Chapter 31
Chapter 31
shaďi ta fara narkarta dashi, bata taba raba dayan biyu Baffa ne yayi cikin nan, dukanta takeyi sosai Haire na tarewa tana faďin karki kashe musu 'ya Ma'u, ki bi komai a hankali, wani irin hankali zan bishi shi amm, ni Baffa zai ciwa amana? Ni zai ha'inta? kuka sosai takeyi tana dada narkar baiwar Allah da sanda, kwace sandar Haire tayi tace "shiyasa nace baki da wayau Ma'u, in ba rashin dabara ba kya fara jibgarta, maimakon ki bari mu yi komai cikin hikima, ga magunguna nan da zaisa cikin ya fita cikin makwarara.... Saidai kiga bin makwarara a gidanki da yardar Allah Aisha ta fadi tana karasa shigowa cikin gidan rai a baceee..... Mrs Tijjani Shattima..... [03/03 9:47 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣6⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* *Rabon Ajali* Da gudu Bingel ta rungume Aisha tana kuka tana fada mata irin dukan da mamanta tayi ma Atika, share mata hawaye tayi tace "Allah ya turo mai cetonta Zainabu, in da take tsugune suka karaso Aisha ta dagata tace "muje can gida, in shaa Allahu daga yau kin bar zaman wahala, cikin nan kuma sai kin haifeshi koda kuwa dukkan kauyen nan zasu taru akanki, kuma dole ya amsa sunan Muhammadu a matsayin uba, wani irin kululun bakin ciki ne ya ziyarci Ma'u, bata dubi girma da darajar da Aisha kedashi a kauyen ba ta fara zaginta, ta inda take shiga bata nan take fita ba, Aisha dai bata waigo ta kalleta ba tace "sai dai ki mutu da bakin ciki dan cikin nan babu abin da zai hanashi zuwa duniya, wani sabon faifan zagin ta bude idanuwanta sukayi jajur, asalinta na arniyar ukari marar imani ya bayyana a jikinta, da sauri Haire ta toshe mata baki tace "mai babban suna kike zagi Ma'u?, kinason Allahn Hardejo yayi fushi da dukka yan kauyen nan ne?, idan hankali ya gushe nemo shi akeyi, cike da masifa ta ture Haire tace "wallee sai kunga abinda zai sameku, dukkanku, badai ni *NANKWAT MANASIR* kukayi wa haka ba,(sunanta kenan kafin haduwarsu da Baffa) walle duk sai kun gani, ta finciko hannun Bingel hade da daukar Boddo ta fice a gidan, hakuri Haire ta bita tana bata, sam bata saurareta ba ta wuce da yaran, Bingel na kuka taki ko kallonta bare ta kula da abinda take so, Alkhairi!!! in shaa Allah Aisha ta fadi tana kallon ma'u da tayi nisa da gidan, gida suka wuce suma Haire na biye dasu tana fadin "Dan Allahn Hardejo kiyi hakuri mai babban suna, walle ko taba jikinta banyi baa, katseta Aisha tayi tace "Babu komai Haire, kowa yayi nagari dan kansa... Suna isa yaran gidan suka rugo suna ihu hade rungumeta, dama sunyi kewarta matuka dan ma'u bata yarda suzo gidansu, Matan Hardejo ma suka fito suna musu barka da zuwa hade da jajantawa Atika, Ďaki Aisha ta wuce da ita, tasa maryam ta iza wuta tasa ruwan wanka, kafin ruwan yayi zafi ta dama mata fura da nono, sannan tasa aka karbo mata kwadon zogale a gurin Laure matar Hardejo ta biyu, zogalen kadai ta iya ci, tasha ruwa, ta dan kwanta a inda take zaune, bacci ne mai karfi da dadi yayi gaba da ita, gyara mata kwanciya Aisha tayi cike da tausayawa, kyakykyawar fuskarta ta kalla ta sa hannu ta share mata hawayen dake gangarowa ta gefen idonta, a zuciyarta tana Hailala ga ubangijin da yake da ikon mayar da mai gata bawa, Allah ka ďaura mana jarabawa mai sauki wacce zamu iya daukarta, da waďannan adduoin mai babban suna ta tashi ta fita tsakar gidan