Chapter 57
Chapter 57
ba, bani da kudi haka na goyashi saboda bashi da kayan sawa, ga rashin karfi nawa da nashi, Cikin ikon Allah muka samu motar zuwa Gombe, saida muka kwana uku a hanya muna tafiya, duk kauyen da muka tsaya anan zan roki ruwan zafi in mishi wanka, wata baiwar Allah ce ta hada min da wani maganin da nasha har na samu karfin jikina, sannan ta bani wanda na barbada ma cibiyarshi hade da gishiri, koda muka isa gida nan ma akayi min caaa ana Allah wadai dani, ban saurari kowa ba na shiga gurin mahaifiyata na roki gafararta, nace mata zan tafi neman abun da zan rike ďa na, Bata kalleni ba amma shashshekar kukanta shi ya tabbatar min da tana cikin tsananin damuwa, har na kai kofa ta kirani, dawowa nayi naga ta kwanto gefen zaninta ta fito da kudi masu yawa na furar da takeyi ta bani ba tare da ta kalleni ba, Murmushin farin ciki nayi na dauki wannan kudin a matsayin sa min albarka tayi, nan nayi mata sallama na fita, A tsakar gida sai zunde na sukeyi, babu wanda ya kula da halin da zamu shiga ni da dana, su dai burinsu in rabasu da abin kunyar da na dauko musu, cikin gari na wuce dan neman aikin da zanyi in ciyar da kaina, Da farko a wani kango muke kwana wanda ake gininshi kullum, kayan sawa na dasu nake dukunkuneshi saboda bashi da na sawa, da safe in masu ginin sun zo sai in goyashi in tayasu dan in samu wani abun rikewa a hannu, a haka har mukayi sati daya a cikin gurin, Ranar da muka cika kwana takwas Abdallah ya tashi da ciwo mai zafi kamar bazai yi ba, saboda rashin sanin abin yi na zauna na tasa shi a gaba nayi ta kuka, daya daga cikin masu kula da gidan ne ya tausaya min ya dauke mu a gurin ya kaimu wani shagon kwano yace mu dinga kwana a ciki, Sannan ya nemo min bedi da yawa da icce da tukunya yace in dafa mishi ya dan sha ruwan in mishi wanka, kafin inyi mishi godiya naga ya fita ya karbo wata kwarya, tuwon dawa ne a ciki da miyar kuka, nan na hau ci kamar karamar zakanyar da taga nama, A haka dai muka cigaba da rayuwa har na samu aikin shara a wani gurin gwamnati, saida na shekara biyu ina aiki a gurin, a lokacin Abdallah ya fara girma amma yau da lafiya gobe babu, kullum matsalar cibiya yake fama da ita, saida ya shekara bakwai sannan na kaishi asibiti, anan ne ake fada min tarin datti ne ya shiga cibiyar, jinjina tsawon rai irin nashi likitan yayi da na bashi labarin yadda na sameshi yace "lallai yaron nan Allah yana san saukar da rubutacciyar aya ta dalilinshi, anan dai likitan yayi mishi aiki, cikin lokaci kalilan ya samu lafiya muka dawo aikinmu, kullum tare muke zuwa yana tayani, A gefen gurin da nake shara akwai wata makaranta, da naga yana yawan zuwa gurin ya tsaya, kuma yana sha'awar karatun, sai na kaishi makarantar, islamiyya ma yana zuwa ta allo sannan ina koyar dashi a gida.. gwagwarmaya babu irin wacce bamu sha ba ni dashi, Lokacin da ya gama makaranta, ya fito da sakamako mai kyau, gwamnati ce ta dauki nauyin cigaban karatunshi saboda hazakar shi, A lokacin da yake karatun ne muka dan fara samun sauki saboda in aka bashi kudi a nan gida yake barin su, ya gwammaci in ya dawo gida muyi amfanin da kudin, *Nasara* ta Allah ce amma ni zan iya cewa ita ainihin kalmar ma'anarta shine Abdallah, shekarar da ya gama jami'a aka bashi aikin koyar da yan aji daya a makarantar, duk