Chapter 54
Chapter 54
Allah yayi ma fuskokinsu gamo, ko wanne saida ya tsorata da ganin fuskarkokinsu cikin na juna..... Mrs Tijjani Shattimah...... [18/03 8:06 AM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣8⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Dammmm..... gaban Baffa yayi mummunar faduwa, karasa mikewa zaune yayi har lokacin bai dauke idanuwanshi kan Papy ba, shi din ma Papy hakan take gareshi, saboda tsananin faduwar gaba bakinshi ya gaza furta koda kalma daya ne, Hafeez dake bayansu ya tsuguna zuciyarshi wasai saboda a yau yana tunanin warwarewar SARK'AK'IYAR da ya shiga watanni bakwai da suka wuce, kallon Baffa yayi hade da dan taba kafadunshi yace "Baffa wannan shine Papy wanda nake zaune a gidanshi a Gombe, a razane Baffa ya dawo hayyacinshi yace "au to madallah, an gode fa, Papy bai amsa shi ba ya zauna sosai zuciyarshi sai kai kawo take, ko tantama bayayi wannan mahaifinshi ne da Anni ta dade tana fada mishi, kamannin sun wuce kamanni kawai, tabbas akwai jini mai karfi a tsakaninsu, gaishe da Baffa yayi hade da tambayar jikinshi, Goggo ce ta iya amsawa babu inda a cikin jikinta bai saki ba, saida sukayi kusan minti biyar a zaune babu wanda ya sake magana, kowa da abun da yake tunani a ranshi, karfin Hali Baffa yayi dan ya gama hange hangenshi a yan uwa yasan babu wanda ya rage mishi na kusa, sannan yasan dai bashi da wani ďa banda wanda ya binne da hannunshi, kuma yasan bai taba yin aure a wani guri ba bare har yayi tunanin ya barta da cikinshi, wannan abun al'ajabin kamanni sun yi yawa, bazai iya jure barin shi a ranshi ba, dole yana bukatar sanin daga inda halittar nan mai tsananin kama dashi ya fito, kallon Papy Yayi yace "dan nan idan bazaka damu ba ina so inyi maka tambaya, takalma da safa Baffa ya cire ya gyara zamanshi sosai a kan tabarmar, ganin yatsun kafarshi ya kara daga hankalin Ma'u, shin meke shirin faruwa ne?, magana Baffa zai fara-- tayi saurin katseshi tace "daga mutum yazo gaisheka sai ka tsareshi da magana, ka sani ko sauri yakeyi, Murmushi Papy yayi yace "babu komai karki damu, ko bai tsayar dani ba nima babu inda zani domin akwai wani al'amarin da yake shirin faruwa, wannan al'amarin zai fitar da rayuka da dama cikin tunanin da suka shekara da shekaru suna yinshi, bude baki tayi da niyyar sake yin magana Baffa ya rigata da cewa "nasan kaima kana cikin zullumin da nake ciki, duk wanda ya ganmu ni da kai yasan jini daya ne saboda kamanni, wasu ka iya cewa yan biyu ne saidai yanayin tsufan da jikin shine kadai ya banbanta, dan Allah ina son ka fada min wanene mahaifinka dan inason sanin ko inada wani sauran dan uwa wanda kaddara ta boye min shi, ina son sanin inda mahaifinka yake dan inje mu gana, in baya raye to dan Allah ka bani tarihin shi wanda zai iya warware min komai, Papy baiyi magana ba ya fito da wayarshi, dannata yayi hade da karata a kunnenshi, "Hello Maimunah, hadani da Anni a waya, Papy na...., Ruwaidah ta fadi murya a shake, "Mama na, kuka kike yi? Kukan ta sake fashewa dashi kamar zata tsaga wayar, rage murya yayi yace "wanene, daina kukan and tell me, M-a-mi ce ta fadi tana ajiyar zuciya, tsaki yayi a hankali, yasan abin da aka mata bai taka kara ya karya ba, "yi hakuri Mamanah, jeki kai mata inji dalilin saki kuka, da dan gudunta ta tashi taje kitchen inda Mami da mai aikinsu ke kwashe