dan samowa Atika naman da zata gasa mata, kicibus tayi da yaro ya shigo da zabuwa an yanka ta, dariya tayi tace "ko baka fada ba nasan Bala ne ya aiko ka, gyada kai yaron yayi ya fita da gudu, albarka ta shiga shi mishi saboda kullum sai ya kawo musu halastacciyar dabba gidan sunci, maryam ta mikawa zabon tace "maza tayi amfani da ruwan zafin ta gyara shi, amsa tayi cikin ladabi ta gyara shi hade da bankareshi yadda zaiyi kyaun gashi, kafin Mamanta ta fito har ta fara gasashi cike da kwarewa, saida ta gama tass sannan ta sa a karamin bangaji ta wuce ta kaima Aisha.... Saboda dadewa bata huta ba, da kuma karancin bacci da take samu yasata ta kai har bayan isha'i bata tashi ba, babu wanda ya tasheta saboda yanayin da take ciki, saida tayi bacci mai isarta sannan ta tashi tana mika hade da salati, ganin duhun dakin ya sanyata mikewa zubur ta fara lulube, dan hasken dake tsakar gidan ta hango ta tsagin tagar dakin, ajiyar zuciya tayi ta dauki mayafinta ta rufe kanta sannan ta fito waje, kamar jiranta yaran sukeyi ta fito suka kewaya ta suna kallonta, magana Aisha tayi mata tace "kije kiyi alwala kiyi salloli sai kici abinci kiyi wanka.. Tana idar da sallah suka kewaye ta da abinci da fura da kuma gasashshen zabo, tuwon taci sosai tana hamdalla a zuciyarta, rabon ta da taci irinshi tunda kaddara ta kaita auren Baffa, saida taci tayi katt sannan ta kora da ruwa, naman ne kadai bata ci ba saboda sam batason jin kamshin gashi, Ba karamin horata Ma'u tayi ba da gashinta na kullum, wanka tayi da ruwan zafi mai dadi sannan ta dawo inda suke ta zauna, rokon Allah ta shiga yi da ya barta a cikin su har Allah ya kawo sanadiyyar da zai hadata da Abbunta da kaninta Ateek, kallon irin zaman da sukeyi takeyi mai cike da tsafta da kaunar juna, yaran gidan duk suna kaunar junansu haka basa yi ma wacce ba uwarsu ba rashin kunya, matan kuwa kullum cikin hira suke da karatun al kur'ani, wani lokacin kuma mai babban suna ta tarasu dukkansu harda makota ta basu tarihin Annabawan Allah da iyalensu, da irin gwagwarmayar da suka sha, shiyasa a ko da yaushe gidan yake a cike da mata da maza, koda yaushe gidan baya rabo da abin ci da kuma sha saboda yawan sadaukarwar da sukeyi..... Shigowa gidan yayi fuska dauke da murmushi ya kalli ahalin gidanshi ya kara samun nutsuwa a cikin ranshi, a kullum kara godewa Allah yakeyi da ya hada shi da Aisha da kuma sauran matanshi masu fahimta da lura, Zama yayi a tsakiyarsu ya kalli Atika yace "Barka da zuwa cikin Ahali na, nayi matukar farin cikin jin zamu samu jininki a cikin zuri'ata, ina miki fatan Allah ya sauke ki lafiya, daga nan sai mu tafi can kasarku da dan da zaki haifa.. Ameen matan shi suka ce cike da farin cikin addu'ar, kallon Maryam yayi yace "Malama Maryama ku koma can gefe ke da kannenki zamuyi magana da iyayenki, mikewa sukayi cike da ladabi suka koma wata tabarmar a kusurwar dakin Saude matar Hardejo ta uku, Aisha ya kalla yace "mun kusa samun siriki, cike da farin ciki laure tace " Alhamdulillah, wanene ke son Maryama? Bala, Bala ne ke sonta, dazu ya turo mahaifinshi, na kuma ce na bashi, cike da farin ciki dukka matan suka ce mashaa Allahu, Allah yasa alkhairi, Allah ya basu zuri'a dayyaba, Ameen Hardejo ya fadi ya kalli Aisha da taki amsawa saidai murmushi kawai takeyi, ita a dole kunyar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156