Skip to content

Chapter 94

Chapter 94

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

number wayarshi ta bukata nan take ya karanto mata sannan yayi musu sallama suka wuce....... Tashin Husna Nadeeya ta dinga yi akan taje ta tada Musaddiq kar ya makara dan jirgin 6 zaibi zuwa lagos, mikewa tayi tana turo baki tace "kije ki tasheshi mana, ni bazan iya ba, hakuri ta shiga bata har ta samu ta yarda ta wuce dakinshi, kamshin turarenshi da taji ne ya bata tabbacin ya tashi, a tsaye ta sameshi yana gyara links din hannun rigarshi, "ashe ka tashi?, alhamdulillah na huta, dariya yayi yace aikin Mummy ne, tun dazu ta tasheni, ina matata? Hamma Husnah tayi tace "tana daki ita ta matsa min inzo in tasheka karka makara, sosai yaji dadi har cikin ranshi yace "muje in ganta kafin in wuce, A kofar shigowa suka kusa karo da Mummy rike da plate din indomie da kwai, Cup din hot choco kadai ya karba ya yi hanyar dakin su Nadeeyah, "Ina zaka je? Mummy ta fadi tana bin bayanshi, "amm zan je.... zan ---- dawo nan ka zauna kaci abinci, ko jirgin na ubanka ne in lokaci yayi bazasu jiraka ba, "Mummy, Nadeeyah bata da lafiya ne zai duba ta.... wani mugun kallo tabi Husnah dashi wanda yasa ta saurin murda kofa, "zo nan sakarya wacce bata san ciwon kanta ba, sum sum Husnah ta dawo inda Mummy take, kunnenta ta kama tace "wallahi kinji na rantse, wannan rawar kafar da kikeyi akan Nadeeyah in baki daina ba sai na ci miki mutunci, kuma in sake jin maganar tafiya Gombe a bakinki sai na tattaka ki, marar mutunci kawai.. ta karashe hade da dungure mata kai, kafa Husnah ta fara bugawa a kasa tana fadin "ni wallahi sai naje, hanyar dakin Daddy tayi Mummy tayi saurin tareta dan karansu na daren jiya baiyi mata dadi ba, yanzu in ta bari Husnah ta kai kararta tofah tasan bazai mata da kyau ba, "Ina matsayin mahaifiyarki kike kokarin bijire min har kike yunkurin kaini kara, ni zakuyi ma tawaye? Babu komai kuyi abin da kuka ga dama ta karashe tana matso kwalla, kewayeta sukayi suka shiga rarrashinta, dakyar ta hakura ta tasa keyar Musaddiq har mota sannan ne ta samu kwanciyar hankali..... Dubu dari biyu Papy ya bada kudin sadakin Nadeeyah, sai dubu dari na gaisuwa... cike da farin ciki Daddy da abokinshi Alh Abubakar suka karbi kudin, nan Daddy yasa biki wata biyu dan yana so ya samar musu gida a can lagos dan suyi nesa da duk wani tashin hankalin gida..... *(Shaff ya manta Raudha na lagos kuma duk tafi kowa matsala cikin 'yayan nashi,)...* ******* Woww mashaa Allah my little brother ya girma, yaushe aka sa bikin Daddy? "June amma bamu cire date ba, Maganar shirye shirye na kira inyi miki, inaga zan turo miki kudi ku shiga Dubai kuyi mishi siyayya, sannan zan bawa su Raliya su siyo wasu anan dan mahaifiyarku tace babu hannunta, dariya Anty Reemah tayi tace "ko sisinka karka kashe Daddy, zamu hadu mu hada mishi lefe na gani na fada, "wallhy naji dadin wannan hadin dan dama bana son Nadeeyah ta kufce mana, kullum cikin tunaninta nake.. "Ajiye kofin zobon dake hannunshi yayi ya dafe kanshi da ke sara mishi, "shikenan ya rasa Nadeeyah, tunda har akasa ranar auren ya fidda ranshi da tunanin ko Allah zai taimakeshi ta zamo tashi, maida kwallar da ke kokarin fito mishi yayi da sauri yace "wish u all the best Nadeeyah, Allah ya dawwamar dake cikin farin ciki... yasan Musaddiq na can yana nemanshi, haka itama Nadeeyar, bashi da karfin kunna waya yayi magana da ko daya daga cikinsu, dan