Chapter 56
Chapter 56
Harira, wacce ta kunso cikin shege aka korota daga garinsu ta dawo nan, ashe kai ka kunsa mata, gashi dai kamanni sun bayyana min komai, wallahi kaji kunya, ta karasa fadi tana haki.. "innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai Baffa da Papy ke fada, ganin shurun da Baffa yayi ya kara hassala Ma'u ta fara surfafa masifa da bala'i, babu inda baya rawa a jikinta, da dai Anni taga shuru bazai taimakesu ba tace. "Wallahi tallahi ban taba koda magana dashi ba... shuru Ma'u tayi tana hararar Hanne tana fadin rainin hankali, uban wa zaki rainawa hankali? "gyara zama Anni tayi ta kalli Baffa tace "in ka yarda dani ka bani dama inyi maka bayanin komai, idonta ta mayar kan Goggo tace "in kikaji labarin abinda ya faru, da kuma yadda ya faru ni nasan gode min zakiyi ba zargi da zagi ba, ni ko a yau Allah ya dauki raina walhy naji dadi saboda zan cika buri na, kullum bani da tunanin da ya wuce ta yaya zan wankewa Abdallah zuciyarshi, ta yaya zan hada shi da mahaifinshi, nasan duniya tana da fadi wata rana ina da yakinin Allah zai amsa min addu'ata, sai gashi ta dalilin Hafeezu adduar da na dade ina yi Allah ya amsa... Alheri danko ne... Kallon su Radiya dasu Hafeez tayi tace "dan Allah ko yaran nan zasu dan bamu guri, "babu inda zasu, Ma'u ta fadi tana tafa hannu, kallon Jamal Mami tayi tace "dauki Ruwaidah ku tafi mota, noke wuya tayi tace "um um, zare mata ido Mami tayi zatayi magana Anni ta dakatar da ita, "zo takwara, zo kuje ku siyo min Goro kinsan kin fishi wayau naki yafi kyau, Jiki na rawa ta mike zata wuce ta taka kafar Radiya, da karfi ta hankada ta cikin ihun azaba saboda tsinin takalmin tace "ke makauniya ce? baki ta bare ta fara kuka idonta kyar akan Radiya, da sauri Hafeez ya ja hannunta suka fita yana rarrashinta, Harara Mummy ta sakarma Radiya tace "sai kace kina yi da sa'arki, turo baki tayi tace "mummy zafi wallahi, "tashi ki bamu guri dalla,mummyn ta fadi a hassale, da sauri Goggo tace "babu fa inda zata, gyara zaman ki, abun kunya ce suka kwaso suji kunyar su kadai, Girgiza kai Anni tayi tace "babu komai ma, zauna! labarin an yishi ne, ba kirkirarre bane, kaddara ce.. Kamar yadda kika sani ni kanwar Harira ce, mahaifina asalinshi dan Gombe ne, mahaifiyata ce yar jalingo.. Allah ya jarabceni da soyayya da dan kanin babanmu, mun dade tare dashi, kullum in na fita tallan nono a gurin yake zama har ya kare, mu tafi gida.. wata rana nono na yayi kwantai, yakai ni dare, a hanyar mu ta dawowa gida kaddara ta afka mana, kaddarar da dan adam bai isa ya tsallake ta ba, kaddarar dake sanya rayuwar budurwa da iyayenta cikin mawuyacin hali... kaddarar da ta sanya Mahaifina rasa rayuwarshi... Bayan an fahimci ina dauke da ciki, saboda tsabar kunya irin ta fulanin "da" mahaifina ya kashe kanshi ta hanyar fadawa cikin teku, a cewarshi bazai iya fuskantar jama'a ba.. mahaifiyata da kishiyoyinta suka sani a gaba, bani da katabus cikin kauyenmu, ko kofi na taba babu wanda yake dauka, haka in na fita gari an dinga darewa kenan, shi kuma wanda yayi min cikin an nemeshi ko sama ko kasa an rasa, daga baya ne muka samu labarin mutuwarshi, nan fa na cire duk wani tsammani na samun mijin aure, saboda tsabar tsana da iyaye da yanuwana suka min na fita hayyacina na kare na lalace, mahaifiyata ma kunya ta