Chapter 23
Chapter 23
ya dake ki? "Uhmmm uhmm--- uhmn--- ka fita lokacin yace in-- in ya dawo zai min dukan tsiya, ina tsoron kar ya dake ni shiyasa na fadi ma mummy ya dake ni dan ayi wa tufkar hanci, kallon Mummy Musaddiq yayi yace "kinji abinda tace ko in maimaita miki? A kunyace mummy tace "to meye nashi na mata barazana, ai dole in gasgata saboda nasan bashi da aiki sai duka da zagin na kasa dashi, Anty Reemah kuwa idonta na kan Hilal dake rike da kunci har lokacin, shi din ma ita yake kallo idonshi jajur, karyar da kanta tayi zata mishi magana yayi hanyar dakin Musaddiq da sauri, ajiyar zuciya tayi ta kalli Musaddiq dake ta ma Mummy magana cikin fada, "Nadeeyah da kika kira munafuka babu abinda tace game da kowa, hasali ma wannan bakar dagar bata san meke faruwa ba har saida muka zo kaita asibiti, ita ce ma tayi ma Hilal rashin kunya ina jinta bai tanka ba, walhy in dai baki daina biyewa yarinyar nan ba wata rana sai kinyi dana sani marar amfani, haba dan Allah ya karashe rai a bace hade da gallawa Badar harara, Durkusawa yayi kusa da Nadeeyah dake kuka yace "tashi kije daki kisha magani ki kwanta, mikewa tayi tana share hawaye ta fara tafiya, kayan da Hilal ya sai mata ya dauko ya bi bayanta, Dakin Delu yaga tana kokarin shiga yace "ba nan bane dakin gashi nan, ya nuna dakin su Badar, Husnah da tun ihun Badar ta farka, tayi hamma tace "a dakin Delu ta kwana kayanta na can, jinginar da kanshi yayi jigin bango yace "Hasbunallah, dakin ya bita ya mika mata kayan ya fito da sauri yayi hanyar Sama, A tsaye yaga Daddy yayi folding arms dinshi fuskar nan tashi a murtuke, asalin Kanuri ya bayyana a tare dashi, "Daddy kana gan----- naga komai *Saaaaaadiq* " haka yake kiranshi har sai yaja sunan! kasa ya sauko ya kalli Mummy da duk ta sukurkurce yace "bana san jin komai, anjima karfe biyu na rana bayan jumm'a duk mu hallara a gidan Baffa, "i want to clear all my mystifications, dole ne ku fitar dani cikin duhu, dan alamu sun nuna min ba Goggo bace ta haifi SUWAIBA, sannan ba talaucin su bane ya sanya ku tsanarsu a matsayinsu na jininku, akwai dai wani abun a kasa, *WALLAHI* Daddy ya fadi da muryar da ta ba Mummy tsoro, "in har baku fitar dani cikin wannan duhun ba aurenmu dake zai kare, saboda na gaji sosai da irin halinku da ya shafi zuri'ata, bazan dauka ba..! ya mike a zafafe ya haye sama.. Jikin Mummy babu inda bai rawa, ta mike ta haye saman ita ma ta bar Musaddiq da Reemah da Husnah a falon sunyi jugum jugum.....!!!! Mrs Tijjani Shattima..... [07/03 6:31 AM] fareedah: ••ZUMUNCINMU A YAU•• 2⃣0⃣ By Aysha Ya'u kurah "Wai ina zaku tafi ne? bakwa ganin dare yayi! hannunta ta nuna saitin agogo ta cigaba da fadin pass 10 fa, bansan yawon banza ku koma dakinku, Ja da baya Musaddiq yayi yace "wallahi Anty Reemah haka na fada mishi wai shi yau a gidan mummy zai kwana, bansan sanda ya fara shiri da compound din gidan ba, ni da ya kyaleni ma bacci nake ji, Harara Hilal ya watsawa Musaddiq hade da tsaki, yace "plss mum, air con din dakina ba gas and u knw dat, Kuma tun isowarmu na fadawa Papa, ajiye kopin coffee Papa yayi ya kalli Hilal yace "wane Papan? "kai mana, Hilal ya fadi hade karyar da kanshi a shagwabe yace "plss papa don't prolong dis issue, dare na dada yi, mukullin motar papa ya dauka yaja hannun Musaddiq