Skip to content

Chapter 10

Chapter 10

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

me nayi,? Dan Allah kiyi hakuri, Wai me yake faruwa ne? kuka mamma takeyi iya karfinta gunin ban tausayi, kallonta Malam Adamu keyi hawaye na zuba ta gefen idonshi a ranshi yana mai Jin dadin kukanta domin ko ba komai zata samu saukin nauyin dake cikin ranta, sai da tayi mai isarta ta share hawayenta, ta kalli Nadiya dake kuka tana share hawayen idon mahaifinta tace "tashi maza kije kiyi wanka kiyi sallah, bari in nemo miki abin da zaki ci, Nadiya ta share hawayenta tace "ki barshi kawai, bari nayi wanka in daura mana, zauna ki kula da baba, Gyada kai mamma tayi kawai, dan bata son tasan abinda ke faruwa, Nadiya na shiga bayi mamma ta fita shagon Tasi da ya kara cika ba kamar da ba, Indomie da Kwai ta ce ya bata, dakyar ya bata dan yana bin ta bashin kusan dubu daya da dari hudu, da sauri tayi cikin gidan, ta hado yayi, ta sauke ruwan dumin da ta daura ma mijinta, ta iza wutar ta daura Indomien cikin karamar tukunya.. Wanka da sallah Nadiya tayi, ta saka doguwar rigar deep blue material mai gajeren hannu ta shan iska,, ko mai bata shafa ba ta daura jar hula a kanta, kyawu mai sirri da cikar budurci suka bayyana a tare da ita, wani irin kyau Nadiya ke dashi marar hayaniya, wanda ya kara fitowa saboda dan hutu da kuma rufin asirin da suka samu,, kusa da Mamma ta tsaya tace "sannu da aiki mamma, ina Zainab? "Tana islamiyya,, mamma ta bata amsa tana tura leda cikin murhun, Tambayoyi ne cure cikin zuciyar Nadiya, ta rasa wanda zata tambaya ya bata amsarsu, ko zata mutu tana tambayar mamma bazata amsa koda tambaya daya cikin tambayoyin da take dasu ba,, Daki ta shige gurin mahaifinta da ya fara bacci numfashin shi na fita dakyar, Kure shi tayi da ido tana addu'a tana tofa mishi, Mamma na kwashe Indomien zainab ta shigo gida da gudu jikinta yayi futu futu, "mamma yunwa nake ji, zainab ta fadi murya a sarke saboda tsabar gajiya.. kallon Indomien mamma tayi tace to bari kiyi wanka ko? , noke wuya tayi kamar zatayi kuka tace cikina na murda min, je ki wanke hannu kizo muci, Nadiya ta fadi tana fitowa daga daki, rungumeta zainab tayi tace "yaushe kika dawo anty? Dazu kina islamiyya, da fatan kina karatu a makaranta, Nadiya ta tambayeta tana shafa kanta,, gyada kai zainab tayi tace Sosai ma, kin kawo min chocolates, Kumatunta Nadiya taja tace "eh yana jaka ta, maza wanko hannu muje muci abinci.. Mamma kinci abincin ne? Nadiya ta tambaya idonta kyar akan mahaifiyarta, mamma dake kofar daki tace "eh munci sosai, bansan zaki dawo ba da na ajiye miki, zainab da ta kai Loma kamar zata shake tace "mamma yaushe kika ci abinci?, bayan tafiya ta makaranta, shine kika cinye baki ajiye min ba, mamma ta saci kallon Nadiya, tayi saurin maida kallonta gurin zainab tace ba gashi kina ci ba, maza kici karki kware, Nadiya dai hannu kawai take juyawa cikin abincin har zainab ta kai karshen shi harda sid'e kwanon, meya ke faruwa mamma??? Tambayar ta fito a bakin Nadiya cikin rashin sanin fitowarta, me kika gani? Mamma ta amsa ta cike da fargaba, rarrafowa Nadiya tayi ta dafa cinyarta tace "mamma boyemin abin da ke damunki bashi da amfani, nasan bani da maganin shi amma atleast zaki ji sauki in kin fada min..... ********** Ohh ni!!! "wacce iriyar rayuwa ce wannan? d'aki kaca kaca sai kace ba na mata ba, mummy ke mitar tana tafe tana tsintar kayayyaki a kasa