Chapter 140
Chapter 140
faďa musu sannan ta roki gafararsu domin ita yanzu rayuwarsu ba irin tata bace... Cike da takaici Daddy yayi daya sanin haďa zuri'a da jinin Ma'u, Wani irin huci ya furzar na bakin cikin irin halayyarsu, mugunta ma har ga kanka sai kayi ta domin biyan bukata, tirrr da dabiyar karnuka irin tasu Goggo ya faďi da kausassar murya... Ke Badariyya... ,tashi maza ki fitar min a gi---- Jiniyar da sukaji ne ya sanya shi yin shuru domin sauraron daga inda jiniyar ke fitowa.... A take Yareemah Suhail ya durkusawa Hafeez kamar zai bauta mishi, Allah yaja ran sarki mai jiran gado, Abubuwa masu Muhimmanci Allah ke yinsu, Mu aron mulki mukayi ta karfin tsiya, kai kuwa Allah ne ya baka shi daga fadar shi, wannan mulkin rubutacce ne a cikin allon Allah, Allah ya baka nasara... Buďe baki Hafeez yayi ya koma can baya, da sauri Husnah ta riko hannunshi suka koma daki dan a ganinsu wata cutar yarima suhail zaiyi mishi..... Mrs Tijjani Shattimah...... [12/06 7:23 PM] fareedah: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 7⃣1⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Cikin azama ta fara tattara langunan gabanta tana turasu cikin lokar katakon dake kofar dakin da aka bata, "Badariyya ina naman da kande tace mu raba? Kinga bana son tashin hankali, ki fito dashi kawai mu raba, wannan ma ai keta ce, Sharce zufar da ke goshinta tayi ta kalli Marakisiyya tace "Na cinye, na bawa Tanimu da jazuli suma sunci, kinga sunci kason uwarsu, ni nawa 'yayan ko kamshi basu ji ba, "Marakisiyya ina namanmu? gashi can su Hannafi suna ci suna mana gwalo, "Tanimu ďan Marakisiyya na farko ya faďi cike da dacin rai.. Maida kallonta gurin Badariyya tayi zuciyarta na k'una ta kasa yi mata magana sai nuni da tayi mata da hannu na "kina jin abin da Tanimu yake faďi? Tsaki mai karfi Badariyya taja ta wuce daki tana goge fuska da zaninta da yasha jiki, Tana sanya kafarta cikin dakin taji an shako wuyanta harda haďawa da labulen tsummar dake kofar dakin, Marakisiyya bata jirayi komai ba ta fara naushin bakin Badariyya tana faďin ina naman mu yake?wallahi in baki fito da naman nan ba sai na yagi na jikinki ya zame mana naman shekarar da bamu ci ba, "Ke ni fa a yanzu saidai a mutu a gidannan, dan wallahi kiriss ya rage in fara maita, in banda mugunta naman da kika san sai shekara muke cinshi shine kika haďa da nawa da naki kika cinye saboda haďama, Wallahi ko ki fito min da naman nan ko inyi fata fata da naman cinyarki, yin karar suya bazai min wahala ba ko Tanimu yayo... Yadda take maganar tana haki idanuwanta yayi jawur ya sanya Badariyya tsurewa, "Tabbas Marakisiyya ta fara maita, cikin muryar azaba jini faca faca da bakinta tace "Sakeni zan baki! Sake shake ta Marakisiyya tayi tace "Ai saidai muje tare, wallahi babu inda zaki ke daya, matsiyaciyya mai bakin hali, Kuka Badariyya ta fashe dashi ta fara tafiya har ta isa gurin da ta boye naman, tana sa hannunta taji an wafce langar harda hannunta sannan ta hankadata jikin katakon, kusar dake jiki ta caki tsakiyar goshin Badar, Wani irin ihu ta tsala wanda ya tattaro hankalin mutanen cikin yalwataciyyar bukkar sarkin, Kande ce ta isa gareta ta toshe mata gurin jinin sannan ta shige da ita daki, ita kuwa Marakisiyya ko a jikinta, namanta ta tusa a gaba suna yaga ita da 'yayanta..... ****** Nayi Nadama, Na tuba, wallahi na yarda zan zauna da kai, yanzu 'yayana biyu da kai, Hannafi, da Suwidi, ina zan tafi