mangyadan da ta zubar, a darare tace "Maami Papy ya kiraki, kwafa tayi ta goge hannunta a jikin tsumma ta karbi wayar, yana jin sallamarta yayi saurin amsawa, ba tare da jin dalilin kukan Ruwaidah ba yace "ina Anni? tana bacci lafiya dai ko, mami ta tambaya cike da zullumi, ajiyar zuciya yayi yace "lafiya kalau Maimuna, gobe da safe ku shirya guraren tara zan kira Badamasi yazo ya taho daku kaduna, zama Mami tayi gabanta na tsananta faduwa tace "Dan Allah ka fada min abin da yake faruwa, ina JAMAL da HAFEEZ?, murmushi yayi cike da tsokana yace khairan in shaa Allah ruďaďďiya, ke dai ku shirya kinji, gyada kai tayi har lokacin gabanta bai daina faduwa ba... Kallon Baffa yayi bayan ya ajiye wayar yace "Sanin abubuwan da ka tambayeni wannan sai maihaifiyata tazo, domin nima ban san kaina ba, tashi nayi na ganni a hannun mahaifiyata ba tare da uba da yan uwa ba, ni kadai na rayu a gabanta, tare muka sha wahalhalun rayuwa, na dai san a kullum tana fada min ina da uba, amma bata san inda yake ba, A lokacin da Ma'u na tsaye to tabbas da ta kai kasa, kokarin mikewa takeyi Papy yace "inna dawo ki zauna ayi komai a gabanki, yau da za'a bincika zuciyata a gani to tabbas da an gano tafi takarda haske, kallon shi Ma'u tayi tace "ďan nan ina ganin dai kamanni ne, dan mu nan bamu da da namiji ko daya, sannan duk wasu y'an uwa namu na kusa duk sun mutu, kasan Allah yana iya halittar mutane masu kama da juna, akwai su da dama sab--- katseta Hafeez yayi cikin girmamawa yace "Goggo wannan ya wuce kamanni kawai, akwai jini mai karfi, ki duba girman makarantarmu duk daliban dake ciki ace dani kadai ya shaku har ya kaini gidanshi cikin iyalinshi, sannan kuma idan kika ga Jamal da Ruwaidah a nan ne zaki tabbatar da su ďin jinin mu ne, Daka mishi tsawa Goggo tayi "kai dalla rufe mana baki, manya na magana kana yi saboda tsabar rashin kunya, tashi ka fita kaba mutane guri, mikewa Hafeez yayi yana fadin kiyi hakuri, harara ta bishi dashi har ya bacewa ganinta sannan ta dawo da kallonta kan Papy tace "to bawan Allah mun gode da ziyara, sai anjima, sake gyara zama Papy yayi yace "Inna, bazan boye miki ba, barin gidannan a guri na sai da daddare, sannan gobe da wuri zanzo domin kuwa ina hango cikar burina na sama da shekaru arbain da doriya zai tabbata, cike da faduwar gaba ta kalli Baffa da ya kasa dauke idonshi a kan Papy, yanayin maganarshi, da komai irin nashi ne, gayu, gogewa da yarinta ne kadai ya banbanta su, taba shi Goggo tayi tace "lokacin Sallah ya kusa tashi ka shiga kayi alwala, da sauri Papy ya kalli agogon hannunshi yace "uku da kwata ne yanzu Inna lokaci baiyi ba, tun Goggo na daurewa kar ta fara nuna mishi halinta, har saida ya kaita bango ta dakawa Baffa tsawa tace "ya tashi su wuce daki, wannan mutumin in ba aljani bane to maye ne, jiki a sanyaye Baffa ya tashi yace ma Papy "yaya Sunanka, da sauri papy yace "Abdallah" nan Baffa yayi ajiyar zuciya yace "ba SAIFU bane, Ma'u ba saifu bane, duk tunanina shine shiyasa na cika da tsoron ya za'ayi wanda ya mutu ya dawo, nasan ni na binneshi da hannuna, kallon Papy Goggo tayi tace "kaji ko, dan Allah tashi ka fitar mana a gida, kuma karka sake zuwa kaje can ka nemi ubanka.. Nan tsakar gida suka barshi zaune yana ta nazarin abubuwa, kodai da gaske bashi bane mahaifinshi, sai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156