Chapter 84
Chapter 84
kamar zata buga ta kira Hajjara, nan suka kulla duk shirinsu na kawar da Abdallah domin a cewarta in ta kuskura ta yarda aka nadashi sarki kuma yayi aure wasu familyn zasu zama iyalan sarki su kuma su zama yan kallo.. Makudan Silalla ta bawa Hajjara ta shirya tafiya can kauyensu Sassoun burum, cikin sa'a, da kuma lokacin akwai wani boyayyen al'amari wanda Allah ya boye a rayuwar Adamu Hajja ta samu bokan da yayi nasarar yin aikin, ya kuma bukaci auren Hajja, a take ta yarje mishi domin dama tana bukatar yin auren, bayan sun kammala aikin ta koma agadez ta karbo sha tara ta arziki daga gurin fulani Ayyu.... Cikin Kuka Hajja tace "kudi ne wadanda basu rufe shekara ba suka kare suka barmu da wahala, saboda muhimmacin Amana naki yarda in watsa asirin, amma fa duk wata tana bibiyar asirin kamar yadda mijinta ya koya mata.... Shuru gurin yayi bayan Hajja tayi shuru, sai kuka dake tashi a gurin, Murya a dashe Sarki yace "Bazan manta ranar karshe da na ganshi ba, ranar muna tsaye a lambu muna hirar sarautar da za'a bashi, yana tsinko ma shareefah yalon lambu, a kasa ya zubar da yalon ya nufi kofar fita, yana kurewa ganina na bishi na hango Haroun da abokanshi, suna Kallon Adamu ya gifta gefensu babu wanda ya gaisheshi bare ya tambayi inda zashi shi daya... Ashe abubuwan da akayi mishi ba kanshi kadai ya tsaya ba har dukkan mutanen agadez, koda na koma gida babu wanda ya tambayeni shi kowa harkarshi yakeyi har sarki bai damu da tambayar inda yake ba domin babin yareemah shafewa yayi a cikin garin agadez, Ya Allahu ina zanga Adamu, ina zan ganshi.... Ganin kukan bazaiyi musu ba suka fita a gidan Hajja domin babu wani hukunci da zasuyi ma musaka irin ta, hukuncin Allah ma ya isheta, Motocin sarkin sassounburum suka shiga suka je gidanshi suka sallemashi sannan suka wuce airport din katsina domin hawa jirgi zuwa agadez, saboda sassounburum tafi kusa da garin daura.... Shawara suka yanke na baza malamai ayi adduar da Allah zai kawo sanadin haduwarsu in har yana da rai, domin basu yarda da maganar Hajja na ya mutu ba.... *Bawan Allah Adamu tun a cikin garin Agadez ya fara watangaliliya, duk inda ya wuce babu wanda ke ganeshi bare har ya bashi girman dan sarkin da suke matukar so, har ya samu motar da zataje zinder, a can ma saida yayi shekara biyu yana wahala, irin masu shigowa daga kawo kaya daga kano zuwa zinder su yabi zuwa nigeria, A kano ma saida ya shekara daya da watanni har Allah ya hadashi da Alh jogana, nan ya kaishi gidanshi dake kaduna dan yi mishi gadi, anan ne ya bude shago har kaddara ta hadashi da Suwaiba, barin agadez, zuwanshi kaduna, haduwarshi da Suwaiba, rabo ne na ya'ya, wanda Allah swt ya boye wasu al'amura a garesu, Tabbas haihuwar da namijin da suwaiba tayi a farko rubutaccen al'amari ne, mulki na Allah ne, shine yake bada aronshi ga wanda yaso koda kuwa almajiri ne.......