Chapter 29
Chapter 29
in daina jin wadannan abubuwan da nake ji, gyara zama malam yayi ya mishi bayanin addinin Allah da duk abinda Allah bayaso, sannan ya daura mishi da cewa "ta yiwu Allah ya yafe maka saboda kayi abubuwan da kayi a baya cikin rashin sani, kasan Allah baya kama mutum da laifin da baida masaniya akai, sannan sharadin tuba, sai ka tabbatar in ka daina ji da ganin abin da kake gani bazaka sake komawa cikin aikata sabo ba, '""Bazan sake ba malee"" ya fadi da sauri, ni kadai nasan irin wahalar da nasha, to Alhamdulillah Hardejo ya fadi yana murmushi, sannan ya fara koyar dashi kalmar shahada da kuma istigfari, ya horeshi da yin istigfari kafa dubu a kullum saboda yana kankare zunubai, sun dade tare yana koya mishi abubuwa zuciyarshi na samun nutsuwa, ita dai Gambo zama tayi kamar gunki tana kallon sabon mutum a gurin danta, da yake ita din mace ce mai son danta, da duk abin da yake so nan take itama tayi mubaya'a, malam Hardejo ya cigaba da fadakar dasu akan abubuwan da Allah keso da wanda baya so..... Rayuwar Atika a gidan Baffa, Rayuwace da ta fara yinta kadaran kadaham, sam ma'u bata kishi da ita saboda sanin yanayin da sukayi auren, da fari ta fara bijirowa da cewa tunda yanzu Shaho yayi nadama ya shiryu mai zai hana Baffa ya saketa ta koma ta auri shahon, a lokacin taga ainihin Fillo Hardejo, dan saida yayi mata wuzu wuzu sannan ta maida hankalinta, da yaga ta nutsu ne yasa shi ya koma lallashi, ya cemata ta sani ko tuban muzuru Shaho yayi, irinsu ba'a gane tubansu har sai an musu gwaji mai karfin gaske, cikin hikima ya kwantar mata da hankali, samm baya ko kaunar hango rabuwar Atika da Muhammadu saboda yasan ko babu rayuwarshi Atika zata zame ma dan uwanshi alkhairi..... **** Ashe dai ma'u baki da hankali ban sani ba kuma ban gama tabbatarwa ba sai yau, yanzu har wannan tsaleliyar budurwar Baffa zaice baze kusanceta ba kuma ki yarda, naman zomon da ta gasa takai bakinta tace " Haire am niko nake da hankali, an fada miki hakanan na sakankance, ai ba sakarai nake ba, nasan yadda Baffa yake da sakarcin nan akan mace wata rana zai iya kusantarta a bayan ido na, shiyasa na aika can garinmu gurin "Iyan gida" ta amso min gadalin mu na ukari, sannan ta hada da duk wata mallakar maida mace namiji a idon Baffa, yaushe zanyi wannan wawancin a barni in zama yar kallo, ai dole na mike tsaye ko dan yadda Hardejo ke nuna min ita din kamar yarshi take ta jini, shewaaa sosai sukayi hade da tafawa, dariya Bingel tasanya itama ganin mahaifiyarta na dariyar babu kakkautawa, dariyar tata ta sake sasu wata dariyar hade da kai naman zomon na karshe cikin bakinsu.... Kallonsu Atika tayi itama tayi murmushin saboda bata san abun da suke fadi ba, kara gyara goyon boddo tayi tana jijjigata tana mata wakensu na larabawa, tunanin Ateek ta tafi wanda ya zame mata tamkar shan ruwa dan kullum, Ya Allah ka dubamin Ateek.. kalmar kadai take ta maimatawa cikin harshenta na larabci...... Mrs Tijjani Shattima...... [02/03 9:59 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣5⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* *RUBUTACCEN AL'AMARI* Sauri sauri yake yi dan samun sahun gaba a cikin masallacin kofar gidan Hardejo wanda Barde da Gambo iyayen shaho suka gama gininshi, dabe ne na kasa suka bada kudi aka hada karfi da karfe aka ginashi cikin gaggawa, Shaho ne tsaye a kofar shiga yana sallama ga duk wanda yazo