayya ga mai yinshi, hannunshi ya rike hade da hada jikinshi da nashi da karfi, "kai jinina ne Hafeez, ashe kai dana ne, ina ma nasan wannan tun ranar farko, da kome zakayi tare zamuyi shi, da ban barka kayi wahalar komai da kanka ba, cikin rashin fahimta Hafeez ya da dago ya kalli idon Papy da yayi jajur, zaiyi magana Papy yayi saurin kada kanshi yace "kai jinina ne Hafeez, kai dan yar uwata ne, dan wacce muka kwanta a mahaifa daya ne, Wani irin kukan farin ciki ne ya kufcewa Hafeez, duk yadda yakai da hangenshi bai hararo kusancin nasu har ya kai haka ba, shidai yasan kamannin Baffa sosai yake gani a jikin Papy sai fari da ya banbanta su, sake rungumeshi Papy yayi yace "yau ranar farin ciki ce ba ta kuka ba, Mummy da karyayyar zuciyarta ta tsumu sosai tace "kukan ya zama dole, kuka ne na farin ciki, Shi yanzu nasan kukan tunowa da Suwaiba yakeyi, share hawayen tausayi tayi tace "ina ma Lokacin da suwaiba ta debo mai tsawo ne ta ga wannan ranar, kallonta Papy yayi yaga ita din ma tana dan yanayi dashi yace "kema yar---- cike da murna Baffa ya katseshi da cewa yayarka ce, ita ce Babba, nuna Ma'u yayi yace "wannan ita ce ta haifeta, su biyu ne, Allah yayi wa Halima rasuwa da dadewa, sai ita kadai ta rage mana, ashe wani farin cikin na tafe zuwa garemu, ashe ina da rabon ganin Magaji na kafin kasa ta rufe min ido, Wannan kalma ta *MAGAJI* ita sanya Goggo jin wani dumi tun daga kanta har cikinta, Ido ta zurawa Baffa da yake ta sambatu a gaban Papy da Anni, duk yadda taso su hada ido dashi sam yaki dan gaba daya ya manta Allah yayi halittar ta a gurin, Yasan dai tana makale cikin ranshi amma ganin Papy ya sanyashi mance duk wata soyayya in ba tashi ba, ji yakeyi ina ma ace da kuruciyarshi da sai yayi zagaye da Papy a bayanshi ba tare da ya gaji ba.. Wani irin kugin taji a cikinta tunda Anni ta fara basu labarin shi dawo mata, ganin yadda tun yanzu Baffa ya ki koda kallonta ya tabbatar mata da lallai akwai aiki a gaban ta, Mikewa tayi da niyyar tafiya bayi dan cikin nata jinshi takeyi kamar zata kasayar da ya'yan hanjinta, Tana mikewa taji kafarta tayi mata nauyi saboda yadda zawon ya taho mata gadan gadan, dakyar ta daga kafarta, tana dagawa zanin jikinta ya sabule ta feso shi ba tare da sanin inda zashi ba, Wani irin ihu Radiya ta saki tana fadin "I'm dead" wayyo Allah na, "Dariyar Ruwaida ce ta cika gurin tana yi tana fadin *nyan nyan nya* disgusting! Papy kagani da kace "in an min abu in dinga hakuri Allah zai saka min, yau gashi naga ni da idona, wayyo cikina, she deserve more old lady karo mata,, Janyota Mami tayi da karfi ta sake maida idonta cikin mayafinta kamar yadda kowa yayi a gurin, kunnenta taja tace "ke wace irin yarinya ce, in sake jin kince pim kiga abun da zan miki, Mummy ce ta tashi da sauri tana tare Goggo tana fadin Goggo lafiya, Hawayen takaicin da Goggo ke rikewa ya zubo a kuncinta, cike tsoron ganin hawaye a idon wacce babu abin da ke sata kuka Mummy ta ja hannunta sukayi bayi, shi kuwa Baffa maida kallonshi gurin Radiya dake kuka tana kyankyame jikinta yayi yace "je ki wanke jikinki mana, ko so kikeyi warin ya kashe mu, baki ganin muna cikin farin ciki ne, karaff kalamanshi a kunnen Goggo, wani Kukan ta sake fashewa dashi a zuciyarta tana tambayar kanta ta inda aka samo matsalar, Damuwa ce karara a fuskar Mummy dan iya rayuwarta bata taba ganin hawaye a idon Goggo ba, bayan ta gama kimtsa ta suna jiyo muryar Baffa yana basu Labarin Suwaiba da 'yayanta, ita kanta Radiya cike take da mamakin yadda yake basu labarin suwaiba da 'yayanta dan a da ko labarinsu baya son ji bare ya ba wani, Kallon Goggo Mummy tayi tace "kiyi ma Baffa uzuri, shekaru sama da arbain rabonshi da dan da ya cire rai da kasancewarsa a duniya, sannan kuma shi kadai ya zame mishi namiji, kinga dole yayi farin ciki, ni kaina cikin farin ciki nake, dan a yanzu na fita a sahun ni kadai, mun zama biyu, ďan uwa dadi gareshi Gog---- dogon tsaki taja wanda ya katse mummy da karasa maganar ta, "Ba tun yau na lura da cewa ke din bakya kishi na da kanki ba, inama Allah Halima ya bar min ya daukeki Goggo ta fadi cikin gushewar hankali, Zaro ido Mummy tayi zatayi magana ta jiyo muryar Baffa yana kwala kiranta, bai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156