Chapter 110
Chapter 110
ya ganmu, tafiya ya fara yi yace "in an ganmu ai da matata aka ganni, ni bacci nakeji, muje ki tayani, Sun kusa step din karshe Mummy ta fito daga ďakin da ta kwana, kokarin sauka Nadeeyah tayi ya sake riketa yana dariya, "Wai kunyar ki take ji! runtse ido Nadeeyah tayi tace "Dan Allah ka saukeni, a hankali ya sauketa yace "Good morning maa, Cike da danniyar maida danta bawa da taga Nadeeyah tayi tace "morning my dear, "Ina kwana Mummy, Nadeeyah ta faďi bayan ta tsuguna kasa, "lafiya kalau Nadeeyah, ya gajiyarki, "babu gajiya Mummy, ga breakfast can ko nan zan hawo miki dashi, "a'a barshi a can, zan fi jin dadin karin a can, Gefe suka matsa dan bata guri, ta wuce tana tunanin ta inda zata sake bullo musu, ya zame mata dole tayi abun da zatayi yau zuwa gobe dan jibi zata wuce...... Ranar throughout Nadeeyah bata basu wata kofar da zasuyi complain ba, kome zatayi a tsantsane take yinshi saboda bata san abin da zai kara sanya mijinta cikin bacin rai, duk yadda Faida taso provoking dinta taki yarda ta kulata dan bata da lokacinta, Cikin dare suka tashi suka shirya kulle kullensu, sannan daga can wani bangaren da basu masaniya ana taimaka wa aikinsu..... *(Kana Bacci ana maka nasari)* Mrs Tijjani Shattima..... [22/04 8:08 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣2⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Kamar kullum yau ma tun uku saura ta farka dan yin sallar Nafila, wata iriyar kasala ce ta sauko mata wacce ta hanata barin kan gadon, zaune tayi tana gyangyadi har huďu ta gota, da ta gaji da gyangyaďin sai ta ja pillow ta kwanta riris, bacci mai nauyi yayi gaba da ita... A kunnenta aka sallame sallah a masallacin kusa dasu, mikewa tayi jiki ba kwari ta nufi bayi dan yin alwala, sai da tayi minti goma akan toilet tana bacci sannan ta buďe ido da kyar tayi tsarki ta mike ta kunna pampo tayi alwala kamar me tsoron taba ruwan, koda ta fito daga bayin zama tayi a kan kujera tana tuno mafarkin da tayi wanda ya kashe mata jiki matuka, mafarkin ya taba ta sosai dan a iya saninta mafarkin dariya bai taba zama alkhairi ga mai yinshi, bare ita da taga dukkan wadanda suke nuna mata kiyayya kewaye da ita suna kuka ita kuma tana tsakiya tana kyakyata musu dariya mai sauti harda kaiwa kasa, gefe kuma Musaddiq na zaune shima dariyar yakeyi yana kurbar juice, dariyar da sukayi a cikin mafarkin kamar wadanda aka saukar musu da wahayin yinta, haka kukan da su Mummy keyi kamar wadanda suka rasa wani sashi na jikinsu, Anty Reemah, Hilal, Hafeez da Husnah kuwa suna tsaye rai a bace suna masifa kamar zasu ari baki, shigowar Daddy da Papy shi ya farkar da ita... Tunda ya farka ya lura da yanayinta, bai kulata ba ya nufi bayi yayi alwala dan yaga garin har ya fara haske, a yadda ya barta haka ya sameta, wannan karan idonta a rufe yake wani baccin take son sake yi, gyara hannun jallabiyarshi yayi ya zauna a gefenta haďe da taba kanta, a hankali ta buďe ido ta kalleshi, "Har ka idar da sallah? Kwantar da kanta yayi kan kafaďunshi yace "yanzu zanyi, shine baki tashe ni ba ko? Cikin magagi tace "Nima banyi sallah ba, bacci ya hana ni, zaunar da ita yayi sosai yace "whatt, ba dai bacci ba, sai dai shaiďan, tashi maza muyi sallah, Mikewa tayi jiki ba kwari tabi bayanshi sukayi Sallar, suna idar da sallar taji duk wani baccin da takeji ya