Skip to content

Chapter 17

Chapter 17

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

ta matso da kunnenta kusa da bakin Nadeeyah, rada tayi mata a kunne wanda Allah kadai yasan me tace mata, sai ko Zainab ta kyalkyace da dariya hade da rungume Nadeeyah, tace "dagaske kikeyi Anti? Gyada kai Nadeeya tayi tace "eh, hawayen da ta boye ne ya fara bin idanuwanta, ta kankame zainab tana zubar dasu ba tare da ta bari ta gansu ba, wayyo mutuwa.....! @ Mrs Tijjani Shattima....! [07/03 6:31 AM] fareedah: ●ZUMUNCINMU A YAU● 1⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Had'a kayayyakinsu cikin jaka Nadeeyah keyi, idanuwan nan nata sai ambaliyar ruwa suke, Hafeez ke tayata had'a kayan yana labarta mata abubuwan da suka gifta tsakaninshi da iyayensu a yan watannin da suka shude, jan numfashi yayi kamar karamin yaro, daga zuciya har idaniyar shi zubar ruwan hawaye sukeyi, "yan kudaden da suka fara shigowa hannuna su suka ruda ni, na canza abokai, kullum bani wancan club bani wancan, ban tsaya nan ba har sai da na koma harkar mata, tun ina boyewa, su Baba basu sani ba har takai ga mata har gida suke biyoni, bazan taba manta daren da zan bar gida ba, Baba ya fito zai tafi Sallar asuba ya jiyo muryata da SAILUBA yar gidan Hinde mai tuwo, ranar a daki na ta kwana, Koda Baba ya bude kofar, Sailuba na kwance a jikina, duk yadda na kai ga tureta in suturta jikina ta kafe ta danneni, na kasa tabuka komai, saida Baba ya juya, nayi karfin halin turata na mike nasa jallabiya nabi bayanshi, Kuka na tarar dashi yana yi a tsakar gida, a tare muka iso inda yake ni da Mamma, ajiye butar hannunta tayi ta fara tambayarshi dalilin zubar hawayenshi, bai kai ga yin magana ba Sailuba ta fito da daurin kirji da kayanta a hannu tana sawa tana fadin "Zo ka sallameni Hafeezu in tafi kar a nemeni a gida, wani irin juwa Mamma ta ji a tsakiyar kanta, bakinta da kyar yake iya furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun, daki Baba ya jata ba tare da ya dubi inda na ke ba, koda na biyosu ciki da sauri Baba ya dakatar dani yace "fitar min a daki da kazantar dake jikinka, tafi kaje ka sallameta, ka wadata ta da duk wani nau'i na jin dadi tunda kaima ta jiyar da kai dadin, ubangiji Allah ya shiryar dakai Ameen, Har na iso kofar dakina ina jiyo sautin kukan mamma, Baba yana ta bata hakuri.. Da kudin da ni kaina bansan yawansu ba na sallami Sailuba, sai na wuce nayi wanka nayi sallah, shaidan ya dinga raya min in bar gidanmu in tafi can inda babu wanda yasanni, tunda ina da kudina inje in ci karena babu babbaka, a haka nabi umurnin zuciyata na shirya kayana tsaff na sasu a mota, Zainab na gani a kofar shagon Tasi, na bata dubu biyar ta kaiwa Mamma, nace ta fada musu nayi tafiya, tun kafin ta shiga gidan na shige mota nayi gaba, a tunanina duniyata zatayi kyau tunda babu mai samin ido, ashe tafiyar da zata kashemin zuciya ta barni da dana sani har karshen rayuwata nayi... ya karashe maganar cikin matsanancin kuka... Takalman Zainab Nadeeyah ta tura cikin ledar dake hannunta, wacce tun fara bata labarin ta budeta da niyyar zuba takalman, ledar ta jike sharkaff saboda hawayen da ke sauka a kanta, kallon Hafeez tayi tace "Yaya Allah yayi mana jarabawa mai zafin gaske, rayuwa ce yanzu zamu fara ta wacce bamu san inda zata kaimu ba, ka godewa Allah da yasa suka yafe maka, sannan kaji tsoron Allah, ka nisanci duk wani aikin alfasha, kasani duk abinda zakayi yanzu za'a tada su Mamma ace su tashi suga dansu, shin