Skip to content

Chapter 106

Chapter 106

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

yaya take, thank Goodness bai taba zuciyarshi ba, but yaso yayi affecting dinta, plss ya kiyaye sosai cos life is very precious... Wasu zafafan hawaye ne suka biyo ta gefen idonshi bayan ya gama sauraron abin da doctorn ya faďi "Life is nothing without Nadeeyah, ya Allah ka sassauta min.. Hannu Anty Saude tasa ta share mishi hawayen itama ta share nata sannan tayi ma doctorn godiya ta kuma yi mishi alkawarin kiyaye duk abinda yace mata, har bakin kofa ta rakashi sannan ta wuce kitchen rai a bace, Wani maganin kwari mai karfin gaske ta dauko haďe da juice ta dawo kusa da Taheer ta zauna, yana kallonta ta ďure maganin a ciki, a hankali ya mike yana tambayarta abun da zatayi dashi, ko kallon inda yake batayi ba ta daga juice din zata kaishi bakinta, Wani irin karfi yaji a jikinshi haďe kabe juice din a hannunta, baki na rawa yace "Are u out of ur senses, poison ne fa, so kikeyi ki kashe kanki? "Gara in kashe kaina da irin kisar da kake shirin yi min Taheer, gara in mutu kafin ka kashe kanka kasa min mutuwar ko'ina na jikina, bani da wani muhimmanci a cikin rayuwarka, akan mace kake so ka kashe kanka har kake kiran rayuwa ba komai bace in babu ita, gara ka barni in fara mutuwa sai ka biyoni, bazan iya jurar ganin gawarka ba Tee... . bazan iya ba.... ta karashe tana kuka sosaiiii.... Kanshi ya daga sama da niyyar haďiye kukan da ya tokare makokwaronshi, inaa sam ya kasa, wanda yake kokarin haďiyewa ya fito da karfinshi, Zaman dirshan yayi a gurin yana kuka sosai kamar karamin yaro, bata hanashi ba dan itama kukan takeyi, wallahi da zatayi arangama da yarinyar da tayi wa ďanta haka sai ta shake wuyanta ta kusa kaita lahira, ita duk tunaninta cin amanar ďanta tayi, domin ita tace ya jirata, sai kuma yaji labarin aurenta, duk da bata san wacece Nadeeyah ba taji a duniya bata ko san karo da mai sunan a rayuwarta, Saida sukayi kukansu ma'ishi sannan Taheer ya rarrasheta ya kuma yi mata alkawarin daina tunani akan wacce ta zamto matar wani, sannan ya roketa da Allah kar ta yi mishi maganar aure nan kusa har sai yayi niyya dan kanshi, Badan taso ba ta yarda da kudurinshi, tasa ma ranta nemo mishi yarinyar da zata maye mishi gurbin cin amanar da akayi mishi...... Lafiyayyen abinci ta shirya mishi ta dinga mishi hira, "auu kaga damuwa ta dauke min hankali, jiya *Mus'ab* ya kirani, wai su *Aman* sun samu gurbin karatu anan university of Toronto, ina ganin gobe ma suna hanya, bakaji daďi da naji ba, dan zasu rage min kaďaici in ka tafi makaranta, nuna mata jin dadinshi yayi yace "mantawa nayi ban faďa miki ba, ni na nema musu admission din, Anty Nuwairah duk ta damu wai sunyi nisa, saida taji a gida zasu zauna shine hankalinta ya kwanta, naman karshe Anty Saude tasa a bakinshi tace "Haka tace min, ai naji dadi sosai, Allah ya kawo su lafiya, "Ameen ya faďi haďe da mikewa yace "bari in watsa ruwa, inaga gobe zani lagos, Kudin Abba na companyn coffee ya fito, sunce in je inyi signing..... cike da jin dadi tace "Kaii mashaa Allah, Allah ya kaimu goben...... ********** Tagumi tayi akan dadduma bayan ta idar da Nafila tana jiran a kira sallar asuba ta tashi tayi, tunanin irin rayuwar da takeyi a gidan aurenta takeyi, tunda tazo gidan ta auri zaman ďaki, bata san kalar kitchen dinta ba domin yadda su Radiya