Chapter 50
Chapter 50
magani, bai jira amsa ba ya fita, magunguna ya siyo na mura kala kala kamar zai bude shagon su, bayan ya biya kudin ne ya dubi yawan maganin, sai a sannan ya fahimci yawansu, murmushi yayi yace "cire min wadanda suka fi kyau, emergency, karba yaron yayi ya cire mishi masu kyau hade da rubuta yadda za'a sha su, barin mishi sauran kudin yayi ya fito ya shiga motar, Mikama Husnah maganin yayi, kafin yayi magana wayarshi ta fara ringing, tada motar yayi ya daga wayar, "Sweet heart, kunya ce ta kama Nadeeyah tayi saurin kunshe bakinta, hirarshi ya dinga yi yana fada mata yadda yayi missing dinta, cike da shagwaba kamar bashi bane mai mugun tsare gida yace "yaushe zaki dawo, gidan is empty witout u darling, basu jin abinda ake cewa a daya bangaren sai ji sukayi yace "Noo i won't accept that from u, in baki dawo ba this week zan bar school ba kowa in biyo ki, ita dai Husna burgeta yayi sosai na yadda yake kula da wacce ta kyautata zaton budurwarshi ce ko matarshi, kallon ledar tayi taga magungunan mura, murmushi tayi ta kalleshi bayan ya gama wayar tace "Sir kaima mura kakeyi, bai kalleta ba yace "ni lafiyata kalau, na siyo miki ne in mura ta kamaki kisha, murmushi tayi dan ta gane Nadeeyah ya siyo mawa tace "bana fatan Mura, saidai nagode sosai zan bawa yar uwata ita murar ta kamata, gyada kanshi yayi yace "kin kyauta, daganan bai kara magana ba har ya kai kofar gidan da ta nuna mishi, godiya Husnah tayi mishi ya amsa yana dan mata murmushi, cikin sanyin murya Nadeeyah tace "Mun gode Allah ya saka da alkhairi, Ameen yace a cikin zuciyarshi, a fili kuma murya can kasa yace "baki da matsala in kinyi failing test ko? It's well, na lura ai karatun bai dameki ba, yadda yayi maganar ba tare da ya kalleta ba ya dan bata mata rai, murda kofar tayi ta dauki school bag dinta tace "nasan bazakayi failing dina ba, ni nayi failing, shiyasa zan duba mistakes dina in gyara a exams, tana kaiwa nan ta rufe kofar ta fara tafiya, murmushi Husna tayi tace "haka take sir, ko cutarta akayi zata dauki kaddara tace haka Allah ya rubuta, mun gode sosai, itama ta bude kofar ta fita, kallo yabi Nadeeyah dashi, ji yayi kara samar mata special guri a cikin zuciyarshi, zai tada motar kenan yaga sun tsaya jikin motar da tazo shiga gidansu, dariyarta mai kyau ya hango, nan ya shagala da kallonta, bai kula da maganin da Husna ta manta dashi ba saida ya tada motar, yana gani yayi saurin kashewa ya fito da maganin yayi hanyar shiga gidan, da yake gate din a bude yake ya hangosu tsaye da wanda ya shiga da motar, sanye yake da uniform din Nysc, akwatinshi Nadeeyah ta dauka yayi saurin matsowa kusa da ita yace "bani yayi miki nauyi, kin bashi tayi tace "a'a yaya Musaddiq babu wani nauyi, kama gefen yayi yace "to mu kama, ni kaina yayi min nauyi bare ke, har sun kusa shigewa parlon mai gadin ya kwala ma Husna kira, a tare suka waigo suka ga Uncle Tahir a tsaye a wajen gate, ledar ya mikawa mai gadin yace ya ba Husna ya juya ya tafi gurin motarshi, haka kawai yaji zuciyarshi ta rike Musaddiq, ya rasa dalilin da yaki alakanta mu'amalarsu a matsayin yaya da kanwa, shiga motar yayi ya fara tukata a hankali kamar baya san barin layin..... Mrs Tijjani Shattima..... [13/03 9:58 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣6⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Magungunan