da takalma, Husna dake kwance tana duba littafi tace "kema kin San ko aikin waye mummy, "ni gaskiya na gaji wallhy, canza min daki za'ayi, bazan iya wannan rayuwar ba, kwance take cikin matsatstsiyar jar riga da yellow mini skirt, Gashinta Parke a tsakiya da yellow ribon, kunnenta dauke da earpiece alamun bata ma San me sukeyi ba, kada kanta kawai takeyi tana bin wakar hade mutstsuka santala santalan kyawawan kafafuwan ta, kafarta mummy taja a hankali, juyowa tayi tana cire earpiece din kunnenta cike da rashin da'a tace "ya akayi ne mum" mummy ta ajiye kayan makarantar ta a gefen gado tace "babu komai baby na, kinci abinci dai ko? gyada kai Badar tayi alamar eh sannan ta juya ta mayar da kanta kan pilo tana cigaba da jin waka hade da chatting,, "hmmmm" kawai Husna tace ta sakko daga kan gado tace "mummy zanje gidan Anty Raudha, "me akeyi?? mummy ta tambaya tana gyara ma Badar skirt dinta, "birthday din Amal diyar Anty Laura, Husna ta bata amsa, gyada kai mummy tayi tace "too jira Badar ta shirya ku tafi tare, hanyar bayi husna ta nufa tace "bata San me muke fadi ba sai ki fada mata dan gaskiya ina shiryawa zan tafi, Badar da ke saurarensu da kunne daya tace "kifi ruwa gudu, ke kika damu da local partys, duk inda kika ji sha'ani jiki na rawa kin tafi, 'anyways baki yar a kasa ba, maida earpiece dinta tayi ba tare da ta kalli mummy ba ta cigaba da danne dannen waya, Husna kuwa bayi ta shige cike da bacin ran irin rainin da Badar ke ma mummy, abin da ke kara bata ranta bai wuce yadda mummyn ko a jikinta ba, duk rainin da badar ke mata sai dai tace "yarinta ke damun ta, ita kuwa komin kankantar abu in tayi mummy ta dinga masifa kenan kamar zata ari baki, watsa ruwa tayi cike da takaici da tunani iri iri.... Mrs Tijjani Shattima... [04/12 09:47] Meela Adeel: ZUMUNCINMU A YAU By Aysha Ya'u Kurah 1⃣2⃣ A hankali take maimaita kalmar "innalillahi wa Inna ilaihir rajiun" ruwan hawaye na tsere akan kumatunta, kirjinshi take dannawa tana share kumfar jinin dake fita a bakinshi, nishi yakeyi Sama Sama yana kakari da karfi, magana yake fisgowa daga can kasan makoshinshi, muryarshi ta kara karfi tamkar amsa kuwwar loud speaker, "kiyi Hakuri suwaiba! , kiyi Hakuri da rayuwa, nasani ban jiyar dake dadin duniya ba saboda talauci na, gashi zan tafi in barki cikin rayuwar talaucin da babu mataimaki, kiyi hakuri suwaiba, Allah kadai yasan tanadin da yayi mana a lahira, ki cigaba da hakuri da duk yadda kika tsinci kanki, nasani kin iya kanki, ki rike yaran nan,, basu da kowa a duniya sai ke, ki fadawa Hafizu in ya dawo na yafe mishi,! na yafe mishi,! na yafe mishi,!!! Idonshi da yake lumshewa ya daga Sama, ga azabar zafin fitar rai ga kuma radadin barin iyalanshi cikin yanayi na rashin garkuwa, Ya Allah! ka iya ma zuri'ata abin da bazasu iya yi ma kansu ba, LA' ILAHAILLALLAH----- kukan mamma ya karu saboda tsabar firgici, A gigice Nadiya ta farka daga gajeren baccin da ya dauketa saboda jiyo kukan mahaifiyarta, fitowa tayi daga daki da sauri har tana turgude kafa ta karasa dakin baban su, kasa shiga tayi saboda hangoshi da tayi damke da karfen gadon dakin hade da hannun mamma, yana haki da sauri sauri. Juyawa tayi ta fita a gigice, "wake ta takalmi ko mayafi a wannan lokacin", gudu takeyi da iya karfinta, ita dai tasan jefa kafafuwan ta kawai takeyi, bata ma San akan abinda suke sauka ba,

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156