suka kanainaye komai, babu inda take fita kullum daga bayi sai ďaki, bata da matsala sam da Musaddiq domin yana kula da ita sosai, abinci ma in ya siyo da kanshi zai bata kuma ya kwashe kayan da kanshi dan shima tsoron tashin hankali yakeyi, a da bata jin son Musaddiq a matsayin abokin rayuwarta, amma kwanaki shidan nan da sukayi tare, halayyarshi ta samar mishi matsayi mai girma a zuciyarta, Mutum ne mai gudun zuciya, yadda bazai bata maka ba, kaima karka bata mishi, samm baya kwana da wani a ranshi, sanyin halinshi shine abu mafi soyuwa a gareta, tun ranar da ya kusanceta yaga irin kukan da tayi, bai sake koda kwatantawa ba, duk ko da tsabar dannewar da yakeyi, samm bayasan abin da zai sata cikin damuwa, ya gwammaci matsuwar ta dameshi akan yasata cikin damuwa... kiran assalatu ne ya katse mata tunanin da takeyi ta mike dan ta tashe shi ta kuma sabunta alwawarta, Bargon da ya dukunkune ta yaye a hankali, zufar da ta gani a fuskarshi ce ta sanyata zaunawa kusa dashi da sauri haďe sa hannu a goshinshi ta fara share mishi, hawayen da ya jika saman idonshi shi yafi komai daga mata hankali, a rude ta fara kokarin ďago kanshi ta kasa saboda har lokacin cikin bacci yakeyi, gefen kunnenta ta kwantar a saitin kirjinshi taji yadda zuciyarshi ke bugawa da sauri da sauri, ajiyar zuciya ya saki haďe da shashesheka ya sanya hannu ya rungumeta sosai a jikinshi, "plss don't lv me, i can't lv without u.... yadda yake maganar ido a rufe ya bata tabbacin mafarki yakeyi, duk wata kunyarta ta nema ta rasa ta rungumo kanshi haďe da share mishi hawayen da yakeyi tace "bazamu rabu ba, in shaa Allahu babu abinda zai rabamu, Allah ne ya haďamu, shine kadai zai iya rabamu in yaso, "bazan barka ba! Jin kalaman da yake a zahiri ba'a mafarki ba yasa shi buďe idonshi haďe da kwantar da ita sosai a jikinshi yace "promise? gyaďa kanta tayi haďe da cewa "Ummm, "umm me? Ya fadi yana daďa narke mata, turo bakinta tayi a shagwabe tace "um um, dariya yayi yace "kinsan nafiki iya shagwaba, in na fara nawa gari zai waye mana ba muyi sallah ba, kinji an tada kabbara, tashi muyi sallah mu roki Allah kar ya tabbatar mana da mafarkin da nayi, juyo fuskarta yayi ya daura hancinshi kan nata numfashinsu ya gauraya da na juna yace "i don't want to loose you, hannunta tasa ta toshe mishi baki cikin zolaya tace "hmmm... muje kayi brush, "bakina wari ko, "ni dai ban faďa ba! "laifin ki ne, baki sani nayi rinsing baki na ba, nidai ba ruwana, kaji anyi sallama ko, dan Allah muje muyi sallah, "zakiyi bayani bari mu idar da Sallah, ya faďi yana dariya haďe da nufar bayin...... Wai Mummy Faida bazata zo bane, babu wani improvement fa, kullum daďa like ma yarinyar nan yake, can u believe that ko gaisheni bata fitowa tayi, ni kam in bazaki turo Faida ba zan shirya in koma gurin 'yayana, Daddyn Ra'ees ko daga wayata baya yi, wannan bai dameni ba, dan nasan ina komawa gida zai huce, burina inga munyi winning yarinyar nan ta bar rayuwar little, Radiya na dire aya Mummy tace "Karki damu, Faida na nan tafe anjima, mun gama magana da Hajiya Aliya, in shaa Allahu komai ya kusa zuwa karshe, kudai ku cigaba da taka tsan tsan kar Daddynku ya gano kina can, dan wallahi in ya gane ba zamuji daďi ba, gyara zama Radiya tayi tace "bazai ji ba in shaa Allah, ai kwana kaďan ya rage, "To Allah ya nuna

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156