Chapter 108
Chapter 108
hakuri yayana, in shaa Allahu zan gyara, Lumshe idonshi yayi ya sake kankameta yace "shiyasa nake sonki, sosai sosai, rikita ta ya dinga yi da kalamai masu daďin sauraro, Bata gama tabbatar da tana sonshi ba sai da taga yadda Faida take mishi, ya zame mata dole ta dage in ba haka ba tana ji tana gani Faida zatayi sanadiyyar raba su.... Murďa kofar tayi haďe da shigowa ba tare da sallama ba, aiko tayi gamo, dan yadda ta samesu saida tayi dana sanin shigowa dakin, wani irin kishi ne ya taso ya tokare mata zuciya, ji takeyi kamar ta shako Nadeeyah ta kasheta kowa ya huta, Dakyar kafarta ta iya daukarta ta fita waje tana sharar kwalla, ganin haka yasa su Anty Radiya zagayeta suna tambayarta ko lafiya, girgiza kanta tayi tace "aikin nan da kamar wuya, munyi kaďan mu raba wannan auren, wannan aikin mutum ďaya ce zata iya shi, *uwa*, mahaifiya ce kaďai keda wannan karfin, in har son rabasu da gaske kukeyi sai kusa mahaifiyarku tazo, ni bazan iya ganin takaici ba, tana kaiwa nan ta wuce daki kirjinta kamar zai faďo kasa.... Assalamu Alaikum... "Ameen wa alaika salam, Shamsuddeen ne yau a office dina, Har kasa ya tsuguna ya gaida Daddy, "tashi tashi, ga guri ka zauna, kuna nan lafiya, sosa keya shamsu yayi yace "lafiya kalau Daddy, "To Madallah, ai haka muke son ji, Cike da kunya shamsu yace "dama nazo kawo maka katin bikina ne, jibi in shaa Allah za'a daura, Duk da abun ya sosa ran Daddy sai ya danne yace "Mashaa Allahu, aiko banji ba, kaii na tayaka murna, Allah ya kaimu, yasa ayi damu, Dabaibayi shamsu ya shiga yace "kayi hakuri Daddy, wallahi banda option ne, nan ya bashi labarin duk abin da Radiya take mishi, sannan ya daura da cewa har yanzu tana lagos gidan Musaddiq bata dawo ba, a gigice Daddy yace "Whattt! Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Tabdijam, nagode sosai shamsu, dubu dari biyu Daddy ya ciro a drawer yace "Dan Allah kayi accepting wannan a matsayin sadaki... Sosai Shamsu ya tausaya mishi kuma ya kara ninka girmanshi da yake gani..... Wacece ma me wannan Sunan? Daddy ya tambaya yana zana takardar dake gabanshi, Hajiya Martai kawata ta Maiduguri, wacce take zuwa duk wani sha'ani nawa ta kwana, "uhmmn sai akayi yaya? Dama mijinta ne ya mutu a sokoto, gobe da wuri za'ayi jana'izarshi, "Ayya, to Allah yayi mishi rahama, sai kin dawo, Cike da murna Mummy tace "nagode kwarai, ka fitar dani kunya, da ido kawai ya bita har ta shige ďaki, ticket din jirgin da Malam Ali ya kawo mata ya juya, bazai taba hanata ba, so yake yaga gudun ruwanta, A gurin yabar ticket din ya mike ya fita waje yana mamakin irin halayyar 'yayanshi, Raliya ya kira a waya ta tabbatar mishi da ita tana gida yanzu ma zata zo gidan, kashe wayar yayi ya kira Reemah, Cike da mamaki tace "Wallahi Daddy bani da Masaniya, yanzu Radiya tana gidan Diku, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Kwantar mishi da hankali tayi ta kuma tabbatar mishi yanzu zata kirata ta sata ta koma gida, "Karki damu Reemah, mahaifiyarku ma ta shirya tafiya, ki barsu kawai, so nake in ga gudun ruwansu, A sanyaye Anty Reemah ta kashe wayar ta faďa ma Papa abinda ke faruwa, duk abinda da akeyi a kunnen Hilal dake gaban system dinshi, Ajiye assignment Hinad tayi ta dawo kusa da Anty Reemah ta bata duk labarin da ta kunso daga gurinsu, ta kuma ce sunce ko sati biyu bazata yi a gidan ba, wallahi mantawa nayi ban faďa ma Yaya Hilal