Skip to content

Chapter 108

Chapter 108

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

hakuri yayana, in shaa Allahu zan gyara, Lumshe idonshi yayi ya sake kankameta yace "shiyasa nake sonki, sosai sosai, rikita ta ya dinga yi da kalamai masu daďin sauraro, Bata gama tabbatar da tana sonshi ba sai da taga yadda Faida take mishi, ya zame mata dole ta dage in ba haka ba tana ji tana gani Faida zatayi sanadiyyar raba su.... Murďa kofar tayi haďe da shigowa ba tare da sallama ba, aiko tayi gamo, dan yadda ta samesu saida tayi dana sanin shigowa dakin, wani irin kishi ne ya taso ya tokare mata zuciya, ji takeyi kamar ta shako Nadeeyah ta kasheta kowa ya huta, Dakyar kafarta ta iya daukarta ta fita waje tana sharar kwalla, ganin haka yasa su Anty Radiya zagayeta suna tambayarta ko lafiya, girgiza kanta tayi tace "aikin nan da kamar wuya, munyi kaďan mu raba wannan auren, wannan aikin mutum ďaya ce zata iya shi, *uwa*, mahaifiya ce kaďai keda wannan karfin, in har son rabasu da gaske kukeyi sai kusa mahaifiyarku tazo, ni bazan iya ganin takaici ba, tana kaiwa nan ta wuce daki kirjinta kamar zai faďo kasa.... Assalamu Alaikum... "Ameen wa alaika salam, Shamsuddeen ne yau a office dina, Har kasa ya tsuguna ya gaida Daddy, "tashi tashi, ga guri ka zauna, kuna nan lafiya, sosa keya shamsu yayi yace "lafiya kalau Daddy, "To Madallah, ai haka muke son ji, Cike da kunya shamsu yace "dama nazo kawo maka katin bikina ne, jibi in shaa Allah za'a daura, Duk da abun ya sosa ran Daddy sai ya danne yace "Mashaa Allahu, aiko banji ba, kaii na tayaka murna, Allah ya kaimu, yasa ayi damu, Dabaibayi shamsu ya shiga yace "kayi hakuri Daddy, wallahi banda option ne, nan ya bashi labarin duk abin da Radiya take mishi, sannan ya daura da cewa har yanzu tana lagos gidan Musaddiq bata dawo ba, a gigice Daddy yace "Whattt! Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Tabdijam, nagode sosai shamsu, dubu dari biyu Daddy ya ciro a drawer yace "Dan Allah kayi accepting wannan a matsayin sadaki... Sosai Shamsu ya tausaya mishi kuma ya kara ninka girmanshi da yake gani..... Wacece ma me wannan Sunan? Daddy ya tambaya yana zana takardar dake gabanshi, Hajiya Martai kawata ta Maiduguri, wacce take zuwa duk wani sha'ani nawa ta kwana, "uhmmn sai akayi yaya? Dama mijinta ne ya mutu a sokoto, gobe da wuri za'ayi jana'izarshi, "Ayya, to Allah yayi mishi rahama, sai kin dawo, Cike da murna Mummy tace "nagode kwarai, ka fitar dani kunya, da ido kawai ya bita har ta shige ďaki, ticket din jirgin da Malam Ali ya kawo mata ya juya, bazai taba hanata ba, so yake yaga gudun ruwanta, A gurin yabar ticket din ya mike ya fita waje yana mamakin irin halayyar 'yayanshi, Raliya ya kira a waya ta tabbatar mishi da ita tana gida yanzu ma zata zo gidan, kashe wayar yayi ya kira Reemah, Cike da mamaki tace "Wallahi Daddy bani da Masaniya, yanzu Radiya tana gidan Diku, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Kwantar mishi da hankali tayi ta kuma tabbatar mishi yanzu zata kirata ta sata ta koma gida, "Karki damu Reemah, mahaifiyarku ma ta shirya tafiya, ki barsu kawai, so nake in ga gudun ruwansu, A sanyaye Anty Reemah ta kashe wayar ta faďa ma Papa abinda ke faruwa, duk abinda da akeyi a kunnen Hilal dake gaban system dinshi, Ajiye assignment Hinad tayi ta dawo kusa da Anty Reemah ta bata duk labarin da ta kunso daga gurinsu, ta kuma ce sunce ko sati biyu bazata yi a gidan ba, wallahi