Chapter 101
Chapter 101
matata bace kanwata ce, zan iya daukarta in lalura ta sameta, to ya zanyi in barta a bayi tunda ku ba fita zakuyi ba itama kuma tace bazata fito ba, shiyasa kawai na raba gardama, "Hmmm yara kanana da makirci ni jikar Ma'u, to bari kaji in fada maka, wannan rawar jikin da kakeyi ka rageshi, ita mace in taga ana sonta sosai nan ne take bude kafar iskanci, ka hankalta ka dinga jan ajinka, ka zamana kai mai gidan ne gaske, yawan sake fuska da hira duk suna sanya mace ta raina namiji, Barshi Raudha "zo ki zauna muci naman nan zan mishi course anjima, dan bana jin bacci... Shi mamaki ma suka bashi, kowa yana ce mishi matarka itace komai naka, itace abokiyar wasanka kuma sirrinka, su kuma ga irin tasu lakcar, murda kofar yayi yace "sai da safenku, "a'a karkayi bacci, zamu--- "Aiko zanyi bacci ya katseta hade da rufe kofar yana dariya, shi ya rasa me ke damunsu, bayan Mummy kawai suke bi, Wanda duk yaso Faida ya bar Nadeeyah a gurinshi baisan me yakeyi ba, a iya gane ganen yan matanshi bai taba ganin macen da ta hada komai irin matarshi ba, wayarshi dake kara ya dauka ya kara a kunne hade da cewa, "Mahmood har kun isa, daga daya bangaren Mahmood yace "yess yanzu na shigo gida, na manta, akwai wasu kaya da Mama ta bani in ba Nadeeyah, suna nan boot din *Zubair,* na kirashi zai kawo maka gobe, "ohk Besty ba matsala, thank u soo much, "most welcome Kyari, a kular mana da kanwa, nyt, "in shaa Allah, Allah ya tada mu lafiya...... Knock knock knock... Little ka kwanta ne, tsaki ya ja hade da nade daddumar da suka idar da Sallah akai, bude kofar yayi yace "lafiya Anty? dan tsaki tayi tace "wallahi na kasa bacci ne, ga gidan yayi min girma in kwana ni kadai a daki, turo min Nadeeyah mu kwanta tare, "Nima gidan yayi min girma, kinsanni da tsoro, har gara ke, ya fadi on a serious nt, "to sai mu kwana mu uku, in a nan ne in shigo in can ne kuma ku dawo, "Da kai kawai ya amsa mata hade da rufo kofar, Juyowa yayi yaga Nadeeyah a bayanshi, "ina zaki? zanje can dakin, tunda tana jin tsoro bai kamata mu barta ita kadai ba.. Hannunta ya riko haďe da janyota gab dashi, a dan shagwabe yace "nima tsoro nakeji, kokarin kwace hannunta tayi tace "ai tace muje mu uku mu kwana, dan Allah zo muje kar ranta ya baci... Hade jikinshi yayi da nata yana shinshinar daddan kamshin kanta hade da lumshe yace "ni dai tare da matata zan kwana, plss ki rabu da ita, kwana nawa rabona dake, kinsan irin wahalar da kika ba zuciyata, "Tsugunawa yayi dan saita tsayinsu haďe da sake narke mata, "pls, pls, pls, wata yar dariya tayi wacce ta sashi sake rikice mata, "dariya kike min ko? "Dan Allah maida bakin, ta fadi tana tura bakin da hannu. yadda ya sake turo bakin yasata sakin dariya mai dan sauti, abun da yake so kenan dama, nan yayi mata wata irin runguma mai dauke da shaukin so, wasu rikirkitattun sakonni ya shiga aika mata masu wuyar fassaruwa wanda ya sanya jikinta kyarma matuka, "kuka sosai ta sanya mishi na rashin sabo tana tureshi, shi din ma kanin kukan yakeyi wanda ya sanyashi daukarta ya ajiyeta a tsakiyan gado, Daga shi har ita basu taba shiga cikin yanayin da suke a yanzu ba, ba kamar Musaddiq da yake namiji mai jini a jiki wanda yake tashe da kuruciya da kudi, ga madarar kyau, amma Allah ya tsare shi da mu'amala da