shiga, sanin muhimmacin Sallama da yayi, da kuma irin ladan da ake samu ya sanyashi a koda yaushe fara yin ta ga duk wanda yayi tozali dashi.. Bayan idar da Sallah Malam Hardejo ya zauna a tsakiyarsu ya fara janyo musu wa'azi mai kashe jiki, kowa a cikin massalacin saida ya nutsu, zuciyoyinsu suka narke matuka da tsoron Allah, a cikin wa'azin ya sako musu muhimmacin aure da kuma hakkin da mace take dashi akan mijinta, "Hakkin duk wani namiji ne ya ciyar da matar shi, Hakkinshi ne ya tufatar da ita, sannan Hakkinshi ne ya sauke duk wata bukata tata, lissafo bukatun yayi cikin hikima, sannan ya tunatar dasu azabar da mutum zaisha a gurin ubangiji in bai sauke wannan hakkin ba, wa'azi sosai yayi mai cike da tausayi da al'ajabi... jikin kowa a sanyaye suka tashi suka fita daga masallacin, matsowa Bala (shaho) yayi kusa da malam yace "Assalamu Alaikum, a sanyaye Malam ya miko mishi hannu suka gaisa hade da yiwa juna murmushi, kayi hakuri Bala, yau jikina baya min dadi, bazamu samu damar yin karatu ba, murmushi Bala yayi yace "Babu matsala Malam, Allahn Hardejo ya kare ka da lafiya, dariya malam yayi yace "Allahn mu gaba daya, gatan mu, kuma gatan zuri'armu.... ●●●●●●●●●● A hankali ya tura kofar gidan ya shiga, wa'azin Hardejo keta kai komo cikin kwakwalwarshi, zama yayi a tsakar gidan kan wani dakali, tunani ya dingayi na yadda zai sauke hakkin marainiyar Allah akanshi, ga kuma alkawarin da yayi wa ma'u shima kuma Allah baya son mai saba shi, yana cikin wannan tunanin ne ruwa ya kece a kanshi, mikewa yayi da niyyar wucewa daki sukayi karo da Atika ta fito ta kwashe kayan da ta wanke a kan duwatsun shanyar gidan, matsawa baya yayi da sauri yana mayar da numfashi, rab'awa tayi ta wuce ta kwaso kayan, kafin ta gama kwashe kayan gaba daya ta jike sharkaff, kallonta Baffa ya tsaya yi shima ruwan ya jikashi sosai, saida ta gama kwashewa tazo wucewa yaji ta dan gogeshi da kaya sannan yayi firgigit ya gane ta wuce, yasan ma'u bata gidan, tana can gidan inna wuro tare da yara, da jan kafa ya bita dakin, cikin kudurar ubangiji ya fara jin wani abu na fusgarshi game da ita, shaukin da bai taba jin irinshi ba ya shiga, a hankali ya kusanceta ya taimaka mata ta rabu da jikakun kayan jikinta, tuni labarin ya canza zuwa wani sabon babi na shafin labarin.... Mikewa yayi jiki a sanyaye zuciyarshi kamar an sauke nauyin da yakai girman dutsen mambila, ita kuwa azaba ta hanata yin kuka, dakyar ta iya tashi, abinka da mutumin "da" shi ficewa yayi yaje bayi ya wanke jikinshi ya barta a cikin dakin, A daddafe ta fito tsakar gidan, tunanin yadda zatayi ta rabu da wannan azabar da take ji take yi, dakyar ta iya ďiban ruwa ta wuce bayi, tsugunon ma zame mata aiki yayi amma haka ta daure dan dai kawai ta daina jin zafin gurin, tana watsa ruwan sanyin tayi wani irin ihun azaba, tsakar gidan ta fito tanata safa da marwa tana zubar da hawaye tana kiran sunan Allah, Azaba kam iya azaba Atika tasha ta a wannan ranar domin ko abincin kirki babu a gidan gashi babu abin da zata iza wuta ta sa ruwan zafi, A haka tayi tsaye tanata kuka a gurin har dare ya farayi, surutun Ma'u ta fara ji sama sama a kofar gidan, nan hankalinta ya fara kwanciya, tasan zata samu ko dan abinci ne taci, sallamaa dai Amarya, hannu tasa ta karbi Boddo dake kuka jikinta jike da fitsari, saboda duhun dake tsakar gidan Ma'u
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156