yace "Gud nyt Honey stars, girgiza kai Anty Reemah tayi tace "Allah ya shirya, Ameen!! Papa yace hade janyota jikinshi, hab'arta ya dago ya kalli kwayar idonta wacce ya hango damuwa sosai a cikin ta, me akayi ma first lady? Wa ya taba min ke? tun dawowarki na lura da yanayin ki, sannan kiran da Raliya tayi miki naga ya kara sanya ki cikin damuwa, fada min matsalarki ko tafi karfina inyi kokarin magance miki ita, Ajiyar zuciya tayi tace "as usual Papa, sai matsala ta dauko kamar zata warware sai ta kara dagulewa, nasan duk family ana samun crisis, amma sai inga namu na daban ne, san zuciya shine ke haddasa komai cikin gurbacewar zumuncin zuriarmu, labarin abin da ya faru a gidan su Nadeeyah ta bashi ta daura da abin da Raliya ta fada mata a waya, sannan ta cigaba da cewa "tun ina karama in naga yadda suke treating mama suwaiba sai inyi ta tunanin anya kuwa Goggo ce ta haifeta, abin da Goggo kema Mummy da Anty Leemah sam yasha banban da wanda take ma mama Suwaiba, a kuruciyata sai nayi tunanin ko dan ta auri talaka ne, furucin Goggo na yau ya sanyani cikin tunani sosai na son sanin wacece ATIKA, meye alakarmu da ita..... Tambayar da Anty Reemah keyi wa zuciyarta a wannan lokacin ita Daddy keyi a zaune a balcony din dakinshi, Isowar mummy gurin ne ya katse tunaninshi, cikin taushin murya tace "in kawo maka ruwan zafin? black or green tea? Wanne zan kawo, Mikewa yayi yace "ko wanne ki kawo, da fatan yaran nan sun kwanta, kuma babu wata matsala,? gyada kai mummy tayi tace "eh Nadeeyah ma tayi bacci ita kuma zainab tana gidan Reemah, Good Daddy yace hade da cewa ki ja ma Badariyya kunne, bana son fitina, suyi zamansu guri daya tunda duk sa'anni ne, zama cikin nasu shine zai kara musu dankon zumunci, dan Allah ki kula sosai dan duk ya'yanki ne banason nuna banbanci, murmushin yake mummy tayi tace "ba sai ka tuna min ba, na riga na fada musu, kuma in shaa Allah komai zai tafi normal, kafin yayi magana yaji Hon din mota ya cika gidan, gate din ya kallo daga sama dan ganin mai shigowa a wannan daren, hasken dake gidan ne ya haska cikin motar, ganin Musaddiq kadai yakan sanya Alhj Mukhtar manta duk wata damuwa, Ajiyar zuciya yayi yace "su kuma daga ina, cike da jin dadin yadda fuskar Daddy ta canza mummy tace "Gidan Reemah, ni duk tunanina a can zai kwana, tafiya ya fara yi yana fadin "gara dai ya dawo gida, tunda ya dawo ma bamu zauna ba, bare mu tattauna akan sakamakon makarantarshi, Sakkowarshi kasa tayi daidai da shigowar su Musaddiq cikin parlon, Remote Daddy ya dauka fuskarshi cike da annashuwar ganin zaratan mazan familyn shi, kuma ababen kaunarshi yace "ABOKI KANGIWA, kai ne a daren nan? yau anan zaka kwana kenan, kusa dashi Hilal yaje ya rungumeshi yace "yes ABOKI DADDY, a dakinka ma zan kwana, mu raba dare muna hira, mun dade bamu hadu ba, dariya Daddy yayi ya zauna yana kallon Musaddiq dake tsaye yana murmushi, "zo ka zauna auta na, kar kafarka ta sage, AUTA fa Daddy? To in shi auta ne ni kuma fa? Husna da ta fito daga kitchen rike da plate din indomie ta fadi tana turo baki, Dariya Daddy yayi yace "haka ne my baby, na manta ne, ba auta bane, kafi auta ne, kece auta,, Kumbura baki tayi tace "ni ce duka biyun, dariya sukayi dukkansu, mummy ta mika
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156