* *A gurguje na takaita muku labarin Adamu saboda mu kai inda muke san zuwa a kan lokaci* _Akwai shagalin biki a page fifty...... ku cinka_ Mrs Tijjani Shattima.... [01/04 9:50 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣1⃣ By *Aysha Ya'u kurah* *EMIR PALACE SASSOUN BOROUM* Sarkin sassoun boroum ne tsugune a gaban sarki "TIDJANI YALLO" yana mika gaisuwa kamar yadda sarakuna keyi wa na gaba dasu, bayan sun gama gaisawa aka cika kayayyakin abinci da sha a gabansu saboda girmamawa, babu abinda Sarki Tidjani da Shareefah suka kalla, bare har su kai ga cin shi, cikin nutsuwa da kasaita suka gabatar da dalilin zuwansu, nan da nan aka wakilta dogarai dan suje can rugar Haldo su nemo Hajja yar Ruga su taho da ita, da yake rugar bata da nisa da gidan sarki sai gasu sun dawo, cikin girmamawa suka ce bata da lafiyar da zata iya zuwa, daka musu tsawa sarkin sassoun burum yayi yace "maza su koma su dauko ta, dakatar dasu Shareefah tayi hade da mikewa tace "su barta kawai, su zasu isa zuwa gidanta, Duk yadda sarkin sassoun burum yaso nuna musu kaskancin zuwa rugar Haldo hakan bai hanasu zuwa ba, a cewarsu su suke nema a gurin ta, ya zame musu dole su ganta yau kota halin kaka..... Wani irin wari dakin Hajja ke fitarwa, warin ma marar misaltuwa, tana kwance a kan tabarmar da takai rabi saboda cinyewa, dakyar aka iya dagota ta jingina da wani sudadden pillow, "wani dan kara tayi saboda wani ciwo da yayi mata rami a mazaunanta, yaron dake kula da ita ne ya sa mata wani pillow a gurin ciwon, saboda tausayin halin da Hajja ke ciki ya sanya Shareefah sharar kwalla, Dakyar muryar Hajja ta iya fita tace "sannunku da zuwa, da kai suka amsa hade da gyara zama akan daddumar da dogarai suka shimfida musu, saboda son jin abun da ya kawosu ko kyankyamin dakin basu ji ba, "Daga ina ranka ya dade? Hajja ta fadi baki na rawa, Shareefah ce ta fada mata sunanta da dalilin da yasa suka zo gurinta, bude ido Hajja tayi sosai ta kure shareefa da ido, *SHAREEFAH YALLO* kece? murmushi Shareefah tayi tace "nice, ashe ma kin sanni, kuka Hajja ta fashe dashi tace "farin sani, ni na raineki tun kina tsumma, nafi shekara ashirin a gidanku tun kafin a haifeki, ashe zan sake ganinki, rabona da ke inaga in banyi karya ba yakai shekara arbain, dan tun kina shekara goma sha biyu na bar agadez, ashe ina da rabon sake ganinki ta karashe da kuka hade da tari, Cike da kosawa sarki Tidjani yace "sai hakuri Baba, dama haka rayuwa take, kuma duniya fadi gareta, wata rana in da rai dole a hadu, yanzu gashi sanadiyar mutuwar UMMU AYYU Allah ya kawo mu gurinki, yanzu bamu da isashen lokaci zuwa mukayi ki fada mana labarin da Ummu tace ke kadai ce kika san dashi, labarin YARIMA, wani kukan ne ya kufcewa Hajja a zuciyarta tace "yau labarin da yayi shekara da shekaru a kunshe, hali yasa zata bayyana shi, labarin da ya zame mata tamkar kwai a cikin zuciyarta saboda riritarshi, ajiyar zuciya tayi tace "babu mamaki fitar labarin nan ya zama silar samun warakarta, Nuni tayi ma yaron dake kula da ita wani gurin dake cike da kaya, mikewa yayi ya dauko wata jakar saka ya mika mata, hannu na rawa ta karbi jakar ta dauko wani ginin mutum mutumi wanda yake kewaye da kawunan mutane babu adadi, Saboda tsananin tsorata saida shareefah ta rungumi kafardar mijinta, abun ba karamin tsoro ya bata ba kuma ya daga tsigar jikinta matuka, yadda aka yanyame shi da wasu abubuwa kamar kwari yasanya har sarki jin tsoro amma kadan, wani guri ta daga a gefenta, inda take ajiyar abubuwa, nan ta mike dayar ruwa nabin bayanta ta fita tsakar gidan ta daki wani dakali dake kofar dakinta, nan take gurin yayi rami, hannu tasa ta ciro layu masu tarin yawa, daga can kasa ta hango kurciyar da suka binne shekara da shekaru kwance babu rai ga layu kewaye da ita, a gigice ta ciro kurciyar da duk wata sai ta bata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156