Skip to content

Chapter 139

Chapter 139

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

tsari daga sharrin zuciya ya raba jikinshi da nata, da sauri ta wuce ciki tana maida numfashi da sauri sauri..... Cikin kwanaki uku soyayya mai karfi ta wanzu a cikin gidan wanda har saida duk mutanen gidan suka gane, Amal da ta sawa ranta auren Taheer tayi gaggawar cirewa dan tasan dama tuni Nadeeyah yake so, a take tayi wa kanta addu'ar samun duk abin da zai zamo mata alkhairi.... Ga mamakin Nadeeyah sosai Anty Saude ta sake mata ta dinga lallabata tana nuna mata kauna ta musamman.. Hakan ba karamin daďi yayi ma Taheer ba.. A daren ranar alhamis suna zaune dukkansu a parlor Taheer na yanke ma junior farce yana tsoma baki cikin hirar tasu.... Kallon shi Anty Saude tayi tace "Munyi magana dazu da kawu Tidjani, na faďa mishi maganar zuwa neman aurenka, na sanar dashi ina son ayi komai cikin sati ďaya dan banasan wata matsala ta biyo baya, Mikewa Nadeeyah tayi ta wuce ďaki da sauri, Dariya yayi yace "Sai su taho ranar sati dan mu haďu tunda gobe zamu tafi, ni zanso ma a ďaura auren a ranar Mommah tunda babu wani shirin da ya rage.. Buďe baki tayi cikin mamaki haďe da sakar mishi dakuwa, Dariya yayi sosai ya dauki Junior suka wuce dakin Nadeeyah...... ******* *Kaduna* Toshe hanci Raudha tayi kamar zatayi amai, hawayen idonta ta share tace "Ya Allah ka sassauta mana, mun wahala iya wahala, mun gina ramin mugunta mun auka ciki, wuyar da muka so wata tasha ita muka haďiya har na tsawon shekaru takwas... Audugar da ta share ruwan ciwon dake fita a jikin Goggo ta yar a bola.. mistakely ya sauka cikin waken da Radiya ke gyarawa, Wata ashar ta sakar mata haďe da mikewa tace "wallahi bazan dafa abincin ba, ni na gaji wallahi, duk ku kuka jamin, yanzu ga Shamsu ko waiwayata baya yi, yana can ya koma Italy da zama shi da yarinyar da tayi min aikatau, wannan wace irin masifa ce.. Mummy dai jinsu kawai takeyi tana kokarin daga Goggo ta daurata akan pour, Kafin ta daurata har ta saki kashin a gurin, a sittin su Raudha sukayi waje dan dama su ba aikin sukeyi ba, Shekara uku kenan Goggo na fama da ciwon da babu wanda yasan irinshi, asibiti sun gaji sun maido ta gida, wani katon rami mazaunanta yayi saboda zama, ga wasu ramuka da jikinta yayi yana fitar da ruwa mai matukar wari, Mummy ce kullum ke hidima da ita saboda a yanzu komai ya fice mata a rai, gara tayi wannan, ta yiwu Allah ya yafe mata sanadiyyar hakan, Dakyar ta iya wanke mata kashin ta canza mata gurin kwanciya, saida ta gyara dakin tsaff sannan ta fita dan shan iska.. Tana zama taji sallamar su Papy da ahalinshi da su Anni, nan fa ta mike ta dinga musu maraba, yadda ta fita hayyacinta sai wanda dama ya santa shi zai ganeta, duk da yanzu suna samun gata domin Raliya na taimakonsu sosai.. Bayan sun duba jikin Goggo suka koma dayan dakin suna ta hirar yaushe gamo, Awan su ďaya sai ga su Hafeez da 'yayanshi uku.. Suwaiba, Adam, da Autan wanda yake hannu mai sunan Papy, sai Husna da ta zama big madam, Dakin suka shiga suka gaida su Mummy sannan suma suka zauna akayi hirar dasu.... Daddy ka dawo ne? akwai abin da nake so mu tattauna.. Raliya ta faďi cikin girmamawa kamar yana gabanta, "Eh Raliya, muna kaduna, jibi zan koma lagos kina iya zuwa gida yanzu, Cike da jin daďi ta mike ta fara shirin zuwa gidan su Goggo dan ta taho dasu Mummy, dama tun last