Musaddiq ya karba yace "waye baida lafiya, "Nadeeyah ce yaya, Husnah ta fada tana tura kanta cikin parlon, kallon Nadeeyah yayi yace "yaushe kika fara ciwo, cikin muryar mura tace "jiya, akwatin ya kwace a hannunta yace "shan ruwan sanyi da kuma A.c, sam bakwa kula da lafiyarku, ga hancinki nan duk ya zuge yayi ja, Husna da ta ji me yace tace "walhy yaya laifin Badar ne, kasan a kasa Nadeeyah take kwana, kuma Badar ta kure a.c, bargon da take rufa kuma ta jikashi, da ta gane ina matsa ma Nadeeyah ta kwanta sai ta fara kwanciya tana cike gurin ta barmin guri kadan, kasan ko school zamu bata hada mota damu, saidai aje akaita a dawo a dauke mu, cike da mamaki Musaddiq yace "kuma Mummy ta sani, a'a bata san tana kwana a kasa ba, amma tasan ba tare muke zuwa school ba, ajiye akwatin yayi a kasa fuskarshi ta bayyanar da bacin ranshi, kallonshi Nadeeyah tayi tace "dan Allah kar kayi ma mummy magana, zaman lafiya yafi komai, wata rana zaka ga kamar ba'ayi ba, tausayi ta bashi matuka na yadda take magana, maganin ya mika mata yace "je ki ci abinci kisha maganin sai ki kwanta, sorry kinji, gyada kai tayi ta wuce dakinsu, tun daga kofa tayi karo da takalmin Badariyya, tattaresu tayi ta ajiyesu a mazauninsu, sannan ta dauke jakar makarantar itama ta ajiyeta a gurin zamanta, tana cire kaya ta hada da na Badar ta zuba a washing machine, sannan ta fito ta karbi na Husna, bayin Husnah ta bita ta tayata zuba ruwa da sabulu ta murda tace "suje suci abinci, duk abinda sukeyi Badar na kallonsu tana game a waya, tsaki taja tayi juyi ta cigaba da abin da takeyi, sam bata da masaniyar dawowar Musaddiq, duk zatonta motar malam Ali ce ta shigo, shiyasa bata fito parlon ba, Abinci suka zuba suka ci sannan tasha magani, a parlon suka kwanta Husna ta kunna tv, tun suna hira sama sama har bacci yayi gaba da Nadeeyah.. Yana gama shiryawa shima ya fito parlon, bai nemi abinci ba saboda baya jin yunwa, zama yayi kusa da Husnah yana tambayarta abubuwan da suka faru bayan tafiyarshi service, labarai ta dinga bashi na yadda Badar da su Anty Raudha suka sa Nadeeyah a gaba, ba kamar ma idan Anty Radiya tazo, ta dinga kakalo aiki kenan tana sata kuma mummy tayi ta kallonsu bata cewa komai, Allah yaya abin da akeyi ba'a kyautawa, abin haushin ma shine in mukaje gidan Goggo, in kaga yadda suke mata sai kayi mata kuka, sai fa in Daddy na nan ne take samun sauki, Anty Rally ce kadai in tazo zata fita yawo damu ta siyan mana abu iri daya da Nadeeyah, yawancin kayan sawanta ma Anty Rally ke dinka mata, jinjina kanshi yayi yace "ashe dai har yanzu wannan zumununcin namu bai daidaita ba, ashe har yanzu bamu zama daya ba, kallon Nadeeyah yayi cikin tausayawa yace "Ya Allah ka kawo ranar sauyi cikin rayuwar wannan baiwar taka, taga jarabawa iri iri kuma duk ta dangana, ya Allah ka rangwanta mata... Suna zaune a gurin har aka kira la'asar, kin tashinta sukayi saboda kar kanta yayi ciwo, masallaci ya fita dan zuwa yayi sallah, ita kuma Husnah ta wuce dakinsu, tana shiga Badar ta fito parlon, jin kamshin turarenshi ya tabbatar mata da dawowarshi, shekeke ta kalli Nadeeyah tana baccinta hankali kwance, kitchen ta shiga ta dauko swan mai sanyin gaske a fridge, ko dar bata ji a zuciyarta ba ta bude ruwan taje saitin kunnen Nadeeyah ta kwarara iya karfinta, wani
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156