ko wace irin mace, Nadeeyar dai kadai yake gani mace a duk matan da yayi arangama dasu, bai taba sanin feelings din kasantuwa da mace haka yake ba shiyasa yayi matukar gigita fiye da tunani, babu abin da yake iya saurare a wannan lokacin sai kukan Nadeeyah da ya kasance abin so a gurinshi, duk irin bugun da Anty Radiya kewa kofar baiji ba saboda a inda Musaddiq yake guri ne wanda bayajin kira komin karfin kiran kuwa..... Mrs Tijjani Shattimah...... [14/04 8:11 PM] +234 807 161 1811: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣8⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Sake duba agogo yayi karo na ba adadi yaga karfe goma da rabi, Rai a bace ya mike ya fara rufe kofofin gidan hade da wutar globe, kitchen ya nufa dan duba ko an kashe kayan wuta, wutar corridor din kitchen ya kashe hade da faďawa ciki, Tozali yayi da Fatima tsaye tana fere dankalin da za'aci da breakfast, gyaran murya yayi wanda yasata juyowa a dan firgice, hada ido sukayi tayi saurin sunkuyar da kanta hade da tsuguwa kasa ta gaisheshi, "Tashi Fadima, aikin ne kikeyi har yanzu?? bakya jin jikinki, murmushi tayi tace "naga gobe da wuri su Ummah zasu tafi shiyasa zan rage aikin da asuba sai in karasa, gyada kanshi yayi hade da fita parlon cike da tunani iri iri, A parlon ya zauna zuciyarshi na ta kitsa mishi abubuwa da dama, motsin fitowa yaji daga dakin dasu Ummah suke, Kanwar Umman ce ta fito da kofi a hannunta, ganinshi a zaune yasata zama kusa dashi itama tana dan janshi da hira, "Bakiyi bacci ba Inna? "ruwa zansha Shamsu, kaima baka kwanta ba, ga yar lelenka bata dawo ba, dariya yayi yace "kinsan biki, inaga a can zata kwana, "auu kana gani ne ma? Lallai kana da aiki shamsu, watanmu biyu a gidannan yarinyar nan bata taba zama ta kula damu ko na second daya ba, wallahi in zaka hankalta ka nemi macen mutunci ka nemeta ka aura, wacce zata zame maka macen gida ba ta titi ba, tana kaiwa nan ta fara kokarin mikewa, ganin Fatima ta fito yasa ta zama tace "yar albarka, zo ki bani ruwa, da sauri ta karbi kofin ta wuce kitchen ta dauko ruwa a gora ta kawo mata hade da yi musu sai da safe, Kallo suka bita dashi har ta kurewa ganinsu, Inna Indo ce ta fara dauke idonta tace "badan son duniya irin na 'yayan zamani masu son 'yayan masu kudi ba, da sai ince wannan yarinyar itace tayi daidai da tsarin macen aure mai mutunci da kamala, to saidai ita ba yar kowa bace, face yar mai aiki, Allah ya saka musu hidimar da sukayi mana ya kuma bata miji nagari, mikewa tayi tace "sai da safe, "Allah ya tashemu lafiya.. ya fadi yana cigaba da nazarin kalamanta, kafin safiya ya gama sawa ranshi zai auri Fatima badan yana sonta ba, sai dan su sami nutsuwa shi da 'yayanshi da yan uwanshi....... Washe gari kafin su Ummah su tafi ya fada musu abin da ya yanke a zuciyarshi, babu wanda a cikinsu bai nuna farin cikinsa ba, Inna indo da kanta ta samu Gyatum ta yi mata magana, sai da aka kai ruwa rana da ita saboda tsananin tsoron Radiya daya cikata, har saida shi kanshi Shamsun yayi mata magana sannan ta yarda, Fasa tafiyar Ummah tayi, tasa yan uwanta sukaje nema ma danta auren Fatima, so takeyi ayi auren kafin Radiya ta dawo.. Shima hakan yakeso saboda tsabar bacin ran da ta haifar mishi na cewa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156