inda yaje a unguwarsu zakiji Ana fadin *Abdallah Hanne*, da sunan da yake amfani kenan ko a makaranta, ko kuma ace uncle Abdallah.. yaran unguwa yake tarawa yayi ta koya musu karatu.. jan majina tayi dan kuka na neman cin karfinta ta cigaba da cewa "tunda muke da Abdallah sau daya ya taba cemin "Ina Babana *ANNE* sunan da yake kirana kenan tun yana yaro, a ranar nayi kuka sosai wanda ya tayar da hankalinshi, tun daga ranar duk gorin da ake mishi bai damunshi, saboda yasan wani mai uban ma bazai nuna mishi jin dadi ba, A kullum saidai in dinga fada mishi kana da uba, kai ba dan shege bane, kai dan sunna, aure ne ya samar dakai, Kullum addu'ata Allah ya hadani da mahaifin Abdallah koda sau daya ne ya ji wannan farin cikin da yayi dakon su shekara da shekaru, bayan ta kai aya ta kalli Papy da ya fita hayyacinshi saboda tsabar kuka tace "shine mahaifinka Abdallah, wannan shine ya haifeka! Rungume Anni Papy yayi ya tsananta kukanshi yace "duk duniya babu na biyunki Anni, saboda ni kika bar gida, kika bata rayuwarki da lokacinki! saboda ni kika ki yin aure, saboda ki inganta rayuwata kika hana taki ta zama ingantacciya, why Anni, Why?? Ya karashe yana kuka sosai, Itama kukan takeyi tace "bani nayi ba Abdallah, Allah ne, yin Allah ne, in ba Allah ba waye zai rabaka da iyayenka, babu mamaki yayi haka ne domin ka zama nagartacce, ya rabaka da danginka ne dan ka zama gawurtaccen mutum, babu mamaki da kana gida duk wadannan abubuwan bazasu samu a gareka ba, dalilin da yasa Allah ya barka da rai bayan ka shiga karkashin kasa ba karamin dalili bane.. Maimuna ma ta taka rawar gani a cikin rayuwarka, tasoka a lokacin da kowa ke kiranka da dan gaba da fatiha, Duk kushe ka da akeyi a lokacin kamar ana zugata ne, ta tubure sai ta aureka, Maimuna ta nuna mana kauna lokacin da kowa ya kyamace mu, Cikin Kuka Mami tace "kinyi jarumtar da ko kwatanshi banyi ba Anni, hadasu yayi ya rungumesu yace "banyi regretting rashin tashi a cikin yan uwana ba, domin babu abin da ban samu ba a gareku, uwa, uba, mata, kawa, Aboki, ni ko me zancewa Allah, babu abin da zance sai tarin godiya a gareshi da ya hada ni daku.... Shuru ne ya dan ratsa gurin, sai ajiyar zuciyar kuka kawai ke tashi, kallon farin ciki Baffa yakewa Papy, fuskan nan tasu jike sharkaff da hawaye, Hannun shi ya kamo ya sake fashewa da kuka yana fadin *SAIFULLAH*, Ma'u dana ne, *SAIFULLAH*, jinina ne Ma'u...... Mrs Tijjani Shattima..... [19/03 8:17 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 4⃣0⃣ By *Aysha Ya'u kurah* *Rayuwa takaitacciya ce. Kada ka cika ta da damuwa. Kada dogon Buri ya dauke hankalinka daga mutuwa. Aikata alheri a kowane lokaci watakila shi zai zamo mabudin Aljanna a gare ka*. Alkalamina bashi da karfin rubuta irin gigitar da Ma'u tayi, a zaune take amma jinta take tamkar a tsaka tsaki take, ita bata kai kasa ba haka bata kai sama ba, jinta take kamar wacce take lilo a tsakiyar iska, gaba daya hanyoyin sadarwa na jinin jikinta da kwakwalwarta sunyi balaguron wucin gadi.. Jin hannu da tayi cikin nata ya sanyata dawowa cikin hayyacinta a firgice, kallon hannun tayi hade da mamallakin hannun, ido cikin ido sukayi Anni tace "Da fatan kin gamsu da bayani na, da fatan kin tuno abubuwan da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156