mantawa nayi ban faďa ma Yaya Hilal ba, i'm very sure Nadeeyah na cikin matsala, "ya kamata a taimaka mata ASAP mum... Rufe system dinshi yayi ya mike ya nufi sama, number Musaddiq ya nema, saida ya kira sau uku sannan ya ďauka, yadda yaji muryarshi ya tabbatar mishi da abun da yaji, dan a lokacin sun gama zagin Nadeeyah kenan saboda ta shiga kitchen zatayi abinci, Hilal baiyi wata wata ba ya kashe wayar, Number Nadeeyah ya kira, tana tsaka da kuka lokacin, duk tunaninta Zainab ce dan ita ke kiranta kullum da wayar Hilal, Cikin Muryar kuka tace "Zainab kuna nan lafiya, zakiji muryata haka, mura nakeyi sosai, ki gaida su Anty, tana kaiwa nan ta kashe wayar... Wani abu yaji ya taso mishi, tuni ya cire Nadeeyah a ranshi a matsayin macen da yake so, amma tana nan makale cikin ranshi a matsayin jininshi wacce ke yawo a dukkan sassa na jikinshi, waya yayi dan neman visa.. Wurgi yayi da wayar saboda tsabar bacin rai, dan sunce sai nan da 3days saboda jirage na hutu, Safa da Marwa ya dingayi a cikin dakin ya dinga jin kamar yayi tsuntsuwa ya ganshi a nigeria........ Mrs Tijjani Shattima.......! [20/04 7:01 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣1⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Yana hangota ya nufo inda take da sauri cike da murnar ganinta, Yasan zuwanta zai sanya su Anty Radiya su bar mishi gida ya samu sakewa da matarshi, baisan komai daga gurinta yake fitowa ba, "I missed u alot Mummy nah, "Missd u more little, nace bari inzo inji ko nayi ma Nadeeyah laifi da har yanzu bata daukar wayata, nan take wani abu ya ďarsu a cikin ranshi, "kodai da gaske ne dasu Anty Raudha ke cewa saboda yana tsananin sonta ne yasa bata girmama mahaifiyarshi da yan uwanshi, hango yadda Faidah take yi musu biyayya yayi a zuciyarshi yace "ina ma abar sonshi ce haka da yan uwanshi, Kauda abun yayi a ranshi yace "Sorry Mummy, wayarta nada matsala ne, kullum sai ta ce in gaishe ki, "Au to Madallah, Muje inga gidan ďana, gaskiya little nayi matukar farin cikin auren nan da kayi, kaga yadda ka canza, Tsaki yayi yace "Dan Allah mummy kice ma Anty Radiya ta koma gida, Cikin dabara tace "dama Radiya bata tafi ba, karka damu tun da nazo tare zamu tafi mu barka ka huta da amaryarka, Cike da jin dadi ya buďe mata motar ya shiga ya tada ta, cike da shauki yake hango su Anty Radiya sun barshi shi kadai a gidan shi da matarshi, so yakeyi ya bata kula ta musamman wanda zai mantar da ita duk bacin ran da ta shiga a farkon amarcinsu, Wani irin sonta yakeji har cikin bargonshi, baisan dalilin da yasa kullum kamar ana dada hura wutar soyayyarta cikin jininshi ba, in ko yana tare da ita jinshi yakeyi a sama kamar su biyun kadai aka halitta a duniyar, Murmushi yayi haďe da karawa motar gudu...... Yana Parking tace "Washh yunwa, da fatan anyi min abinci?.. "Baki da matsala Mummy, Nadeeyah tayi miki abincinta mai daďi, nuna mishi jin daďinta tayi tace "yayi kyau ďan albarka..... Gaurayewa gidan yayi da ihun su, suna kiran sunan Mummy, Kallon gidan tayi cike da jin dadi tace Mashaa Allah, gida yayi kyau little, Allah ya kawo min jikoki suyi ta yawo a gidan sai ya zama complete.. Dariya yayi sosai yana duban ta inda zaiga rabin rayuwarshi, hangota yayi cikin dogon hijab tana sakkowa daga sama fuskar nan dauke da murmushinta mai kyau, Gaban Mummy tazo ta tsuguna ta gaida ta, dagota tayi cike da kissa ta rungumeta

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156