sanyata ta rame, saida abin ya isheta tace "in shirya in tafi jalingo gurin mahaifiyarta, To acan ma hakan take domin kuwa saida na gwammaci zama a Gombe da zaman jalingo, duk ranar jumma'a sai Yakumbo kakata ta turani Gembu gidan Harira saboda gudun kunyar jumma'a, tana tsoron kar mutane su shigo su ganni, gaba daya yan uwa sun tsane ni ta ko ina, bani da gurin shan iska... wata ranar jumma'a mai cike da ban alajabi da tsoratarwa, Jumma'ar da manta ta ga yan uwan mutanen kauyen Gembu abu ne mai matukar wahala.. Tun cikin dare nake jin kaina kamar bani ba saboda yadda cikina ya dinga murda min, a hakan Yakumbo tace in fito in wuce Gembu, tun a hanya cikin ke murda min har al'amarin yaso fin karfina, cikin ikon Allah cikin ya lafa min har muka shiga cikin kauyen, a daddafe na karasa cikin kauyen nayi gamo da tashin hankalin da yasanya cikina kadawa har kafata ta gaza daukata, ina kallonka sanda ka dauko matarka da wata mace kuna gudu, da rarrafe na bi bayanku har nazo lungun shiga gidanku, nan gaba daya karfina ya kare, haihuwar ta taho min gadan gadan, Cikin ikon Allah na haifi 'yata mace, dankwalina na cire na nadeta dashi hade da mahaifar, koda na duba ta na dinga jijjigata na tabbatar bata raye, anan ne nayi kuka sosai har muryata ta dashe, ban kara sanin inda hankalina yake ba saboda zubar jinin da nakeyi.. Iska mai karfi ce ta taso a kauyen wacce kafin ruwa ya sauka saida ta dauke gidaje, wannan iskar ita ta farkar dani nayi saurin mikewa da gawar yata na fada cikin gidan ka, koda na shiga babu kowa a gidan sai kasar da ke tashi tana rufe ko ina na gidan, Daki na shige da sauri, har cikin dakin kasar ke shiga saboda iskar ba ta wasa akeyi ba, Iskar na lafawa ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya, A nan ne naji ihun jariri daga waje, da sauri na fito na iso gurin na hango dan Mala'ikan Allah cikin zani kwance a kirjin mahaifiyarshi, Share hawayen idonta tayi tace "Allah shi ke raya Matacce a lokacin da yaso, in ba Allah ba waye zai raya wanda kasa ta rufe idonshi, ko da na dagoshi jini ne ke fita daga cikin cibiyar da ba'ayi mata yanka da kyau ba, nan take nayi daki dashi na gyara yankan cibiyar na daureta da tsumma, ruwan bai tsagaita ba sai can gurin magriba, yana tsayawa na kunshe yata na mayar da ita cikin gawar da Allah ya nuna ikonsa akanta, A tare na rufesu da kyau saboda ko yadda aka zuba kasar wata rana ruwa ka iya dago gawar saboda sam kabarin baiyi zurfi ba.. A lokacin ne na fahimci wani abu guda daya game da cikin da nayi, wannan abu kuwa shine bak'in zare mai shara shara wanda babu mai ganinsa sai ubangiji, wannan zaren kuwa shine zaren kaddara! kaddarar rainon Abdallah ta nuna Baffa tace "danka, ita ta sani na dauki ciki har sanadiyar shi nazo har wannan kauyen.. Da fari a kullum ina tunanin ni kadai ce Allah baya so a duniyar nan da ya jarabceni da yin cikin shege a cewar bahaushe, haduwata da Abdallah na fahimci dama nazo duniya ne domin shi, koda na koma gida Yakumbo tayi tayi ta rabani dashi, a lokacin ne na nuna musu nima ina da hakki akan dana, tunda ni na haifeshi, babu wanda ya taba samun labarin bani na haifeshi ba, A lokacin da na bijirewa yakumbo sai ta koreni tace in tafi gurin uwata ita bazata iya da wannan abun kunyar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156