raunin da yake ciki bazai barshi ya danne zuciyarshi ba, dole ya koka musu har su gane yana cikin damuwa, Yana cikin wannan tunanin yaji Anty Reemah ta dafashi tace "shine baka fadamin wannan abun dadin ba, yanzu sai mu fara shiri daga bangarenmu, dan bazan bar kowa yayi mishi kayan lefe ba, kai kuma sai ka shir---- Mum kinsan ina Msc, kuma mun kusa fara exams, dakyar zan samu zuwa, "cike da Mamaki tace "Hilal... Musaddiq ne fa, kada kanshi yayi cike da damuwa yace "Mum bance bazani ba, amma for nw banda karfin shirye shirye, plsss ku barni inyi karatu... Mikewa tayi cike da tausayin danta tace "take ur time dear, Allah ya bada sa'a... tana kaiwa nan ta wuce kitchen ranta duk a dagule..... Gaba daya Nadeeyah ta mance damuwarta tunda tazo garin gombe, gidan karamci, wani irin ji dasu Mami takeyi kamar ita ta tsuguna ta haifesu, Yawo kuwa babu gurin da basu je ba a cikin Gombe, ga wani shiri na musamman da Mami tasa akewa Nadeeyah wanda ya kara fitar da kyawunta ta ciko tayi bulbul, fatar jikinta sai sheki takeyi ga santsi kamar tarwada... Husnah da Hafeez kuwa wata shakuwa mai kama da soyayya ce ta musamman ta shiga tsakaninsu, tun Hafeez na dari dari har ya saki jikinshi sosai da ita, raba dare sukeyi suna tsaftattaciyar hirarsu mai ban sha'awa, da Papy ya lura da hakan ya kirasu duk su biyun ya tambayesu, Husna ce ta fara amsawa da tana sonshi, sannan ne Hafeez ya samu karfin gwiwar bada tashi amsar, farin ciki marar misaltuwa Papy ya shiga.. sallamarsu yayi hade da kiran Daddy ya labarta mishi, Daddy cike da jindadi yace to ai bazamu jira ba, gara a hade bikin ayi shi rana daya, nan suka gama tsara yadda zasuyi sannan sukayi sallama cike da jindadi.... Kwanciya Daddy yayi yana kabbara da girmama hukuncin ubangiji, wato ubangiji ya hanashi auren Suwaiba saboda wannan ranar da auratayya zata bullo a tsakanin jinin da suka yi tsaftattaciyar soyayya ta tsakani da Allah, lallai *kaddara* itace jigon rayuwar dan Adam, domin da ita yake yawo duk inda zashi.... ina ma Suwaiba zata dawo taga hukuncin ubangiji, taga yadda rayukan 'yayanta suka canza, wata yar kwallar murna ya share yayi adduoinshi hade da runtse idanuwanshi...... Hauka ne kadai Mummy bata yi ba da taji labarin hade auren harda na Husnah da suka gama maganarta da kawarta Hajiya Safara'u, babu irin masifar da batayi ba, shiko Daddy ko a jikinshi kudin kayan kitchen ma yayi mata transfer zuwa account dinta dan sauran da kanshi zaiyi su, Sa kai yayi ya fita ya bar gidan dan lagos ma zai tafi da daddare akan maganar gidan da aka samu... Kuka ta zauna a parlor tana yi sosai kamar an mata mutuwa, bakin cikin da take ciki yau har gwammaci dama bata taba sanin Daddy a rayuwarta ba, Badar ce ta fito tana hamma, duk wainar da ake toyawa a gidan bata da masaniyarsu dan ba zaman gidan takeyi ba, da sauri ta isa gurin Mummy tana tambayar abun da yasa ta kuka, Ganin da tayi wa Badariyya ya sa hankalinta dan kwanciya, dan wani abu da ya darsu a ranta, tasan Badariyya ce kadai zata iya yi mata maganin damuwarta... Hannunta ta rike ta sake rushewa da kuka tace "Badar na shiga uku, Musaddiq zai auri Nadeeyah, Hafeez kuma Husnah, kinji a inda zan kare a ya'yan da basu da asali, yayan mai gadi ni zainab..... Wani irin ihu Badar ta saki tace "Whattt? Nadeeyah zata auri Musaddiq dina.... ta fadi hannu na rawa tana dafe kirji....... Mrs Tijjani

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156