irin wannan tarbiyar suka baka, kasani yanzu babu wani wanda zai fada maka gaskiya, rayuwa ce zakayi ta ta rashin mafadi, kai da kanka zaka zama mafad'in kanka, ni da zainab kuma duk inda zamuje na tabbatar bazamu rasa mai kwaba mana ba, kaga mummy yanzu ta canza, matsalata daya itace "Bad----- shigowar Hinad cikin dakin ya katseta, ta kallesu tace "Nadeeyah Mummy tace kuyi sauri, hawaye ta share ta dauki karamar jakar, Hafeez ya dauki babbar suka fito sukayi waje, loda kayan sukayi a motar Hafeez, sannan kowa ya shiga mota, Hinad da Nadeeyah motar Hafeez suka shiga, makota suka kewaye su Nadeeya anata musu fatan alkhairi, Tasi ya leko ta windon motar, ya miko mata ledar lolli pop idonshi cike da kwalla yace "ki ajiyewa Zainab, Allah ya hadaku da alkhairi Nadeeyah, Wani kukan ta fashe dashi na tuno memories dinsu na lokacin da dukkan iyayenta suna da rai, da irin kara kainin da sukayi tsakanin gida da shagon Tasi, Tasi ya bada gudunmuwa mai karfi a rayuwarsu, bai taba kazawa gurin tallafa musu da bashi da kuma kyauta ba, kallonshi tayi yana share hawaye tace "mun gode Tasi Allah ya saka maka da gidan aljanna.... Islamiyyar su Zainab suka biya dan daukota, motar Mahmoud suka tarar a kofar makarantar, kafin suyi parking suka hango Musaddiq rike da hannunta sun fito daga ciki, baya ya bude mata suka shige, Mahmoud yaja motar suka wuce, Bayansu Hafeez yabi, zuciyarshi ta dan rage zafi da fargaba saboda yasan in shaa Allahu Musaddiq da mahaifinshi bazasu bar kannenshi cikin garari ba..... A katafaran gidan "Alhaji Mukhtar Kyari dukka motocin sukayi parking, Ta window Badariyya take lekensu daya bayan daya, Husna da dawowarta daga saloon kenan ta fito daga bayi tana kallon Badariyya a jikin Window tana leke, murmushi tayi ta zira Hijab dinta ta fito tsakar gidan tana ma mummy barka da dawowa, dan ita ba gidan rasuwar take kwana ba, gidan Anty Raudha take bin ta su kwana, yau ne kadai bata je gidan rasuwar ba taje saloon dan wanke kanta, Anty Radiya da Anty Raudha suka kalleta cike da shakiyanci suka ce "Amarsu ta ango, cikin rashin fahimta ta waiga bayanta taga babu kowa tace "wacece haka? Dariya suka kwashe da ita suka ce ke mana! Zatayi Magana Anty Reemah tace "wani irin sakarci ne wannan, ku dan matsa daga can mu wuce sai ku cigaba da shakiyancin tunda sa'arku ce Husnan, darewa sukayi ta wuce ita da Anty Raliya, harara Raudha tabi Raliya dashi tayi tsaki tana kunkuni a ranta, "su in an barsu mutanen kirki, Radiya tace "manta dasu dallah, taja Husna sukayi ciki, mummy tayi kamar bata jinsu tace ma Nadeeyah su kamo kayan su shigo, A d'arare ta dauki jakar ta fara tafiya, kama gefen jakar Hinad tayi suka karasa cikin parlon, wani irin faduwar gaba Nadeeyah taji, idanuwanta suka ciko da kwalla, tuno abubuwa mabanbanta da suka faru da mahaifiyarta na rashin dadi ta dingayi, wani lungu ta zauna inda suka saba zama da mahaifiyarta in sunzo gidan..... Labulen windon Badariyya ta saki kirjinta kamar zai fado saboda bakin ciki, bata hango Nadeeyah ba, amma ganin Zainab a gurin Musaddiq suna magana yana dariya ya tabbatar mata da lallai su Nadeeyah sun dawo gidansu da zama, bata karasa tunaninta ba taji an shigo dakin ana dariya, Cikin kaguwa Husnah tace "Anty Raudha tell me, waye amaryar plss, Radiya ta ajiye yaronta Fadeel a kan gadon tayi hanyar bayi tace "ke mana, kece amaryar Hafeez, wata dariyar suka sake kecewa da ita sannan Radiya ta

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156