week ta gindaya ma Anty Reemah karyar Goggo ta shiga coma tazo su dubata.. Anty Reemah ta tabbatar mata yau suna nan tafe, saida ta kaiwa su Fadeel abinci makaranta sannan ta wuce gidan Goggo... Taji dadin ganin su Papy, nan take ta shirya plan din da yasa duk suka shirya tafiya gida.. Goggo kaďai aka bari a gida sai Rilwanu dake zaman jiran zuwan iyayenshi.... Suna isa gidan Mummy ta fara hawayen bakin ciki da dana sani, lallai in baka godewa Allah ba to tabbas zaka godewa azabarshi, A darare ta karasa cikin gidan saboda gudun wulakanci a gurin mamallakin gidan... A lokacin da yaji sallamar su yana parlor yana kallon news, da sauri ya mike ya taro Papy yana faďin maraba da proff, bismillah shigo, bai lura da mutanen bayanshi ba saboda yadda yayi kewar ganinshi shekara da shekaru, Saida suka nutsu cikin gaisuwa sannan ya kalli sauran mutanen parlon, yana sauke idonshi kan su Mummy mood dinshi ya canza gaba ďaya, Cike da masifa ya mike zaiyi magana yaji Sallamar su Anty Reemah, nan take fuskarshi ta sauya yace "A'a yau gida yayi albarka, Allah ya sanya alkhairi a wannan taron.. kafin a amsa da Ameen Muryar little Nadeeyah ta karaďe parlorn, *HABIBI*, *YAA OMRI*.. Ta sama Musaddiq ya leko dan jin muryarta kamar amsa kuwwar speaker.. ganin parlon a cike yasashi sakkowa da sauri.. Da ita ya fara tozali rike da kugu tana mishi wani irin kallo, karasowa yayi ya dagata sama ya dinga juyata tana kyalkyala dariya, Wani wawan duka Hilal ya kai mishi a baya sai a sannan ya dakata ya rungumeshi, haka nan ya tsinci kanshi cikin farin cikin da ya rasa na meye, Cikin parlon suka karasa suka gaiggaisa da mutane, Mummy ce kadai ya gimtse fuska kafin ya gaisheta, shi dinma dan yaga su papy ne a zaune da Anty Reemah dake yawan matsa mishi, hirar yaushe gamo palon ya karaďe dashi, Sudai su Mummy suna ra'be kamar Mamma Suwaiba lokacin da take da rai bata da galihu, *Allah kenan*, babu yadda bai iya ba..... Murďa kofar dakin sukaji anyi an shigo ba tare da sallama ba, Yara biyu farare cikin kayan fulani kafarsu tayi butu butu suka shigo suna ta ďari ďari da kafarsu dan kar su faďi, can bayansu kuma mace ce ta shigo naďe da zani akanta hannunta rike da kullin dankwali, sai wani namiji fari da riga budaddiya da layu a duk jikinshi har kunne, Babu wanda a cikinsu ya gane Badariyya, sai Mummy wacce ko a cikin dubu ne zata tsamo ta, "BADARIYYA! "Na'am Mummy ta amsa haďe da fashewa da kuka, karasowa inda take tayi ta rikota haďe da yin wurgi da kayan hannunta, kowa a cikin parlon da ido ya bita cike da mamaki, Zama yaran sukayi a gefe suka matse juna su a dole suna tsoron tiles, Shi kuwa Yareemah Suhail gani yakeyi duk ya fisu muhimmanci a parlon, Hafeez ne kaďai yayi mishi kwarjinin da zai iya tsuguna mishi, direct gaban Hafeez yaje ya tsuguna har kasa irin gaisuwar da akema sarki yace "Ina wuni ranka ya dade, Shi Hafeez abin ma tsoro ya bashi, da sauri ya maida kafarshi baya yace "Ga iyayenmu can su ya kamata ka fara gaisarwa, "Duk cikin runkar nan babu mutum mai muhimmanci, daga kai saini, ranka ya daďe, sauran duk mu ya kamata su gaisar... Kallon mahaukaci duk sukayi mishi suka maida dubansu kan Badariyya wacce take kuka tana neman gafara, Labarin abinda ya faru da ita ta fara basu, har yadda ta taimakawa su Mummy suka raba Nadeeyah da Musaddiq saida ta

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156