in barsu? dan Allah ka yenta ni kamar yadda ka yanta gimbiya Sailuba, na saduda zan zauna dakai, wahalar da nake sha a gidannan ta isheni, ka taimakeni ka kaini inga iyayena ko sau ďaya ne takk, nayi alkawarin bazan bujire maka ba duk abin da kake so shi zanyi---- ta karashe cikin matsanancin kuka.. garin maganin da aka sa mata a goshi ya murmuso mata a ido... Dariya yayi sosai yace "Wuya makarantar kare, To ai dama laifinki ne da kika biye wa mai son zuciya irin Marakisiyya, da a yadda aka kawoki gidannan kinyi min ladabi da babu abinda zai hanaki fin Sailuba fada a guri na, to sai kika nuna kinfi Marakisiyya rashin imani, shiyasa na nuna muku karfina a kanku, na sanya ku kuka zamto tamkar karnuka, tunda kin gane kanki yanzu to baki da matsala, zan kaiki kiga yan uwanki nan bada jimawa ba, amma sai naga kamun ludayin nadamarki, in har kika canza hali gaba daya to babu wanda zai kaiki jin dadi duk cikin matana domin na fi kaunar kasancewa dake.... Janyota jikinshi yayi cikin wani irin siga ta sha'awa, karfin turaren dake tashi a jikinshi ya kusa zautata saboda tsabar rashin dadi, wasu zafafan hawayen dana sani ne ya dinga kwaranya a cikin idanuwanta, dana sanin rashin kasantuwarta mutuniyar kirki har halayyarta da kaddararta ta sanya wannan masifar afkuwa da ita, tunano irin rashin mutuncin da ta dinga yi ma yan uwanta musamman Nadeeyah da Musaddiq tayi, da ace lokaci zai sake bata dama, da ta kaunaci har mai gadin gidansu, da ta nuna ma yan uwanta kauna domin tana tsananin kewar su... Ta sha wahalar da ko makiyinta bata fatan yasha, mace kamar ita ace bata da zanin kirki da take daurawa, dakin baccinta babu ko katifar da zata sanya hakarkarinta, ba'a ma maganar hasken lantarki domin bata taba ganinshi a gidan ba, duk yadda mai karatu ke auno kuncin rayuwar da Badariyya take ciki ya wuce haka domin kunci ne na mutane marasa galihu da 'yancin kai, 'ya'yanta da ta samesu ta hanyar tursasawa, tamkar almajirai saboda tsabar wahala da suke sha, tasan tabbas in akayi bincikenta abin da za'a fara cin karo dashi a tare da ita shine infection, sannan wasu ciwukan su biyo baya, Runtse idonta tayi saboda azabar da takesha na cakalkalata da yakeyi, saida yayi fin awa yana abu daya, bayan ya gama yayi mata albishir da indai tana san ganin yan uwanta to ta cigaba da kasancewa mai biyayya da dauriya a gareshi kamar yadda ta kasance mishi a yau...... *Canada* Ohhh.. ya Allah Mukhtar ai sai ka karyani, ajiye remote din hannunta tayi ta karbi cupin da ya bata, "Mashaa Allah, nasan jika na is the best, Allah ya albarkaci rayuwarka.. ta karashe haďe da sumbatarshi... "Barka da gida Aunty!! Nadeeyah ta faďi a ďan russune, "Barka dai ta amsa babu yabo babu fallasa, ta cigaba da yi ma junior wasa.. Ciki Nadeeyah ta wuce ba tare da ta damu da yadda Anty Saude ta amsa mata gaisuwarta ba, ko wacce uwa hakan zatayi in dai danta ya fuskanci abunda Taheer ya fuskanta, soyayyar da take nunawa Junior shi yake sanya zuciyarta sanyi a duk lokacin da ta ga irin halin ko in kulan da Anty sauden ke nuna mata, kula babu wacce bata yi mashi, ita ko me zata ce mata banda godiya, sannan tana rokon Allah ya kawo lokacin da zata saka musu da mafificin alkhairin da sukayi mata..... "Me zaka ci?, noodles ko peppersoup? Kallon Taheer Junior yayi yace Daddy me zamu ci? A'a my dear ba cin abinci yanzu sai anyi wanka, jeka Mamma tayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156