tafi, sai dai kasalar da ta kasa barinta, Bayan ta gaisheshi ta fita dan zuwa kitchen haďa ma Mummy break fast, karar tv da taji shi ya bata tabbacin akwai mutane a parlon, a nutse ta karasa saukowa ta nufi parlon dan duk tunaninta Mummy ce ko Anty Radiya, turuss... tayi tana kallon Faidah wacce ke kwance daga ita sai mini skirt da wata yar riga wacce iyakarta cibi, kwanciyar da tayi bai boye komai na surar jikinta ba, kirjinta kuwa ya bulluko kamar zai faso rigar kayan kirjin su fito, Saman ta kalla taga ko Musaddiq ya biyota, ganin baya gurin yasata saurin karasawa gurin Faidah rai a bace, gaba daya tsoron da takeji nata ta nemeshi ta rasa, "Baiwar Allah, gidan nan ba na mata bane zallah akwai maza, dan Allah ki tashi ki canzo kaya, Mikewa Faidah tayi tana murmushi tace "Ba matsala bane dan ya ganni a haka, musulunci ma ya yarda in kana neman auren mace ta bayyana maka surar jikinta kafin ka aureta, karki damu dani je kiyi cookun ki, Ran Nadeeyah in yayi dubu to duka sun baci, baki yin kanshi yakeyi, bata san lokacin da bakinta ya furta cewar "Ke bakiyi kama da tsarin matan mijina zai ruďe akan surarsu ba, bance shi nawa bane ni kadai, amma fa ki sani ko zaiyi wani auren sai dai ya nemo wacce ta fini ba wai ya koma baya ya dauko wacce bata kaini ba... "Ahayyyyyeee..... Faidah ta faďi tana tafa hannu, wacce ta fiki me? kyau? Kudi? Asali ko me? Ko dayake banda lokacinki, nasan a cikin abun da kike takama dashi nafiki su 99%, Asali shi kadai zaka fini ka cuceni, Faďa min menene asalinki? Waye mahaifinki wanda ya kamata ya zamto ado a gareki? Waya sani ma ko irin yan fashin shanun nan ne aka buďe musu wuta suka arto nigeria neman maf--- Zazzafan Mari Nadeeyah ta sauke a fuskar Faidah wanda saida ta dauki lokaci mai tsawo tana tattaro confidence dinta kafin ta iya aiwatar dashi, sauke marin yayi daidai da sakkowar Mummy daga sama... "Kaii kaii, me nake gani haka? Mari fa? Mummy ta faďi tana karasowa har tana missing steps kafarta na gurďewa, ko kallonta Nadeeyah batayi ba dan a lokacin ji takeyi kamar ana hura wuta a cikin zuciyarta, Kuka Faida ta fashe dashi ta rungume Mummy wacce ta rufe mata jiki da hijab din da ta sakko dashi, "Subhanallahi.. Nadeeyah me yayi zafi haka harda mari, in baki dubi cewa ba sa'arki bace ai kya duba cewa ita bakuwarki ce, "Bakuwarku dai Nadeeyah ta faďi cikin ficewar hayyaci, ranta yayi matukar baci, ba'a taba aibata mahaifinta har haka ba, abun ya haďe mata biyu ne, ga kishi ga tabo iyaye, mai hankali ne kadai yasan halin da zuciyarta ke ciki a wannan lokacin, Sakin baki Mummy tayi tace "Ni kike fadama bakar magana, gefenta tabi ta haye sama ba tare da ta kulata ba zuciyarta na tafasa, ta gaji da zaman nan na kaskanci da takeyi, badan tana jin soyayyar Musaddiq har cikin jininta ba wallahi da babu abinda zai hana ta tattara kayanta ta gudu ta bar musu gidan, to bazata iya rabuwa dashi ko na second ba dan tayi matukar sabawa dashi, ta dai ďauki alwashin kwatar ma kanta yanci gurin duk masu neman muzanta ta, dakinsu ta shiga ta sameshi yana baccinshi hankali kwance, key tasawa ďakin ta karaso kusa dashi ta cire hijab dinta ta shige cikin jikinshi taja musu bargon, rungumeta yayi sosai yace "Har kin gama? a shagwabe tace "um um, bacci nakeji, in na tashi zanyi, bai damu ba dan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156