ba, i'm very sure Nadeeyah na cikin matsala, "ya kamata a taimaka mata ASAP mum... Rufe system dinshi yayi ya mike ya nufi sama, number Musaddiq ya nema, saida ya kira sau uku sannan ya ďauka, yadda yaji muryarshi ya tabbatar mishi da abun da yaji, dan a lokacin sun gama zagin Nadeeyah kenan saboda ta shiga kitchen zatayi abinci, Hilal baiyi wata wata ba ya kashe wayar, Number Nadeeyah ya kira, tana tsaka da kuka lokacin, duk tunaninta Zainab ce dan ita ke kiranta kullum da wayar Hilal, Cikin Muryar kuka tace "Zainab kuna nan lafiya, zakiji muryata haka, mura nakeyi sosai, ki gaida su Anty, tana kaiwa nan ta kashe wayar... Wani abu yaji ya taso mishi, tuni ya cire Nadeeyah a ranshi a matsayin macen da yake so, amma tana nan makale cikin ranshi a matsayin jininshi wacce ke yawo a dukkan sassa na jikinshi, waya yayi dan neman visa.. Wurgi yayi da wayar saboda tsabar bacin rai, dan sunce sai nan da 3days saboda jirage na hutu, Safa da Marwa ya dingayi a cikin dakin ya dinga jin kamar yayi tsuntsuwa ya ganshi a nigeria........ Mrs Tijjani Shattima.......! [20/04 7:01 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣1⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Yana hangota ya nufo inda take da sauri cike da murnar ganinta, Yasan zuwanta zai sanya su Anty Radiya su bar mishi gida ya samu sakewa da matarshi, baisan komai daga gurinta yake fitowa ba, "I missed u alot Mummy nah, "Missd u more little, nace bari inzo inji ko nayi ma Nadeeyah laifi da har yanzu bata daukar wayata, nan take wani abu ya ďarsu a cikin ranshi, "kodai da gaske ne dasu Anty Raudha ke cewa saboda yana tsananin sonta ne yasa bata girmama mahaifiyarshi da yan uwanshi, hango yadda Faidah take yi musu biyayya yayi a zuciyarshi yace "ina ma abar sonshi ce haka da yan uwanshi, Kauda abun yayi a ranshi yace "Sorry Mummy, wayarta nada matsala ne, kullum sai ta ce in gaishe ki, "Au to Madallah, Muje inga gidan ďana, gaskiya little nayi matukar farin cikin auren nan da kayi, kaga yadda ka canza, Tsaki yayi yace "Dan Allah mummy kice ma Anty Radiya ta koma gida, Cikin dabara tace "dama Radiya bata tafi ba, karka damu tun da nazo tare zamu tafi mu barka ka huta da amaryarka, Cike da jin dadi ya buďe mata motar ya shiga ya tada ta, cike da shauki yake hango su Anty Radiya sun barshi shi kadai a gidan shi da matarshi, so yakeyi ya bata kula ta musamman wanda zai mantar da ita duk bacin ran da ta shiga a farkon amarcinsu, Wani irin sonta yakeji har cikin bargonshi, baisan dalilin da yasa kullum kamar ana dada hura wutar soyayyarta cikin jininshi ba, in ko yana tare da ita jinshi yakeyi a sama kamar su biyun kadai aka halitta a duniyar, Murmushi yayi haďe da karawa motar gudu...... Yana Parking tace "Washh yunwa, da fatan anyi min abinci?.. "Baki da matsala Mummy, Nadeeyah tayi miki abincinta mai daďi, nuna mishi jin daďinta tayi tace "yayi kyau ďan albarka..... Gaurayewa gidan yayi da ihun su, suna kiran sunan Mummy, Kallon gidan tayi cike da jin dadi tace Mashaa Allah, gida yayi kyau little, Allah ya kawo min jikoki suyi ta yawo a gidan sai ya zama complete.. Dariya yayi sosai yana duban ta inda zaiga rabin rayuwarshi, hangota yayi cikin dogon hijab tana sakkowa daga sama fuskar nan dauke da murmushinta mai kyau, Gaban Mummy tazo ta tsuguna ta gaida ta, dagota tayi cike da kissa ta rungumeta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156